• English
  • Business News
Saturday, October 25, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Ɓangaren Bafarawa Kan Rikicin Shugabannin PDP A Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
9 months ago
Kotu

Babbar kotun Jihar Sakkwato, ta yi watsi da ƙarar da ɓangaren tsohon gwamnan jihar, Attahiru Bafarawa, suka shigar, inda suke ƙalubalantar sahihancin zaɓen shugabannin jam’iyyar PDP na jihar.

A hukuncin da ya yanke, mai shari’a Kabiru Ahmad ya bayyana cewa zaɓen shugabannin jam’iyya lamari ne da ya shafi cikin gida na jam’iyyar, don haka waɗanda suka shigar da ƙarar ba su da hurumin yin hakan.

  • Hare-haren ‘Yan Bindiga Sun Ragu A Watan Disamban 2024, Amma Har Yanzu Ana Fuskantar Barazana – Rahoto
  • Mahalarta Ɗaurin Aure 19 Daga Kano Sun Rasu A Hatsarin Mota A Filato

Ya ce kotu ba ta da zaɓi face ta kori ƙarar.

Rikici ya kunno kai a PDP tun bayan zaɓen 2023, musamman a ƙarƙashin jagorancin tsohon gwamna Aminu Waziri Tambuwal.

Rikicin ya ƙara tsananta a lokacin zaɓen shugabannin mazaɓu na jam’iyyar a 2024, inda ɓangaren da ke goyon bayan Attahiru Bafarawa suka yi zargin rashin adalci.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce

Hukumar Kare Ƴancin Masu Amfani Da Kaya (FCCPC): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa

Ɓangaren Bafarawa sun kai ƙarar gaban kotu, suna neman a soke zaɓen shugabannin mazaɓu, suna zargin cewa an hana wasu ’ya’yan jam’iyyar damar sayen fom ɗin tsayawa takara domin a sharewa wasu hanya.

Lauyansu, Ibrahim Abdullah, ya ce hakan ya saɓa wa dokar zaɓe ta 2022 da kuma kundin tsarin mulkin ƙasa.

Sai dai, ɓangaren PDP da Bello Goronyo ke jagoranta sun musanta zargin.

Lauyan jam’iyyar, A.Y. Abubakar, ya shaida wa kotu cewa waɗanda suka kai ƙarar ba su da rajistar jam’iyyar, kuma lamuran da suka shafi zaɓen shugabannin jam’iyya ya kamata a warware su a cikin gida, ba gaban kotu ba.

Bayan sauraron ɓangarorin biyu, kotu ta yanke hukuncin korar ƙarar, tana mai cewa ba ta da hurumin shiga cikin rikicin cikin gida na jam’iyyar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce
Manyan Labarai

Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Labarai

Hukumar Kare Ƴancin Masu Amfani Da Kaya (FCCPC): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa

October 25, 2025
Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu
Manyan Labarai

Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu

October 25, 2025
Next Post
Xi Ya Zanta Da Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Ta Tarho

Xi Ya Zanta Da Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Ta Tarho

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce

Jami’ar ABU Ta Ƙaryata Zargin Ƙera Makamin Nukiliya A Asirce

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Hukumar Kare Ƴancin Masu Amfani Da Kaya (FCCPC): Tabbatar Da Adalci A Kasuwa

October 25, 2025
Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu

Fiye da Janarori 50 Za Su Yi Ritaya Bayan Sabbin Naɗe-Naɗen Tinubu

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Banki Na Shekarar 2025 Dakta Tony Okpanachi

October 25, 2025
Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

Muna Duba Ƙudirin Ƙirƙiro Jihohi 55 – Barau Jibrin

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Shugaban Kamfani Na Shekarar 2025 Gbenga Olu Komolafe

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Thomas Etuh: Gwarzon Ɗan Kasuwa Na 2025

October 25, 2025
Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

Fansho Da Garatuti A Kano: Yau Fari Gobe Tsumma (3)

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Babban Sarki Oweizide Ekpemupolo (Tompolo): Hiddimta Wa Al’umma Ba Tare Da Gajiyawa Ba

October 25, 2025
Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

Kasar Sin Ta Nemi Amurka Ta Dakatar Da Hare-haren Shafin Intanet Kan Muhimman Kayayyakinta Nan Take

October 24, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.