ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Ɓangaren Bafarawa Kan Rikicin Shugabannin PDP A Sakkwato

by Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
2 years ago
Kotu

Babbar kotun Jihar Sakkwato, ta yi watsi da ƙarar da ɓangaren tsohon gwamnan jihar, Attahiru Bafarawa, suka shigar, inda suke ƙalubalantar sahihancin zaɓen shugabannin jam’iyyar PDP na jihar.

A hukuncin da ya yanke, mai shari’a Kabiru Ahmad ya bayyana cewa zaɓen shugabannin jam’iyya lamari ne da ya shafi cikin gida na jam’iyyar, don haka waɗanda suka shigar da ƙarar ba su da hurumin yin hakan.

  • Hare-haren ‘Yan Bindiga Sun Ragu A Watan Disamban 2024, Amma Har Yanzu Ana Fuskantar Barazana – Rahoto
  • Mahalarta Ɗaurin Aure 19 Daga Kano Sun Rasu A Hatsarin Mota A Filato

Ya ce kotu ba ta da zaɓi face ta kori ƙarar.

ADVERTISEMENT

Rikici ya kunno kai a PDP tun bayan zaɓen 2023, musamman a ƙarƙashin jagorancin tsohon gwamna Aminu Waziri Tambuwal.

Rikicin ya ƙara tsananta a lokacin zaɓen shugabannin mazaɓu na jam’iyyar a 2024, inda ɓangaren da ke goyon bayan Attahiru Bafarawa suka yi zargin rashin adalci.

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ɓangaren Bafarawa sun kai ƙarar gaban kotu, suna neman a soke zaɓen shugabannin mazaɓu, suna zargin cewa an hana wasu ’ya’yan jam’iyyar damar sayen fom ɗin tsayawa takara domin a sharewa wasu hanya.

Lauyansu, Ibrahim Abdullah, ya ce hakan ya saɓa wa dokar zaɓe ta 2022 da kuma kundin tsarin mulkin ƙasa.

Sai dai, ɓangaren PDP da Bello Goronyo ke jagoranta sun musanta zargin.

Lauyan jam’iyyar, A.Y. Abubakar, ya shaida wa kotu cewa waɗanda suka kai ƙarar ba su da rajistar jam’iyyar, kuma lamuran da suka shafi zaɓen shugabannin jam’iyya ya kamata a warware su a cikin gida, ba gaban kotu ba.

Bayan sauraron ɓangarorin biyu, kotu ta yanke hukuncin korar ƙarar, tana mai cewa ba ta da hurumin shiga cikin rikicin cikin gida na jam’iyyar.

Kotu
Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
+ postsBio
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    2027:Cece-kuce Ta Barke Tsakanin Tinubu Da Atiku
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Yadda Rikici Ya Tsananta Tsakanin Dan Daba Da Malaman Addini A Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Dalilin Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Yankin Sakkwato
  • Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
    https://hausa.leadership.ng/author/sharfaddeen-sidi-umar-sokoto/
    Atiku Ya Koka Kan Ƙaruwar Ta’addanci A Sakkwato

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Xi Ya Zanta Da Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Ta Tarho

Xi Ya Zanta Da Shugaban Majalisar Tarayyar Turai Ta Tarho

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.