• English
  • Business News
Tuesday, June 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kuncin Rayuwa: Jan Hankali Ga Iyaye Da Yayyen ‘Yan Mata

by Ibrahim Bala
1 year ago
in Marurun Zuciya
0
Kuncin Rayuwa: Jan Hankali Ga Iyaye Da Yayyen ‘Yan Mata
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Assalamu Alaikum Warahmatullahi Ta’ala Wa Barakatuhu.

Muna rokon Allah ya ba mu alhairan da ke cikin wannan wata mai girma na Ramadana.

Jan hankalin da zan yi tare da tunatarwa a yau, a kan iyaye maza da mata da kuma su kansu ‘ya’ya ne, sannan da kuma yayye wadanda ke kasancewa a matsayin magadan uba, da kuma wadanda ke da kanne mata.

Hakika mun shiga wani irin yanayi na kuncin rayuwa, wanda iyaye ba lallai ba ne su iya yi wa ‘ya’yansu abubuwan da suke bukata ba, musamman a bangaren da ya shafi dinkunan sallah da sauran makamantansu.

Don haka, yana da matukar muhimmanci iyaye su sa ido a kan ‘ya’yansu, su kuma kula sosai wajen ganin da me da me yarinya ta shigo gida da me kuma ta fita? Ka da ‘yarka ko ‘yarki ko kanwarka ta rika shigowa gida da kayayyakin dinki da sunan saurayi ne ya ba ta ta kuma karba, ba tare da kun yi bincike ba, har sai wani abu ya je ya zo; sannan a fara neman mafitar da za ta yi wuyar samu.

Labarai Masu Nasaba

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 

Ba don komai na ce haka ba, sai don sanin yadda dabi’un wasu mazan take a halin yanzu, wasu ba su da kirki ko kadan; domin kuwa za su iya amfani da halin da ake ciki na kuncin rayuwa a kan atamfa kadai ko shadda ko takalmi ko wani abu da yarinya za ta saka da sallah, su lalata mata rayuwa.

Don haka, dole ne a mayar da hankali kwarai da gaske a kansu, sannan duk abin da ta kawo; ya kamata a san wanda ya bayar a kuma ji dalilin bayarwar. Kazalika, idan abin aka ga ya yi yawa ma sai a bincika a dalili, tunda ita ba ‘yar sarki ba ce; iyakar abin da Allah ya hore iyaye a yi hakuri da shi, sannan kuma ku ja wa ‘ya’yanku kunne, saboda yanzu ‘yan mata suna da irin wannan hangen, yarinya za ta ga waya a hannun wata; sai ta saka abin a ranta cewa; ya kamata ita ma ta rike irin ta da sallah, ko da kuwa ta halin kaka ne.

Haka nan, idan ta ga kaya ko jallabiya ko riga ko wani abu dai makamancin irin wannan a hannun kawayenta, ita ma sai ta ce lallai sai ta samu, kar ka yarda a matsayinka na uba ko a matsayinki na uwa, idan an kawo irin wannan ki yi shuru, ya kamata ki binciki asalin abin da yake faruwa.

Kazalika, kai ma da kake a matsayin babban wa na dawo gare ka, lallai ne ka sa ido a kan kannanka sosai, ba zai yiwu don lokacin azumi ne saurayi ya zo ya kai karfe daya ko karfe sha biyu yana tare da kanwarka ba, haka nan yau wannan ya zo, gobe wannan ya zo.

Sannan, yau wannan ya kawo takalmi; gobe wancan ya kawo shadda, jibi kuma wancan ya kawo doguwar riga, dole ne ku sa ido a mayar da hankali ka da a ga cewa ai ana cikin halin ha’ula’i, ko ana cikin wani irin yanayi da iyaye ba za su iya yi wa ‘ya’ya dinkunan da suke so ba, duk abin da Allah ya yassare sai a yi hakuri a karba, ya kamata kuma a lura da cewa; duk abin da ka same shi ta wata hanya ta daban, idan da ka yi hakuri ta hanyar halak ma zai zo ya same ka har inda kake.

Don haka, yanzu lokaci ne na addu’a da ya kamata su kansu samari da ‘yan matan su yi amfani da shi a roki Allah subhanahu wata’ala ya kawo mana sauki da sassauci, idan budurwa ce ki roki Allah ya kawo miki miji nagari, haka nan saurayi shi ma ya roki Allah ya kawo masa mata ta gari.

A takaice, wannan shi ne jan hankalina da fatan Allah ya sa za mu sa ido yadda ya kamata, Allah ya sa mu dace, amin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Wasu Daga Cikin Matan Da Ke Sharafi A Nijeriya

Next Post

Hanyoyin Da Za A Taimaka Wa Malamai Inganta Aikinsu (4)

Related

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
Marurun Zuciya

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)

6 months ago
Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
Marurun Zuciya

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 

6 months ago
Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba
Marurun Zuciya

Ba Gwamnati Ce Kadai Za Ta Magance Yawan Barace-Barace Ba

1 year ago
Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki (1)
Marurun Zuciya

Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki (1)

1 year ago
Ya Kamata Mu Dore Da Ibadu Da Kyawawan Halayenmu Na Ramadan
Marurun Zuciya

Ya Kamata Mu Dore Da Ibadu Da Kyawawan Halayenmu Na Ramadan

1 year ago
Ya Kamata Iyaye Ku Yi Wa Tufkar Hanci…
Marurun Zuciya

Ya Kamata Iyaye Ku Yi Wa Tufkar Hanci…

1 year ago
Next Post
Hanyoyin Da Za A Taimaka Wa Malamai Inganta Aikinsu (4)

Hanyoyin Da Za A Taimaka Wa Malamai Inganta Aikinsu (4)

LABARAI MASU NASABA

An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani

An Cafke Mutum 22 Kan Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato – Uba Sani

June 24, 2025
Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford

Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford

June 24, 2025
Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3

Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3

June 24, 2025
Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

Iran Da Isra’ila Sun Amince Su Tsagaita Wuta – Trump

June 24, 2025
Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi

June 23, 2025
EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

EFCC Ta Kama Tsohon Babban Jami’in NNPC Kan Zargin Satar Dala Biliyan 7.2

June 23, 2025
Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

June 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gargaɗin Amurka: Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja

June 23, 2025
Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya

Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya

June 23, 2025
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

June 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.