• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiya Ta Yaba Wa Shugaba Tinubu Kan Inganta Tsaro Da Yaki Da Rashawa

by Leadership Hausa
2 years ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Kungiya Ta Yaba Wa Shugaba Tinubu Kan Inganta Tsaro Da Yaki Da Rashawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Arewa New Agenda, mai fafutukar kare martaba da shigar Arewa cikin harkokin kasa, ta yaba wa Shugaban Kasa Ahmed Bola Tinubu bisa tsarin shugabancinsa tun hawansa mulki makonni biyu da suka gabata.

Shugaban kungiyar Sanata Ahmed Abubakar MoAllahyidi ne ya yi wannan yabon a wata ganawa da manema labarai a Abuja ranar Juma’a.

Arewa New Agenda ta bayyana wasu muhimman shawarwari da matakan da shugaban kasan ya dauka tun bayan hawansa mulki, wadanda suka hada da: soke tallafin man fetur, hana yajin aikin da kungiyoyin kwadago suka shirya yi a fadin kasa, da kafa tsarin kudin musaya na Naira bai-daya, da ganawa da shuwagabannin hukumomi masu muhimmanci tare da kai ziyara a cibiyoyin tsaro da tattara bayanan sirri da sauransu.

A cewar MoAllahyidi, “Wadannan matakai sun nuna jajircewar Shugaba Tinubu wajen tunkarar muhimman al’amurra a kasar nan da kuma samar da jagoranci nagari a harkokin mulki”.

“Nade-naden da Shugaba Tinubu ya yi ya haifar da samun kwarin gwiwa a kan ingantuwar tsaro da kuma yaki da cin hanci da rashawa”.

Labarai Masu Nasaba

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

“Muna farin ciki da cewa shugaban kasa Tinubu, wanda kungiyar ta goyi bayansa a lokacin da yake neman takararsa a jam’iyyar APC kuma ya lashe zaben shugaban kasa a shekarar 2023, ya fara aikinsa da kafar dama.”

tinubu

“Shugaba Tinubu ya yanke shawarar nada masu ba da shawara na musamman guda takwas, kuma wannan matakin ya samu karbuwa da farin ciki a fadin kasar nan, ciki har da ‘yan adawa. Wani abin lura a cikin wannan ci gaban shi ne babu wata adawa ko rashin jituwa dangane da wadannan nade-nade, wanda ke nuni da goyon bayan zaben da aka yi wa shugaban kasar.

“Wani nadin da ya sanya farin ciki a fadin kasar nan shi ne na mai ba da shawara na musamman kan harkokin tsaro. ‘Yan Nijeriya na da kyakkyawan fata na cewa Shugaba Tinubu zai magance kalubalen tsaro yadda ya kamata a wannan karon”.

A baya dai ANA ta jaddada cewa nasara ko gazawar da Tinubu zai samu zai ta’allaka ne a kan ayyukansa na yaki da rashin tsaro da cin hanci da rashawa, wadanda su ne manyan batutuwa biyu da suka addabi al’ummar kasar nan.

Daga cikin fitattun wadanda aka nada akwai Malam Nuhu Ribadu, wanda a baya ya rike mukamin Shugaban Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) a shekarar 2003. Idan aka duba, Ribadu, tarihinsa na nuna irin kishinsa, sadaukarwa, da kwazonsa na musamman wajen yaki da cin hanci da rashawa. A lokacin da yake rike da mukamin a hukumar ta EFCC, ya sa ido a kan kafa cibiyar horarwa a kan nazarin manyan laifuka da bincike, wanda hakan ya kara tabbatar da martabar hukumar a matsayin babbar hukumar tabbatar da doka a Afirka.

tinubu

Ribadu ya jajirce wajen neman adalci har aka karrama shi a matsayin wanda ake girmamawa a matsayin dan gwagwarmayar yaki da cin hanci da rashawa a duniya. Kin karbar cin hancin Naira miliyan 30 a shekarar 2005 da kuma cin hancin dala miliyan 15 daga hannun tsohon gwamna a 2007 a shekarar 2007 ya zama abin kwatance game da da’ar aiki.

Bugu da kari, Ribadu ya taka muhimmiyar rawa wajen fitar da Nijeriya daga cikin jerin kasashen kungiyar FATF, da samun damar shigarta kungiyar Egmont, da kuma tabbatar da janye Jami’an da ke sanya ido a kan manyan laifukan kudi a Baitul-malin Amurka daga Nijeriya.

A karshen taron dai, Arewa New Agenda ta yaba wa shugaban kasa Ahmed Bola Tinubu bisa kyakkawan jagorancinsa da tsarin gudanar da mulkinsa a cikin makonni biyun farko da hawansa karagai. Kungiyar ta yi imanin cewa, matakin da shugaban kasar ya dauka da abubuwan da yake aiwatarwa ne ya sanya Nijeriya ta fara jin kamshin kyakkyawar makoma.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: jagoranciKasaNijeriyaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hikimar Kasar Sin Ta Ba Da Gudummuwa Ga Ci Gaban Kungiyar SCO

Next Post

Hajjin Bana: NAHCON Ta Samar Da Biza 73,310, Tare Da Kai Alhazai 46,000 Kasar Saudiyya

Related

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano
Labarai

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

4 hours ago
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 
Labarai

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

5 hours ago
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi
Labarai

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

6 hours ago
Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore
Ra'ayi Riga

Wannan Kyakkyawan Tunani Ya Shafa Ma Hamadar Sahara Launin Kore

8 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

10 hours ago
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

10 hours ago
Next Post
Hajjin Bana: NAHCON Ta Samar Da Biza 73,310, Tare Da Kai Alhazai 46,000 Kasar Saudiyya

Hajjin Bana: NAHCON Ta Samar Da Biza 73,310, Tare Da Kai Alhazai 46,000 Kasar Saudiyya

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.