• English
  • Business News
Friday, June 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiya Ta Yaba Wa Shugaba Tinubu Kan Inganta Tsaro Da Yaki Da Rashawa

by Leadership Hausa
2 years ago
in Labarai, Kananan Labarai
0
Kungiya Ta Yaba Wa Shugaba Tinubu Kan Inganta Tsaro Da Yaki Da Rashawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Arewa New Agenda, mai fafutukar kare martaba da shigar Arewa cikin harkokin kasa, ta yaba wa Shugaban Kasa Ahmed Bola Tinubu bisa tsarin shugabancinsa tun hawansa mulki makonni biyu da suka gabata.

Shugaban kungiyar Sanata Ahmed Abubakar MoAllahyidi ne ya yi wannan yabon a wata ganawa da manema labarai a Abuja ranar Juma’a.

Arewa New Agenda ta bayyana wasu muhimman shawarwari da matakan da shugaban kasan ya dauka tun bayan hawansa mulki, wadanda suka hada da: soke tallafin man fetur, hana yajin aikin da kungiyoyin kwadago suka shirya yi a fadin kasa, da kafa tsarin kudin musaya na Naira bai-daya, da ganawa da shuwagabannin hukumomi masu muhimmanci tare da kai ziyara a cibiyoyin tsaro da tattara bayanan sirri da sauransu.

A cewar MoAllahyidi, “Wadannan matakai sun nuna jajircewar Shugaba Tinubu wajen tunkarar muhimman al’amurra a kasar nan da kuma samar da jagoranci nagari a harkokin mulki”.

“Nade-naden da Shugaba Tinubu ya yi ya haifar da samun kwarin gwiwa a kan ingantuwar tsaro da kuma yaki da cin hanci da rashawa”.

Labarai Masu Nasaba

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

“Muna farin ciki da cewa shugaban kasa Tinubu, wanda kungiyar ta goyi bayansa a lokacin da yake neman takararsa a jam’iyyar APC kuma ya lashe zaben shugaban kasa a shekarar 2023, ya fara aikinsa da kafar dama.”

tinubu

“Shugaba Tinubu ya yanke shawarar nada masu ba da shawara na musamman guda takwas, kuma wannan matakin ya samu karbuwa da farin ciki a fadin kasar nan, ciki har da ‘yan adawa. Wani abin lura a cikin wannan ci gaban shi ne babu wata adawa ko rashin jituwa dangane da wadannan nade-nade, wanda ke nuni da goyon bayan zaben da aka yi wa shugaban kasar.

“Wani nadin da ya sanya farin ciki a fadin kasar nan shi ne na mai ba da shawara na musamman kan harkokin tsaro. ‘Yan Nijeriya na da kyakkyawan fata na cewa Shugaba Tinubu zai magance kalubalen tsaro yadda ya kamata a wannan karon”.

A baya dai ANA ta jaddada cewa nasara ko gazawar da Tinubu zai samu zai ta’allaka ne a kan ayyukansa na yaki da rashin tsaro da cin hanci da rashawa, wadanda su ne manyan batutuwa biyu da suka addabi al’ummar kasar nan.

Daga cikin fitattun wadanda aka nada akwai Malam Nuhu Ribadu, wanda a baya ya rike mukamin Shugaban Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) a shekarar 2003. Idan aka duba, Ribadu, tarihinsa na nuna irin kishinsa, sadaukarwa, da kwazonsa na musamman wajen yaki da cin hanci da rashawa. A lokacin da yake rike da mukamin a hukumar ta EFCC, ya sa ido a kan kafa cibiyar horarwa a kan nazarin manyan laifuka da bincike, wanda hakan ya kara tabbatar da martabar hukumar a matsayin babbar hukumar tabbatar da doka a Afirka.

tinubu

Ribadu ya jajirce wajen neman adalci har aka karrama shi a matsayin wanda ake girmamawa a matsayin dan gwagwarmayar yaki da cin hanci da rashawa a duniya. Kin karbar cin hancin Naira miliyan 30 a shekarar 2005 da kuma cin hancin dala miliyan 15 daga hannun tsohon gwamna a 2007 a shekarar 2007 ya zama abin kwatance game da da’ar aiki.

Bugu da kari, Ribadu ya taka muhimmiyar rawa wajen fitar da Nijeriya daga cikin jerin kasashen kungiyar FATF, da samun damar shigarta kungiyar Egmont, da kuma tabbatar da janye Jami’an da ke sanya ido a kan manyan laifukan kudi a Baitul-malin Amurka daga Nijeriya.

A karshen taron dai, Arewa New Agenda ta yaba wa shugaban kasa Ahmed Bola Tinubu bisa kyakkawan jagorancinsa da tsarin gudanar da mulkinsa a cikin makonni biyun farko da hawansa karagai. Kungiyar ta yi imanin cewa, matakin da shugaban kasar ya dauka da abubuwan da yake aiwatarwa ne ya sanya Nijeriya ta fara jin kamshin kyakkyawar makoma.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: jagoranciKasaNijeriyaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hikimar Kasar Sin Ta Ba Da Gudummuwa Ga Ci Gaban Kungiyar SCO

Next Post

Hajjin Bana: NAHCON Ta Samar Da Biza 73,310, Tare Da Kai Alhazai 46,000 Kasar Saudiyya

Related

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP
Labarai

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

1 hour ago
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 
Labarai

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

2 hours ago
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi
Daga Birnin Sin

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

10 hours ago
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210
Manyan Labarai

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

11 hours ago
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

13 hours ago
Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
Manyan Labarai

Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji

15 hours ago
Next Post
Hajjin Bana: NAHCON Ta Samar Da Biza 73,310, Tare Da Kai Alhazai 46,000 Kasar Saudiyya

Hajjin Bana: NAHCON Ta Samar Da Biza 73,310, Tare Da Kai Alhazai 46,000 Kasar Saudiyya

LABARAI MASU NASABA

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)

June 27, 2025
Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP

June 27, 2025
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana 

June 27, 2025
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

June 26, 2025
Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

Tinubu Ya Nemi Ƴan Nijeriya Su Taimaka A Yaƙi Shan Muggan Kwayoyi

June 26, 2025
An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome

June 26, 2025
NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

NNPC Ta Gaza Halartar Zaman Binciken Majalisa Kan Ɓatan Naira Tiriliyan 210

June 26, 2025
Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Na Ci Gaba Da Ba Da Gudunmuwa Ga Habakar Tattalin Arzikin Duniya

June 26, 2025
Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

Kashim Shettima Ya Tafi Habasha Ziyarar Aiki

June 26, 2025
Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin

June 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.