ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Kare Hakkin Dan’adam Ta Yi Tir Da Korar Malamai A Kaduna

by Shehu Yahaya
3 years ago
Kaduna

Kungiyar marubuta kare hakkokin Dan’adam ta Nijeriya (HURIWA) ta yi tir da matakin gwamnatin Jihar Kaduna karkashin jagorancin Gwamna Nasiru el-Rufa’i na korar malaman makarantu da ta yi, inda ta bayyana hukuncin a matsayin daukar fansa ba bisa ka’ida ba kuma abin Allah wadai.

Malaman da aka kora sun hada da shugaban kungiyar malamai ta kasa (NUT), Audu Amba, wanda aka kora bisa zargin kin yin jarabawar cancanta da hukumar ilimin bai-daya ta jihar (KADSUBEB) ta shirya.

  • Gwamnatin Kaduna Ta Sake Sallamar Malaman Makaranta 2,357 Daga Aiki

HURIWA ta goyi bayan shugaban kungiyar NUT na jihar wanda tun da farko ya bayyana korar malaman a matsayin haramtacce.

ADVERTISEMENT

Kungiyar kare hakkin ta ce matakin korar malamai a jihar ya saba wa sashi na 42 na kundin tsarin mulkin kasa, domin a cewar kungiyar, “Gwamnan da yake ma’aikacin ne a jihar da wadanda ya nada ba a yi musu irin wannan gwajin cancantar ba, sai a kan malamai, tabbas akwai nuna wariya,” in ji kungiyar.

Hakazalika, shi ma dan takarar gwamnan Jihar Kaduna na jam’iyyar PDP, Isah Ashiru Kudan, ya yi kira ga gwamnan Nasir el-Rufa’i ya dakatar da korar ma’aikatan da yake yi a jihar ba tare da bata lokaci ba.

LABARAI MASU NASABA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

Isah Ashiru ya soki hakan ne a cikin wani sako da ya fitar, inda ya ce a wannan lokaci da talaka ke hannu-baka-hannu- kwarya bai kamata a ce an gallaza masa da irin wannan azaba ta korar aiki da rana tsaka ba.

Ya ce ana fama da talauci da wahalhalun rayuwa sai kuma a wayi gari dan aikin da talaka ke samun abinci an kore shi, wannan rashin imani ne.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle
Manyan Labarai

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS
Labarai

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS
Labarai

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
Next Post
Da Aka Gama Rarraba Wa Deliget Kudi, Sai Kuma Me? (Ra’ayinmu)

Da Aka Gama Rarraba Wa Deliget Kudi, Sai Kuma Me? (Ra'ayinmu)

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.