• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Mata Lauyoyi Na Bukatar Sanya Mata A Gaba A Fannin Fasaha Da Kirkire-Kirkire

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Kungiyar Mata Lauyoyi Na Bukatar Sanya Mata A Gaba A Fannin Fasaha Da Kirkire-Kirkire
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata Kungiyar mata lauyoyi ta kasa ‘International Federation of Women Lawyers’ (FIDA), ta nuna bukatar da ke akwai na sakarwa mata cikakkiyar dama domin su baje baiwar fasahar da Allah ya huwace musu ta hanyar amfani da fasahar zamani, kimiyya da kuma kirkire-kirkire.

A wata sanarwar da shugabar kungiyar reshen jihar Bauchi, Fatima Abubakar ta fitar domin raya ranar mata ta duniya na wannan shekarar mai taken Maida hankali kan rawar da kirkire-kirkire da fasaha ke takawa wajen inganta daidaiton jinsi a tsakanin maza da mata.

  • ‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa 2 Da Ceto Mutum 1 A Bauchi
  • An Fara Gwagwarmayar Neman Shugabancin Majalisun Kasa

FITA ta ce, lura da yadda zamani ke tafiya a halin yanzu, kirkira da fasaha su ne hanyoyi da suka fi dace a maida hankali a kai. Kana, sannu a hankali fasaha na shiga cikin harkokin rayuwa na yau da gobe, ayyukanmu, sadarwa, hada-hadar cinikayya, koyo da koyarwa da kuma sha’anin sarrafa kudade.

Kazalika, kungiyar ta nuna damuwarta kan yadda mata kalilan ke samun dama wajen baje baiwar da Allah ya musu na fasaha a wurare daban-daban.

“Mun yi la’alari da kalubalen da mata ke fuskanta a wannan fannin saboda yadda aka saba tun da farko bisa al’adar da ya dakile mata musamman iyaye.

Labarai Masu Nasaba

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

“Fasaha ya bude sabon babi wa mata a bangaren aiki domin kuwa su na samun damar tafiyar da harkokinsu na kashin kai da kuma na ayyukansu da shi.

“Ko a lokacin annobar Korona da ya tilasta wa mata aiki daga gida. Mun jinjina wa kokarin mata ta yadda suka tashi suka koya suka kuma rungumi amfani da kimiyya da fasaha.”

FIDA ta kara da cewa, bisa rungumar kimiyya da mata suka yi, hakan ya bude musu sabbon babin koyon ilimi ta yadda suke iya amfani da shiga dauran darussan kwasa-kwasai ta hanyar yanar gizo a fadin duniya, “Hakan ya bude damarmaki sosai masu kyau da nagarta ga ‘yan uwa mata da ke taimaka mana a fannonin aikinmu sosai.”

Don haka FIDa ta ce, akwai gayar bukatar a cire dukkanin wani banbance-banbancen da ke dakile mata daga shiga a dama da su a harkar kimiyya, kungiyar tana mai cewa babu wani nau’in fasaha da wani namiji zai iya shiga a dama da shi da mata ma ba za su iya yin hakan ba.

Fatima ta karfafi mata a Nijeriya da suke shiga a dama da su a dukkanin wani gasa ko gabzatar gwajin fasaha da ake sanyawa a ko’ina a duniya domin bai wa mata cikakken dama da kwarin guiwar amfanuwa da kimiyya tare da kara samun damarmaki a fannin. Ta kuma nemi masu ruwa da tsaki da suke daukan nauyin mata wajen neman ilimi a fannin kimiyya, Fasaha da lisasafi (STEM) domin karfafa wa mata masu tasowa guiwa.

Kazalika, kungiyar ta ce akwai kuma bukatar cigaba da wayar wa yara mata alfanun da kimiyya ke da shi a garesu da cigaban al’umma.

Daga bisani kungiyar ta yi sha’awar a shawo kan banbance-banbance da ake da su a tsakanin maza da mata a fannin kimiyya da Fasaha domin Mata na suke samun cikakken damar guragwn ayyukan yi da bada nasu gudunmawar a cikin al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Kotun Koli Ta Umarci INEC Ta Maye Sunan Shekarau Da Hanga

Related

Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi

4 weeks ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum 245 Da Miyagun Kwayoyi Da Makamai A Abuja

2 months ago
‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda A Legas Sun Kama Mutum 35 Da Ake Zargi Da Fashi Cikin Mako Guda

2 months ago
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Na Farautar Wadanda Suka Kashe Dalibi A Katsina

2 months ago
Rikita-rikitar Da Ta Biyo Bayan Mutuwar Mawaki Mohbad
Kotu Da Ɗansanda

MohBad: Nurse Za Ta Fuskanci Shari’a, Sannan Kotu Ta Wanke Naira Marley, Sam Larry Da PrimeBoy

2 months ago
‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kubutar Da Wata Mata Da Aka Yi Garkuwa Da Ita A Otal Din Abuja

3 months ago
Next Post
Kotun Koli Ta Umarci INEC Ta Maye Sunan Shekarau Da Hanga

Kotun Koli Ta Umarci INEC Ta Maye Sunan Shekarau Da Hanga

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta Ɗage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.