• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Mata Lauyoyi Na Bukatar Sanya Mata A Gaba A Fannin Fasaha Da Kirkire-Kirkire

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
Kungiyar Mata Lauyoyi Na Bukatar Sanya Mata A Gaba A Fannin Fasaha Da Kirkire-Kirkire
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata Kungiyar mata lauyoyi ta kasa ‘International Federation of Women Lawyers’ (FIDA), ta nuna bukatar da ke akwai na sakarwa mata cikakkiyar dama domin su baje baiwar fasahar da Allah ya huwace musu ta hanyar amfani da fasahar zamani, kimiyya da kuma kirkire-kirkire.

A wata sanarwar da shugabar kungiyar reshen jihar Bauchi, Fatima Abubakar ta fitar domin raya ranar mata ta duniya na wannan shekarar mai taken Maida hankali kan rawar da kirkire-kirkire da fasaha ke takawa wajen inganta daidaiton jinsi a tsakanin maza da mata.

  • ‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa 2 Da Ceto Mutum 1 A Bauchi
  • An Fara Gwagwarmayar Neman Shugabancin Majalisun Kasa

FITA ta ce, lura da yadda zamani ke tafiya a halin yanzu, kirkira da fasaha su ne hanyoyi da suka fi dace a maida hankali a kai. Kana, sannu a hankali fasaha na shiga cikin harkokin rayuwa na yau da gobe, ayyukanmu, sadarwa, hada-hadar cinikayya, koyo da koyarwa da kuma sha’anin sarrafa kudade.

Kazalika, kungiyar ta nuna damuwarta kan yadda mata kalilan ke samun dama wajen baje baiwar da Allah ya musu na fasaha a wurare daban-daban.

“Mun yi la’alari da kalubalen da mata ke fuskanta a wannan fannin saboda yadda aka saba tun da farko bisa al’adar da ya dakile mata musamman iyaye.

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

“Fasaha ya bude sabon babi wa mata a bangaren aiki domin kuwa su na samun damar tafiyar da harkokinsu na kashin kai da kuma na ayyukansu da shi.

“Ko a lokacin annobar Korona da ya tilasta wa mata aiki daga gida. Mun jinjina wa kokarin mata ta yadda suka tashi suka koya suka kuma rungumi amfani da kimiyya da fasaha.”

FIDA ta kara da cewa, bisa rungumar kimiyya da mata suka yi, hakan ya bude musu sabbon babin koyon ilimi ta yadda suke iya amfani da shiga dauran darussan kwasa-kwasai ta hanyar yanar gizo a fadin duniya, “Hakan ya bude damarmaki sosai masu kyau da nagarta ga ‘yan uwa mata da ke taimaka mana a fannonin aikinmu sosai.”

Don haka FIDa ta ce, akwai gayar bukatar a cire dukkanin wani banbance-banbancen da ke dakile mata daga shiga a dama da su a harkar kimiyya, kungiyar tana mai cewa babu wani nau’in fasaha da wani namiji zai iya shiga a dama da shi da mata ma ba za su iya yin hakan ba.

Fatima ta karfafi mata a Nijeriya da suke shiga a dama da su a dukkanin wani gasa ko gabzatar gwajin fasaha da ake sanyawa a ko’ina a duniya domin bai wa mata cikakken dama da kwarin guiwar amfanuwa da kimiyya tare da kara samun damarmaki a fannin. Ta kuma nemi masu ruwa da tsaki da suke daukan nauyin mata wajen neman ilimi a fannin kimiyya, Fasaha da lisasafi (STEM) domin karfafa wa mata masu tasowa guiwa.

Kazalika, kungiyar ta ce akwai kuma bukatar cigaba da wayar wa yara mata alfanun da kimiyya ke da shi a garesu da cigaban al’umma.

Daga bisani kungiyar ta yi sha’awar a shawo kan banbance-banbance da ake da su a tsakanin maza da mata a fannin kimiyya da Fasaha domin Mata na suke samun cikakken damar guragwn ayyukan yi da bada nasu gudunmawar a cikin al’umma.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

GORON JUMA’A

Next Post

Kotun Koli Ta Umarci INEC Ta Maye Sunan Shekarau Da Hanga

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

3 weeks ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

3 weeks ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

3 weeks ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

4 weeks ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

4 weeks ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

4 weeks ago
Next Post
Kotun Koli Ta Umarci INEC Ta Maye Sunan Shekarau Da Hanga

Kotun Koli Ta Umarci INEC Ta Maye Sunan Shekarau Da Hanga

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.