ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, September 11, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Fara Gwagwarmayar Neman Shugabancin Majalisun Kasa

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
majalisar kasa

A wani wani yanayi na ba-zata, za a kaddamar da majalisar kasa ta 10 a ranar Talata, 13 ga watan Yunin 2023, kwana biyu bayan wa’adin majalisar ta 9 zai kare a  ranar Lahadi 11 ga watan Yuni.

Idan za a iya tunawa cewa majalisar dokoki ta kasa mai ci an bude ta ne a ranar 11 ga watan Yunin 2019. Tsawon rayuwarta zai kare ne a ranar 11 ga watan Yunin 2023 wato Lahadi, ranar da ba a yin aiki, yayin ranar 12 ga watan Yuni ya kasance ranar hutun dimokuradiyya.

  • 2023: Majalisar Dattawa Ta Kasa, Ta Tafi Hutun Wata Daya

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, mambobin majalisa ta 10 da aka zaba wadanda suka hada da sanatoci da ‘yan jamalisan wakilai za su karbi shaidar takararsu a ranakun Talata da Laraba 7 da 8 ga watan Fabrairu, bayan da aka bayyana su a matsayin wadanda suka lashe zaben ‘yan majalisar dokokin Nijeriya da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu.

ADVERTISEMENT

Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, a ranar Asabar da ta gabata yayin wata ganawa da kwamishinonin zabe gabanin zaben Gwamna da na ‘yan majalisar jiha da za a yi a ranar 11 ga Maris, ya bayyana cewa ta fuskar wakilcin jam’iyya, majalisar kasa ta 10 mai zuwa ita ce mafi yawan bambancin tun 1999.

Ya ce a zuwa yanzu dai a majalisar dattawa, jam’iyyar APC mai mulki ta samu kujeru 57, yayin da babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta samu kujeru 29.

LABARAI MASU NASABA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

Sauran sun hada da APGA wacce ta samu guda, Jam’iyyar LP ta samu 6, Jam’iyyar NNPP ta samu 2, SDP ta samu 2, sai kuma YPP wacce ta samu daya.

A majalisar wakilai kuwa, APC ta lashe kujeru 162, PDP ta samu 102, APGA ta samu 4, LP ta samu 34, NNPP na da 18, SDP tana da 2, YPP ta samu 1, sannan kuma ADC ta samu 2.

Idan aka yi la’akari da wannan tsari na sama jerin yawan jam’iyyun, zaben shugabannin majalisun biyu na 10 zai yi matukar zama mai abun sha’awa.

Gabanin kaddamar da majalisar dokokin kasar karo na 10 a ranar 13 ga watan Yunin 2023, wasu zababbun ‘yan majalisa sun fara fafutukar neman shugabancin majalisar dattawa da shugaban majalisar wakilai.
Baya ga shugabancin majalisar dattawa da shugaban majalisan wakilai, sauran mukaman da za a nada sun hada da na mataimakin shugaban majalisar dattawa da mataimakin shugaban majalisar wakilai.

Sakamakon binciken LEADERSHIP ya nuna cewa an fara zawarcin ofisoshin a tsakanin jam’iyya mai mulki tare da zababbun ‘yan majalisar dattawa da zababbun ‘yan majalisar wakilai na jam’iyyar APC da ke kokarin ganin ba a sake kuskuren 2015 a zaben shugabannin majalisar ba, inda aka zabi Sanata Bukola Saraki a matsayin shugaban majalisar dattawa, sannan aka zabi Yakubu Dogara a matsayin shugaban majalisar wakilai sabanin zabin jam’iyya mai mulki.

Duk da cewa jam’iyyar APC mai mulki, wadda tabbas za ta samu rinjaye a majalisun biyu na 10, har yanzu ba ta fito da wani tsari na shiyya-shiyya ko raba madafun iko na gwamnati mai zuwa karkashin jagorancin Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ba, tuni wasu daga cikin zababbun ‘yan majalisar tuni suka shiga tattaunawa ta bayan fage domin samun manyan mukaman a majalisar dokokin kasar da za ta fara aiki a ranar 13 ga watan Yuni.

Wadanda suka nuna sha’awarsu na zama shugaban majalisar dattawa ta 10 sun hada da zababben Sanata Orji Uzor Kalu (daga Abia ta Arewa), zababben Sanata Godswill Akpabio (daga Akwa Ibom ta arewa masu yamma), zababben Sanata Ali Ndume (daga Borno ta Kudu), da Sanata Jibrin Barau (daga Kano ta arewa).

Yayin da Kalu, Ndume da Barau suka kasance mambobi a majalisan dattawa ta 9 a halin yanzu, sai dai shi Akpabio ya kasance dan majalisar dattawa ta 8, wanda ke shirin komawa majalisar dattawa na 10.

Sai dai LEADERSHIP ta yi amanna cewa shugaban majalisar dattawa na yanzu, Ahmed Lawan, dan jam’iyyar APC daga yankin Yobe ta Arewa zai so ya ci gaba da rike mukaminsa idan akasarin sanatoci suka mara masa baya. Amma lokaci ne kawai zai nuna.

A halin da ake ciki a majalisar wakilai kuwa, shugaban majalisan na yanzu, Femi Gbajabiamila, wanda ke zama na hannun daman zababben Shugaban kasa, Bola Tinubu, na iya son gwada sa’arsa don ya ci gaba da rike mukaminsa a majalisa mai zuwa. Zai hau kan tasirin Tinubu don yin hakan idan lokaci ya yi.

Kafin hakan ta faru, Gbajabiamila zai samu manyan abokan hamayyar da zai yi takara da su wadanda suka hada da Hon. Ado Doguwa daga Jihar Kano da Hon. Aliyu Betara daga Jihar Borno da kuma sauran jiga-jigan ‘yan majalisa.

Majalisun kasa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe

September 5, 2026
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta

September 4, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027

August 28, 2026
Next Post
Goro

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

Ding Xuexiang Ya Halarci Taron Kolin CIFTIS Tare Da Ganawa Da Manyan Jami’an Kasashen Waje

September 10, 2026
Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

Sin Ce Ta Zo Ta Farko A Rahoton Yanayin Tsaron Jama’a Na Duniya

September 10, 2026
Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

Sin Ta Ciri Tuta Game Da Rawar Gani Da Take Takawa A Fannin Warware Kalubalen Tsaro A Gabas Ta Tsakiya

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

Gwamnatin Tarayya Ta Gwangwaje Tawagar Kwallon Kwando Ta Mata Da Dala 100,000 Kowace

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

Sin Da Amurka Na Gudanar Da Tattaunawa Dangane Da Yiwuwar Rage Harajin Ramuwar Gayya Wanda Darajarsa Ka Iya Kaiwa Dala Biliyan 30

September 10, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar da Shirin Ƙara Kuɗin Jarabawar WAEC da NECO

Gwamnatin Tarayya Za Ta Rika Bai Wa Ɗalibai 100MB Na Data Kyauta Kullum

September 10, 2026
Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

Sin Da Amurka Na Wanzar Da Mu’amala Game Da Shirin Ganawar Da Manyan Shugabannin Kasashen Biyu Za Su Yi A Bana

September 10, 2026
Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji Uku Da ‘Yan Bindiga Suka Harba A Filato

September 10, 2026
Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

Xi Zai Halarci Taron BRICS Karo Na 18 A Indiya

September 10, 2026
Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

Rodri Ya Nemi Afuwar Valencia Dangane Da Kalaman Da Yayi Akanta

September 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.