ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

An Fara Gwagwarmayar Neman Shugabancin Majalisun Kasa

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
majalisar kasa

A wani wani yanayi na ba-zata, za a kaddamar da majalisar kasa ta 10 a ranar Talata, 13 ga watan Yunin 2023, kwana biyu bayan wa’adin majalisar ta 9 zai kare a  ranar Lahadi 11 ga watan Yuni.

Idan za a iya tunawa cewa majalisar dokoki ta kasa mai ci an bude ta ne a ranar 11 ga watan Yunin 2019. Tsawon rayuwarta zai kare ne a ranar 11 ga watan Yunin 2023 wato Lahadi, ranar da ba a yin aiki, yayin ranar 12 ga watan Yuni ya kasance ranar hutun dimokuradiyya.

  • 2023: Majalisar Dattawa Ta Kasa, Ta Tafi Hutun Wata Daya

LEADERSHIP ta ruwaito cewa, mambobin majalisa ta 10 da aka zaba wadanda suka hada da sanatoci da ‘yan jamalisan wakilai za su karbi shaidar takararsu a ranakun Talata da Laraba 7 da 8 ga watan Fabrairu, bayan da aka bayyana su a matsayin wadanda suka lashe zaben ‘yan majalisar dokokin Nijeriya da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu.

ADVERTISEMENT

Shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Mahmood Yakubu, a ranar Asabar da ta gabata yayin wata ganawa da kwamishinonin zabe gabanin zaben Gwamna da na ‘yan majalisar jiha da za a yi a ranar 11 ga Maris, ya bayyana cewa ta fuskar wakilcin jam’iyya, majalisar kasa ta 10 mai zuwa ita ce mafi yawan bambancin tun 1999.

Ya ce a zuwa yanzu dai a majalisar dattawa, jam’iyyar APC mai mulki ta samu kujeru 57, yayin da babbar jam’iyyar adawa ta PDP ta samu kujeru 29.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Sauran sun hada da APGA wacce ta samu guda, Jam’iyyar LP ta samu 6, Jam’iyyar NNPP ta samu 2, SDP ta samu 2, sai kuma YPP wacce ta samu daya.

A majalisar wakilai kuwa, APC ta lashe kujeru 162, PDP ta samu 102, APGA ta samu 4, LP ta samu 34, NNPP na da 18, SDP tana da 2, YPP ta samu 1, sannan kuma ADC ta samu 2.

Idan aka yi la’akari da wannan tsari na sama jerin yawan jam’iyyun, zaben shugabannin majalisun biyu na 10 zai yi matukar zama mai abun sha’awa.

Gabanin kaddamar da majalisar dokokin kasar karo na 10 a ranar 13 ga watan Yunin 2023, wasu zababbun ‘yan majalisa sun fara fafutukar neman shugabancin majalisar dattawa da shugaban majalisar wakilai.
Baya ga shugabancin majalisar dattawa da shugaban majalisan wakilai, sauran mukaman da za a nada sun hada da na mataimakin shugaban majalisar dattawa da mataimakin shugaban majalisar wakilai.

Sakamakon binciken LEADERSHIP ya nuna cewa an fara zawarcin ofisoshin a tsakanin jam’iyya mai mulki tare da zababbun ‘yan majalisar dattawa da zababbun ‘yan majalisar wakilai na jam’iyyar APC da ke kokarin ganin ba a sake kuskuren 2015 a zaben shugabannin majalisar ba, inda aka zabi Sanata Bukola Saraki a matsayin shugaban majalisar dattawa, sannan aka zabi Yakubu Dogara a matsayin shugaban majalisar wakilai sabanin zabin jam’iyya mai mulki.

Duk da cewa jam’iyyar APC mai mulki, wadda tabbas za ta samu rinjaye a majalisun biyu na 10, har yanzu ba ta fito da wani tsari na shiyya-shiyya ko raba madafun iko na gwamnati mai zuwa karkashin jagorancin Asiwaju Bola Ahmed Tinubu ba, tuni wasu daga cikin zababbun ‘yan majalisar tuni suka shiga tattaunawa ta bayan fage domin samun manyan mukaman a majalisar dokokin kasar da za ta fara aiki a ranar 13 ga watan Yuni.

Wadanda suka nuna sha’awarsu na zama shugaban majalisar dattawa ta 10 sun hada da zababben Sanata Orji Uzor Kalu (daga Abia ta Arewa), zababben Sanata Godswill Akpabio (daga Akwa Ibom ta arewa masu yamma), zababben Sanata Ali Ndume (daga Borno ta Kudu), da Sanata Jibrin Barau (daga Kano ta arewa).

Yayin da Kalu, Ndume da Barau suka kasance mambobi a majalisan dattawa ta 9 a halin yanzu, sai dai shi Akpabio ya kasance dan majalisar dattawa ta 8, wanda ke shirin komawa majalisar dattawa na 10.

Sai dai LEADERSHIP ta yi amanna cewa shugaban majalisar dattawa na yanzu, Ahmed Lawan, dan jam’iyyar APC daga yankin Yobe ta Arewa zai so ya ci gaba da rike mukaminsa idan akasarin sanatoci suka mara masa baya. Amma lokaci ne kawai zai nuna.

A halin da ake ciki a majalisar wakilai kuwa, shugaban majalisan na yanzu, Femi Gbajabiamila, wanda ke zama na hannun daman zababben Shugaban kasa, Bola Tinubu, na iya son gwada sa’arsa don ya ci gaba da rike mukaminsa a majalisa mai zuwa. Zai hau kan tasirin Tinubu don yin hakan idan lokaci ya yi.

Kafin hakan ta faru, Gbajabiamila zai samu manyan abokan hamayyar da zai yi takara da su wadanda suka hada da Hon. Ado Doguwa daga Jihar Kano da Hon. Aliyu Betara daga Jihar Borno da kuma sauran jiga-jigan ‘yan majalisa.

Majalisun kasa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Majalisun kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Goro

GORON JUMA’A

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.