• English
  • Business News
Tuesday, May 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Mata Masu Yaki Da Shaye-shaye A Kano Ta Sha Damara – Dakta Fauziyya

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
in Rahotonni
0
Kungiyar Mata Masu Yaki Da Shaye-shaye A Kano Ta Sha Damara – Dakta Fauziyya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

DAKTA FAUZIYYA BUBA IDRIS ita ce mataimakiya ta musamman ga Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje kan harkokin Lafiya, babbar jakadiya ga kokarin Mai Dakin Gwamnan Kano Farfesa Hafsat Ganduje wadda ke jagorantar gangamin kaddamar da dakarun Mata masu yaki da shaye-shayen Miyagun Kwayoyi a Kano.

Dakta Fauziya gogaggiyar likitar Mata ce sannan ‘yar siyasa mai rajin inganta rayuwar Mata da Kananan Yara.

  • Hanyoyin Kula Da Fatar Jiki (4)
  • Xi Ya Jaddada Bukatar Inganta Farfado Da Yankunan Karkara

 A tattaunawartar ta Wakilinmu a Kano ABDULLAHI MUHAMMAD SHEKA, Dakta Fauziyya ta jinjina wa kokarin Mai Dakin Gwamnan Kano bias kyakkawar kulawar da take bai wa Harkokin Mata da Kananan Yara, ta kuma bayyana bukatar kowa a cikin al’umma su kawo nasu gudummawar don ganin an kawo karshen shaye-shayen miyagun kwayoyi a Jihar Kano. Ga dai yadda tattaunawar ta Kasance:

Za muso jin wanda muke tare da ita a halin yanzu

Sunana Dakta Fauziyya Buba Idris mashawarciya ta musammana kan harkokin lafiya ga Gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje, sannan kuma jagorar aiwatar da kudurin Mai Dakin Gwamna Farfesa Hafsat Ganduje na kaddamar da dakarun yaki da shaye-shaye Miyagun Kwayoyi a fadin kananan Hukumomin Jihar Kano 44

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

Mene dalilin kokarin samar da dakarun Mata wadanda za su yi aiki wajen dakile matsalar shaye -shayen Miyagun Kwayoyi a tsakanin matasa?

Alhamdulillahi kullum Mai Dakin Gwamna damuwarta shi ne ta ga yara Mata da maza na kara tsunduma cikin wannan mummunar ta’ada, wannan ta sa ta yanke shawarar samar da dakarun Mata domin iyaye mata suke galabaita da wannan matsala domin su ake bari da dawainiya da yara a gida ko makarantu.  Saboda haka ta kirkiri wannan aiki wanda zuwa yanzu mun kusa kamala karade Kananan Hukumomin Jihar Kano 44 tare da kaddamar da wadannan da karu.

Mene ayyukan wadannan dakaru?

Aikinsu shi ne shiga cikin gidaje domin fadakar da iyaye Mata illar ta’ammali da Miyagun Kwayoyi, sannan kuma mace tafi kowa sanin matsalar ‘yar uwarta mace, wadannan dakaru na da karfin guiwar tunkarar kowacce uwa da aka hangi danta a ciki masu irin wannan matsala kuma a yi mata gargadi tare da wayar da kanta domin kara himma wajen Lura da mu’amalar yaranta sannan kuma an samar da tsare-tsare na fadakar da duk wanda yantsunci kansa a irin wannan matsala.

Mene kuke ganin na kara ta’azzara wannan matsala tashaye-shaye?

Daga ciki akwai matsalar rabuwar iyali, muna nan abokai, damuwa, talauci da sakacin Iyaye, wadannan na cikin abubuwan da ke kara rura wutar matsalar shaye-shayea tsakanin matasa. Sai Kuma rashin samun ingantaccen Ilimi da kulawar iyaye.

Dakta kasancewar ki Mace kuma likita sannan gashi kina zaman mashawarciya ga Gwamna kan Harkokin Lafiya, shin ko ya kike kallon matsalar da a halin ake fuskanta na shigar Mata har ma da matan aure cikin matsalar Shaye-shayen miyagun kwayoyi?

Gaskiya wannan lamari ne mai tada hankali, kuma shi Mai Dakin Gwamna Farfesa Hafsat Ganduje ta kalla kuma ta himmatu wajen neman hanyar magance matsalar, Alhamdulillahi Jihar Kano mun yi dacen Gwamna wanda kullum damuwarsa ita ce ya za a Inganta rayuwar al’umma, wannan tasa shi ne Gwamna daya tilo da ya fara zartar da dokar dole duk wani mai neman takara ko nadi a mukamin Gwamnati sai an gwada kwakwalwarsa, kuma yanzu kowa ya Fara ganin tasirin wannan kokari na Gwamna Ganduje.

Ana samun yawaitar kwararar masu tallace-tallacen maganunuwa a kan Tituna da kasuwanni, wanda a lokuta da dama suke yin amfani da wasu kalmomi da ba su dace da harshen Hausa da al’adun mu ba Kai har ma da addini, shin ko akwai wannan matsala?

Babu shakka tuni wannan Gwamnati tare da hadin kan Ma’aikatar Lafiya Gwamnati ta bijiro da wasu dokoki ga duk wanda ke bukatar tallan Maganin Gargajiya ko makamancinsa, sannan dole mutum ya je a tantance shi tare don yi masa rijista, sannana na shirya masu taron bita lokaci zuwa lokaci domin kara samun wayewa da kwarewa ta fuskar sana’arsu.

Wane kira za ki yi musamman ga matasa a lokaci irin wannan da aka fara kada kugen siyasa?

Daman tuni Gwamna ya ja kunnen Jama’a musamman ‘yan Jam’iyyar APC cewar kar wanda ya bari aka yi amfani da shi wajen tunzura matasa ko amfani da kayan maye ko makamai a lokacin yakin Neman Zabe, wannan tasa yanzu matasa a Kano an daina tunzura su aikata bangar siyasa.

Mun gode kwarai da gaske

Ni ma na gode


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GandujekanoKungiyaMashawarciyaMata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kawancen Sin Da Afrika Na Da Muhimmanci Ga Cimma Ajandun Nahiyar Da Na Duniya

Next Post

Wurin Adana Kayan Tarihi Na Shaida Al’adun Kasa

Related

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi
Rahotonni

Gwamna Umar Namadi Ya Dauki Matakan Kai Jihar Jigawa Babban Matsayi

1 month ago
Janar Tiani Ya Fara Sabon Mulkin Shekaru Biyar A Nijar
Rahotonni

Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro

1 month ago
An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya
Rahotonni

An Gudanar Da Taron Zaman Lafiya Tsakanin Manoma Da Makiyaya

1 month ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Rahotonni

Amurka Ta Sayi Kayayyakin Nijeriya Na Dala Miliyan 643 A Wata 2 – Rahoto

1 month ago
Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi
Rahotonni

Gwamnoni 20 Na Fuskantar Matsin Lambar NULGE Kan Rashin Aiwatar Da Mafi Karanci Albashi

1 month ago
Tinubu
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027

2 months ago
Next Post
Wurin Adana Kayan Tarihi Na Shaida Al’adun Kasa

Wurin Adana Kayan Tarihi Na Shaida Al’adun Kasa

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-yanzu: Tukunyar Gas Ta Fashe A Harabar Filin Wasannin Na Kasa Da Ke Gudana A Ogun

Yanzu-yanzu: Tukunyar Gas Ta Fashe A Harabar Filin Wasannin Na Kasa Da Ke Gudana A Ogun

May 20, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Dandalin SCO Na 2025

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Dandalin SCO Na 2025

May 20, 2025
Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo

Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo

May 20, 2025
Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya

Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya

May 20, 2025
Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola

Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola

May 20, 2025
Ana Zargin ‘Yansanda Da Keta Haddin Dan Jarida A Kano

‘Yansanda Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Fashi, Sun Kama Wasu 7 A Abuja

May 20, 2025
An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

May 20, 2025
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu

DSS Ta Cafke Ɗan Bindiga Yayin Da Yake Shirin Tafiya Aikin Hajji A Sakkwato 

May 20, 2025
NiDCOM Ta Ceto ‘Yan Nijeriya 13 Da Aka Yi Safarar Zuwa Ghana Da Mali

NiDCOM Ta Ceto ‘Yan Nijeriya 13 Da Aka Yi Safarar Zuwa Ghana Da Mali

May 20, 2025
Shugaban Kasar Colombia: Ayyukan Kasar Sin Sun Nuna Wani Sabon Salo Na Ci Gaban Zamantakewar Al’ummar Bil’adama

Shugaban Kasar Colombia: Ayyukan Kasar Sin Sun Nuna Wani Sabon Salo Na Ci Gaban Zamantakewar Al’ummar Bil’adama

May 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.