• English
  • Business News
Monday, September 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Mata Masu Yaki Da Shaye-shaye A Kano Ta Sha Damara – Dakta Fauziyya

by Abdullahi Muh'd Sheka
3 years ago
in Rahotonni
0
Kungiyar Mata Masu Yaki Da Shaye-shaye A Kano Ta Sha Damara – Dakta Fauziyya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

DAKTA FAUZIYYA BUBA IDRIS ita ce mataimakiya ta musamman ga Gwamnan Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje kan harkokin Lafiya, babbar jakadiya ga kokarin Mai Dakin Gwamnan Kano Farfesa Hafsat Ganduje wadda ke jagorantar gangamin kaddamar da dakarun Mata masu yaki da shaye-shayen Miyagun Kwayoyi a Kano.

Dakta Fauziya gogaggiyar likitar Mata ce sannan ‘yar siyasa mai rajin inganta rayuwar Mata da Kananan Yara.

  • Hanyoyin Kula Da Fatar Jiki (4)
  • Xi Ya Jaddada Bukatar Inganta Farfado Da Yankunan Karkara

 A tattaunawartar ta Wakilinmu a Kano ABDULLAHI MUHAMMAD SHEKA, Dakta Fauziyya ta jinjina wa kokarin Mai Dakin Gwamnan Kano bias kyakkawar kulawar da take bai wa Harkokin Mata da Kananan Yara, ta kuma bayyana bukatar kowa a cikin al’umma su kawo nasu gudummawar don ganin an kawo karshen shaye-shayen miyagun kwayoyi a Jihar Kano. Ga dai yadda tattaunawar ta Kasance:

Za muso jin wanda muke tare da ita a halin yanzu

Sunana Dakta Fauziyya Buba Idris mashawarciya ta musammana kan harkokin lafiya ga Gwamnan Jihar Kano Dakta Abdullahi Umar Ganduje, sannan kuma jagorar aiwatar da kudurin Mai Dakin Gwamna Farfesa Hafsat Ganduje na kaddamar da dakarun yaki da shaye-shaye Miyagun Kwayoyi a fadin kananan Hukumomin Jihar Kano 44

Labarai Masu Nasaba

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

Mene dalilin kokarin samar da dakarun Mata wadanda za su yi aiki wajen dakile matsalar shaye -shayen Miyagun Kwayoyi a tsakanin matasa?

Alhamdulillahi kullum Mai Dakin Gwamna damuwarta shi ne ta ga yara Mata da maza na kara tsunduma cikin wannan mummunar ta’ada, wannan ta sa ta yanke shawarar samar da dakarun Mata domin iyaye mata suke galabaita da wannan matsala domin su ake bari da dawainiya da yara a gida ko makarantu.  Saboda haka ta kirkiri wannan aiki wanda zuwa yanzu mun kusa kamala karade Kananan Hukumomin Jihar Kano 44 tare da kaddamar da wadannan da karu.

Mene ayyukan wadannan dakaru?

Aikinsu shi ne shiga cikin gidaje domin fadakar da iyaye Mata illar ta’ammali da Miyagun Kwayoyi, sannan kuma mace tafi kowa sanin matsalar ‘yar uwarta mace, wadannan dakaru na da karfin guiwar tunkarar kowacce uwa da aka hangi danta a ciki masu irin wannan matsala kuma a yi mata gargadi tare da wayar da kanta domin kara himma wajen Lura da mu’amalar yaranta sannan kuma an samar da tsare-tsare na fadakar da duk wanda yantsunci kansa a irin wannan matsala.

Mene kuke ganin na kara ta’azzara wannan matsala tashaye-shaye?

Daga ciki akwai matsalar rabuwar iyali, muna nan abokai, damuwa, talauci da sakacin Iyaye, wadannan na cikin abubuwan da ke kara rura wutar matsalar shaye-shayea tsakanin matasa. Sai Kuma rashin samun ingantaccen Ilimi da kulawar iyaye.

Dakta kasancewar ki Mace kuma likita sannan gashi kina zaman mashawarciya ga Gwamna kan Harkokin Lafiya, shin ko ya kike kallon matsalar da a halin ake fuskanta na shigar Mata har ma da matan aure cikin matsalar Shaye-shayen miyagun kwayoyi?

Gaskiya wannan lamari ne mai tada hankali, kuma shi Mai Dakin Gwamna Farfesa Hafsat Ganduje ta kalla kuma ta himmatu wajen neman hanyar magance matsalar, Alhamdulillahi Jihar Kano mun yi dacen Gwamna wanda kullum damuwarsa ita ce ya za a Inganta rayuwar al’umma, wannan tasa shi ne Gwamna daya tilo da ya fara zartar da dokar dole duk wani mai neman takara ko nadi a mukamin Gwamnati sai an gwada kwakwalwarsa, kuma yanzu kowa ya Fara ganin tasirin wannan kokari na Gwamna Ganduje.

Ana samun yawaitar kwararar masu tallace-tallacen maganunuwa a kan Tituna da kasuwanni, wanda a lokuta da dama suke yin amfani da wasu kalmomi da ba su dace da harshen Hausa da al’adun mu ba Kai har ma da addini, shin ko akwai wannan matsala?

Babu shakka tuni wannan Gwamnati tare da hadin kan Ma’aikatar Lafiya Gwamnati ta bijiro da wasu dokoki ga duk wanda ke bukatar tallan Maganin Gargajiya ko makamancinsa, sannan dole mutum ya je a tantance shi tare don yi masa rijista, sannana na shirya masu taron bita lokaci zuwa lokaci domin kara samun wayewa da kwarewa ta fuskar sana’arsu.

Wane kira za ki yi musamman ga matasa a lokaci irin wannan da aka fara kada kugen siyasa?

Daman tuni Gwamna ya ja kunnen Jama’a musamman ‘yan Jam’iyyar APC cewar kar wanda ya bari aka yi amfani da shi wajen tunzura matasa ko amfani da kayan maye ko makamai a lokacin yakin Neman Zabe, wannan tasa yanzu matasa a Kano an daina tunzura su aikata bangar siyasa.

Mun gode kwarai da gaske

Ni ma na gode


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: GandujekanoKungiyaMashawarciyaMata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kawancen Sin Da Afrika Na Da Muhimmanci Ga Cimma Ajandun Nahiyar Da Na Duniya

Next Post

Wurin Adana Kayan Tarihi Na Shaida Al’adun Kasa

Related

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Rahotonni

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

4 hours ago
Arewa
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Gwamnonin Arewa Sun Bullo Da Sabbin Matakan Yaki Da Ta’addanci

1 day ago
'Yan Bindiga
Rahotonni

Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Haifar Da Da Mai Ido A Katsina

3 days ago
Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
Rahotonni

Babban Taron Lauyoyi Na Kasa: Sarkin Musulmi Ya Gargadi Alkalai Kan Tabbatar Da Adalci

1 week ago
Sin Ta Fara Amfani Da Tauraron Dan Adam Wajen Duba Manyan Hanyoyin Wutar Lantarki A Karo Na Farko
Rahotonni

Cire Tallafin Wutar Lantarki Zai Kara Kuntata Rayuwar ‘Yan Nijeriya – Kungiyar Kwadago

1 week ago
Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu
Rahotonni

Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu

1 week ago
Next Post
Wurin Adana Kayan Tarihi Na Shaida Al’adun Kasa

Wurin Adana Kayan Tarihi Na Shaida Al’adun Kasa

LABARAI MASU NASABA

'yansanda

An Kama Mutane 30 Da Zargin Laifin Aikin Dabanci A Yayin Zagayen Maulidi A Neja

September 8, 2025
Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

Xi Jinping Ya Aika Da Sakon Taya Murnar Bude Taron Cifit Karo Na 25

September 8, 2025
Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

Gwamnatin Tarayya, NUPENG Da Ɗangote Sun Fara Tattaunawa Don Kawo Ƙarshen Yajin Aikin Ma’aikatan Mai

September 8, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

Sin Ta Gabatar Da Sabon Injin Aiki A Manyan Na’urori Mai Amfani Da Iskar Gas Kirar Gida

September 8, 2025
Mata

Jarin Da Sin Ta Zuba Kai Tsaye A Kasashe Cikin Shawarar Ziri Daya Da Hanya Daya Ya Karu Da Kashi 22.9% A 2024

September 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Abin Fargaba Ne Yadda Bashin Nijeriya Ya Haura Tiriliyan 149 – Shugaban Majalisar Wakilai 

September 8, 2025
Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

Adadin Kamfanonin AI A Sin Sun Haura 5,000

September 8, 2025
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Uba Sani Ya Buƙaci Al’ummar Jihar Kaduna Da Su Yi Rijistar Katin Zaɓe 

September 8, 2025
Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

Xi Ya Halarci Taron Kungiyar BRICS Ta Yanar Gizo

September 8, 2025
DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

DSS Ta Ba Sowore Mako Ɗaya Ya Janye Maganarsa Kan Tinubu

September 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.