• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban BUK Ta Karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim Da Walimar Kammala Digiri Na 3

byMuhammad
5 months ago
Ƙungiyar

Gamayyar Kungiyar Tsofaffin Ɗaliban Jami’ar Bayero waɗanda suka kammala karatu a shekarar 2015 a Sashen Koyar da Harsuanan Nijeriya da Sashen Kimiyyar Harshe da Harsunan Ƙasashen Waje na Jami’ar, sun karrama abokin karatunsu da ya zama zakara wajen zama mutum na farko a ajin su da ya kammala digiri na uku a ɓangaren Kimiyyar Harshe, Dr. Sani Dauda Ibrahim.Ƙungiyar

Taron an gabatar da shi ranar Asabar 10, ga Mayu 2025 a dakin cin abinci da shaƙatawa na Albaik Chicken da ke titin zuwa Gwarzo a jihar Kano. A yayin taron walimar, tsofaffin ɗaliban sun karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim a matsayin gwarzo kuma wanda ya yi fice ajin 2015 da wata shaidar girmamawa ta musanman kan nuna ƙwazo wajen zama mutum na farko da tarihin ɗaliban ba zai manta da shi ba.

  • Tsofaffin Ɗaliban BUK Sun Yaba Wa Masarautar Hausawan Turai Kan Naɗa Ma’ajin Hausawan Turai
  • Ɗaliban Jami’ar Bayero ‘Yan Ajin 2015 Sun Zamanantar Da Ɗakin Karatu Na M.A.Z Sani

A jawabin shugaban taron kuma Sakataren Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban, Muhammad Bashir Amin, ya godewa Allah bisa cikar burinsu na samun damar shirya walimar karrama abokin na su da ya yi fice a tsakaninsu tun lokacin da suke karatu tare da shi a matakin digirin farko a Jami’a, ya kuma yi fatan ci gaba da shirya makamancin irin wannan taruwa girmamawa ga mambobin ƙungiyar a fannonin rayuwa da dama, da fatan nasarar Dr. Sani Dauda Ibrahim ya samu ta amfani ilahirin ɗalibai da jami’ar da dukkan al’umma baki ɗaya, a jawabin nasa ya godewa shugaban Ƙungiyar Alhaji Hassan Baita Ubawaru (Ma’ajin Hausawan Turai) da ‘yan kwamitin shirya taron da sauran mambobin ƙungiyar kan irin haɗin kai da gudunmawar da suke bayarwa a koyaushe wajen ci gaban ƙungiyar.

Ƙungiyar
Mambobin Ƙungiyar Tsofaffin Ɗaliban Jami’ar Bayero lokacin da suke karrama Dr. Sani Dauda Ibrahim

A nasa jawabin, Dr. Sani Dauda Ibrahim, ya nuna farin cikinsa tare da godewa shugabancin ƙungiyar bisa karrama shi da suka yi wajen shirya liyafar ta ya shi murna da suka yi, ya ce nasarar ba ta shi ce kaɗai ba, ta kowa da kowa, saboda tabbas bai san wahalar karatu ba saboda Allah ya shiga cikin lamarinsa sosai tare kuma da addu’a iyaye da dafawar malamansa da abokan karatunsa, ya kuma bayyana cewa a nasa ɓangaren ya ci alwashin ci gaba da bayar da tasa gudunmawar wajen ci gaban ƙungiya tare da tabbatar da dorewar zumunci a tsakanin mambobin ƙungiyar.

Dr. Tijjani Shehu Almajir a lokacin da ya ke miƙa kyautar karrama wa ga Dr. Sani Dauda Ibrahim
Dr. Tijjani Shehu Almajir a lokacin da ya ke miƙa kyautar karrama wa ga Dr. Sani Dauda Ibrahim

Shugaban Sashen Kimiyyar Harshe na Jami’ar Bayero, Dr. Tijjani Shehu Almajir, wanda shi ne ya jagoranci duba aikin Dr. Sani Dauda Ibrahim, ya bayyana ƙwazo da hazaƙar da ɗalibin ya ke da ita a matsayin wani abu da suke alfahari da shi.

LABARAI MASU NASABA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

“Haƙiƙa muna alfahari da Dr. Sani Dauda Ibrahim da wannan ajin naku, musanman cewa akan ku na fara koyarwa a jami’a, kuma haɗin kan ‘yan wannan ajin ya zama na daban a cikin ƙungiyoyin tsofaffin ɗalibai, musanman saboda ayyuka da kuka gabatar na ci gaban ilimi a jami’ar Bayero da yadda kuke damuwar da al’amuran ilimi” cewar Dr. Almajir.

Taron ya samu halartar Dr. Maimuna Isma’il da ke koyarwa a sashen da sauran mambobin ƙungiya da ‘yan uwa da abokan arzikin Dr. Sani Dauda Ibrahim da aka karrama a wajen taron.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kolin Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Na Duniya Na Shekara Ta 2025 A Beijing

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version