• English
  • Business News
Thursday, October 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kungiyar Zauren Al’ummar Hausawa Ta Duniya Ta Nada Sarkin Zazzau Uban Kungiya

by Bello Hamza
3 years ago
Hausawa

A kwanakin baya ne kuniyar zauren al’ummar Hausawan Duniya, cikin bukuwan ranar Hausawan Duniya ta kai wa Mai Martaba Sarkin Zazzau, Ambasada Ahmad Nuhu Bamalli ziyara, tare da zabarsa a matsayin uban wannan kungiya.

Cikin jawabinsa na maraba, Mai martaba Sarkin Zazzau, Alhaji Ahmad Nuhu Bamalli ya nuna godiyarsa ga Allah ya ba da ikon kabar bakuncin wadannan baki nasa.

  • Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Keta Ka’idojin Fitar Da Kayayyaki
  • Wani Abun Fashewa Ya Tarwatse A Wani Masallaci Ya Kashe Akalla Mutane 18 A Afganistan

Mai Martaba Sarki ya ce, “muna mika matukar godiyar mu ga Allah da ya ba mu ikon ganin wannan rana cikin koshin lafiya har muka karbi bakuncin ku.

Muna godiya ga Allah da ya kawo ku lafiya, tate da fatan za ku koma lafiya.”

Haka kuma Sarkin ya nuna farin cikinsa da zabarsa da aka yi a matsayin Uba na wannan kungiya ta Zauren al’ummar Hausawan Duniya, “ba abin da za mu ce sai dai Allah saka maku da alhairi,” in ji Sarki.

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Ya ci gaba da bayyana cewa saboda muhimmancin wannan rana da kuma al’ummar Hausan Duniya, “ya zama wajibi a gare mu mu karbi wannan girma da aka dora mana.

Tare da fatan Allah zai mana ludufi ya ba mu ikon dauka,” In ji Sarkin na Zazzau.

Cikin zantawarsa da manema labarai jim kadan bayan kammala wannan ziyara, Shugaban zauren Hausa ta duniya, Ambasada Muhammad Kabir Gure ya bayyana cewa sun zabi kawo wannan ziyara a wannan rana ce domin muhimmancin ranar, wacce ya ce Majalisar Dinkin Duniya ta ware don Hausan duniya.

“Wannan muhimmiyar rana ce a gare mu, shi ne muka kawo wa Mai martaba Sarkin Zazzau ziyara domin ya sanya mana albarka.

Kuma a matsayinsa na Uba, ya sa mu ka zo neman albarka, wanda kuma a yanzu haka mun ba shi matsayin Uba na wannan kungiya,” in ji Ambasada.

Alhaji Sanusi ya kara da cewa a halin da ake ciki, Bahaushe bai isa ya tashi ya yi doguwar tafiya cikin kwanciyar hankali ba, “saboda haka sai muka ga ashe ke nan ba biki ya kamata mu yi ba, alhini za mu nuna, ai ranar bikinmu, ita ce ranar da ‘yan uwanmu suka fito daga daji,” in ji shi.

Ya ce, wannan ne ya sa suka zo wurin mai martaba Sarkin Zazzau domin jajanta wa juna, tare da yin kira ga gwamnati ta hanzarta karbo mutanenmu da ke dazuka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sabbin Ministoci
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku
Labarai

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC
Manyan Labarai

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Next Post
Na Samu Nutsuwa Bayan Karanta Al’ƙur’ani, In ji Baturiyar Da Ta Musulunta

Na Samu Nutsuwa Bayan Karanta Al'ƙur'ani, In ji Baturiyar Da Ta Musulunta

LABARAI MASU NASABA

Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Amince Da Amupitan A Matsayin Shugaban INEC

October 16, 2025
Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

Ɗaga Matsayin Dangantakar Zambia Da Sin Ya Haifar Da Manyan Nasarori

October 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Fursunoni Bayan Kammala Zaman Kurkuku

October 16, 2025
Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Amupitan Ya Isa Majalisar Dattawa Domin Tantance Shi A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Majalisar Dattawa Ta Fara Tantance Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 16, 2025
An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

An Dakatar Da Tashi Da Saukar Jirage A Kenya Don Karɓar Gawar Raila Odinga

October 16, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

Baba-Ahmed Ya Zargi El-Rufai Da APC Kan Haifar Da Rashin Tsaro Don Neman Mulki

October 16, 2025
Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

Jami’an FRSC Sun Mayar Da N6.2m Da Suka Tsinta Bayan Aukuwar Hatsarin Mota A Katsina

October 16, 2025
An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato

October 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.