• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kura-kuran Da Aka Tafka A Zaben Gwamna A Kogi, Imo Da Bayelsa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An samu kura-kurai masu dimbin yawa a lokacin gudanar da zaben gwamna a jihohin Kogi, Imo da Bayelsa a ranar 11 ga Nuwambar 2023.

Masu sa ido a zabukan sun bayyana yadda tashe-tashen hankula da sayan kuri’u da sauran nau’o’in magudi sunka turnike zabekan a dukkan jihohin guda uku.

  • Zaben Kogi: INEC Ta Musanta Zargin Sauya Kuri’un Da Ta Dora A Manhajar Tattara Sakamakon Zaɓe
  • San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne

Sai dai kuma hukumar yaki da cin hanci da rashawa da sauran hukumomin tsaro sun samu nasarar damke mutane da dama wadanda ake zargi da sayan kuri’u da kitsa tashe-tashen hankula a lokacin zabukan.

Haka kuma an samu tangardan na’uran wajen tantance masu zabe da kuma saka sakamakon zabe. Sannan a wasu rumfuna da dama ba a samu nasarar kai kayayyakin zabe da wuri ba, wanda yakan ya kawo tsaiko wajen fara zabukan kamayar yadda aka tsara.

A cikin rahoton kungiyoyin masu saka ido a zabuka, sun bayyana cewa ‘yan siyasa da dama sun karya dokokin zabe a jihohin Kogi, Imo da Bayelsa, wanda suka dunga sayan kuri’u da kuma haddasa tashe-tashen hankula domin su samu damar cimma burikansu na siyasa.

Labarai Masu Nasaba

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Shugabannin kungiyoyin karkashin jagorancin, Dakta Asmau Maikudi da Cynthia Mbamalu sun ce a ranar zabukan an samu tangardar na’ura wajen tantance masu zabe da kuma tura sakamakon zabe a kananan hukumomi masu yawa da ke jihohin guda uku.

A cewar rahoton masu saka idon, rumfuna da dama a zabukan an tantance mutane ne ba tare da na’ura ba kamar yadda dokar zabe ta tanada, wanda hakan ya kawo yin magudi da kuma karya dokokin zabe.

Sun dai yi kira da a gaggauta kame wadannan ‘yan siyasa da kuma jami’an hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), wadanda suka kada kai da ‘yan siyasan wajen yin magudi.

“Mun yi matukar damuwa yadda aka dunga tantance masu zabe ba tare da na’urar ba, wanda yakan ya hassasa hanyar yin masudi da sauran hanyoyin karya dokokin zabe a jihohin Kogi, Imo da kuma Bayelsa.”

Masu saka idon sun yi Allah wadai da yadda aka yi garkuwa da babban jami’in hukumar INEC a karamar hukumar Sagbama, inda suke kira da a gaggauta sako shi tare da cafke wadanda suka aikata mummunan aikin.

Rahoton masu saka idon ya bayyana cewa kashi 65 na rumfunan zabe a Bayelsa aka fara zabe da wuri, yayin aka samu kashi 80 a Jihar Imo, sabanin a Jihar Kogi da aka samu na kashi 40 wurin fara zabe a kan lokaci.

Rahoton ya ce an samu rashin fitowar masu jefa kuri’a a wasu rumfuna, inda a rumfa mai lamba ta daya da ke Orsu ta Jihar Imo, jami’an INEC sun fito tun da wuri, amma masu jefa kuri’a kalilan ne aka samu sun zo jefa kuri’a sakamakon fargabar tashin hankali.

A Jihar Bayelsa kuwa, rahoton masu saka idon ya bayyana cewa jami’an INEC da suka gudanar da zabe a rumfar ta 24 a Yenagoa, an fara zaben ne da misalin karfe 11: 37 na safe, yayin da a Oporoma da ke kudancin karamar hukumar Ijaw, jami’an INEC sun iso rumfar zaben ne da misalign karfe 12: 15, sannan a rumfa ta 10 da ke karamar hukumar Ogbia an fara zaben ne da misalin karfe 12: 40 na rana.

Haka kuma rahoton masu saka idon a Jihar Kogi ya bayyana cewa har zuwa karfe 10:54 ba a fara zabe a rumfunan zabe da ke Iluteju, Okesi, Okibo, Eni, Oshobeni da Aiyeronmi a karamar hukumar Ogori-Magongo.

A Jihar Imo ma an samu jami’an INEC da zuwa latti a mafi yawancin runfunan zabe da suka hada da Abu/Oforola, Ehime Mbano, Mbaitoli-Ezinihitie, Umuokpiriri, Umuogu, Arewacin Owerri da kuma Isiala Mbano. Rahoton ya ce sai da misalin karfe 10: 23 na safe ne aka fara gudanar da zabe a rumfunan zabe a

Ihitteoha da wasu rumfunan zabe da ke karamar hukumar Owerri ta Arewa.

Rahoton ya ce a dukkan jihohin guda uku an samu rahoton sayan kuri’a daga kan naira 5,000 zuwa 22,000 ga kowani mai kada kuri’a.

Sannan rahotanni sun bayyana cewa an samu satar akwatin zabe tare da farmakar jami’an INEC a lokacin gudanar da wannan zabuka.

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa (EFCC) ta bayyana cewa ta samu nasarar damke mutum 14 da ake zargi da sayan kuri’u a zaben gwamna a jihohin Kogi da Imo da kuma Bayelsa.

Mai magana da yawun hukumar EFCC, Dele Oyewale shi ya bayyana hakan a lokacin tattaunawa da manema labarai kan zabukan gwamna a jihohin uku.

Ya ce an samu nasarar kwato jamillar kudade da suka kai naira 11,040, 000 da 9,310,00 da kuma 1,730,000 daga hannun masu sayan kuri’a a dukkan jihohin guda uku.

Hukumar EFCC ta ce za ta gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu da zarar ta kammala bincike.

Jam’iyyar APC ce ta samu nasarar lashe zabe a jihohin Kogi da Imo, yayin da jam’iyyar PDP ta lashe zabe a Jihar Bayelsa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BayelsaDino MelayeImoINECKogi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wannan Kyauta Ce Ta Musamman Daga Daliban Makarantar Sakandaren Amurka

Next Post

Za A Samar Wa ‘Yan Nijeriya Gida 80,000 Cikin Shekara 4

Related

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

5 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

5 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

8 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

8 hours ago
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega
Labarai

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

11 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

12 hours ago
Next Post
nijeriya

Za A Samar Wa ‘Yan Nijeriya Gida 80,000 Cikin Shekara 4

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.