ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, June 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kura-kuran Da Aka Tafka A Zaben Gwamna A Kogi, Imo Da Bayelsa

by Yusuf Shuaibu
3 years ago

An samu kura-kurai masu dimbin yawa a lokacin gudanar da zaben gwamna a jihohin Kogi, Imo da Bayelsa a ranar 11 ga Nuwambar 2023.

Masu sa ido a zabukan sun bayyana yadda tashe-tashen hankula da sayan kuri’u da sauran nau’o’in magudi sunka turnike zabekan a dukkan jihohin guda uku.

  • Zaben Kogi: INEC Ta Musanta Zargin Sauya Kuri’un Da Ta Dora A Manhajar Tattara Sakamakon Zaɓe
  • San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne

Sai dai kuma hukumar yaki da cin hanci da rashawa da sauran hukumomin tsaro sun samu nasarar damke mutane da dama wadanda ake zargi da sayan kuri’u da kitsa tashe-tashen hankula a lokacin zabukan.

ADVERTISEMENT

Haka kuma an samu tangardan na’uran wajen tantance masu zabe da kuma saka sakamakon zabe. Sannan a wasu rumfuna da dama ba a samu nasarar kai kayayyakin zabe da wuri ba, wanda yakan ya kawo tsaiko wajen fara zabukan kamayar yadda aka tsara.

A cikin rahoton kungiyoyin masu saka ido a zabuka, sun bayyana cewa ‘yan siyasa da dama sun karya dokokin zabe a jihohin Kogi, Imo da Bayelsa, wanda suka dunga sayan kuri’u da kuma haddasa tashe-tashen hankula domin su samu damar cimma burikansu na siyasa.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

Shugabannin kungiyoyin karkashin jagorancin, Dakta Asmau Maikudi da Cynthia Mbamalu sun ce a ranar zabukan an samu tangardar na’ura wajen tantance masu zabe da kuma tura sakamakon zabe a kananan hukumomi masu yawa da ke jihohin guda uku.

A cewar rahoton masu saka idon, rumfuna da dama a zabukan an tantance mutane ne ba tare da na’ura ba kamar yadda dokar zabe ta tanada, wanda hakan ya kawo yin magudi da kuma karya dokokin zabe.

Sun dai yi kira da a gaggauta kame wadannan ‘yan siyasa da kuma jami’an hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), wadanda suka kada kai da ‘yan siyasan wajen yin magudi.

“Mun yi matukar damuwa yadda aka dunga tantance masu zabe ba tare da na’urar ba, wanda yakan ya hassasa hanyar yin masudi da sauran hanyoyin karya dokokin zabe a jihohin Kogi, Imo da kuma Bayelsa.”

Masu saka idon sun yi Allah wadai da yadda aka yi garkuwa da babban jami’in hukumar INEC a karamar hukumar Sagbama, inda suke kira da a gaggauta sako shi tare da cafke wadanda suka aikata mummunan aikin.

Rahoton masu saka idon ya bayyana cewa kashi 65 na rumfunan zabe a Bayelsa aka fara zabe da wuri, yayin aka samu kashi 80 a Jihar Imo, sabanin a Jihar Kogi da aka samu na kashi 40 wurin fara zabe a kan lokaci.

Rahoton ya ce an samu rashin fitowar masu jefa kuri’a a wasu rumfuna, inda a rumfa mai lamba ta daya da ke Orsu ta Jihar Imo, jami’an INEC sun fito tun da wuri, amma masu jefa kuri’a kalilan ne aka samu sun zo jefa kuri’a sakamakon fargabar tashin hankali.

A Jihar Bayelsa kuwa, rahoton masu saka idon ya bayyana cewa jami’an INEC da suka gudanar da zabe a rumfar ta 24 a Yenagoa, an fara zaben ne da misalin karfe 11: 37 na safe, yayin da a Oporoma da ke kudancin karamar hukumar Ijaw, jami’an INEC sun iso rumfar zaben ne da misalign karfe 12: 15, sannan a rumfa ta 10 da ke karamar hukumar Ogbia an fara zaben ne da misalin karfe 12: 40 na rana.

Haka kuma rahoton masu saka idon a Jihar Kogi ya bayyana cewa har zuwa karfe 10:54 ba a fara zabe a rumfunan zabe da ke Iluteju, Okesi, Okibo, Eni, Oshobeni da Aiyeronmi a karamar hukumar Ogori-Magongo.

A Jihar Imo ma an samu jami’an INEC da zuwa latti a mafi yawancin runfunan zabe da suka hada da Abu/Oforola, Ehime Mbano, Mbaitoli-Ezinihitie, Umuokpiriri, Umuogu, Arewacin Owerri da kuma Isiala Mbano. Rahoton ya ce sai da misalin karfe 10: 23 na safe ne aka fara gudanar da zabe a rumfunan zabe a

Ihitteoha da wasu rumfunan zabe da ke karamar hukumar Owerri ta Arewa.

Rahoton ya ce a dukkan jihohin guda uku an samu rahoton sayan kuri’a daga kan naira 5,000 zuwa 22,000 ga kowani mai kada kuri’a.

Sannan rahotanni sun bayyana cewa an samu satar akwatin zabe tare da farmakar jami’an INEC a lokacin gudanar da wannan zabuka.

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa (EFCC) ta bayyana cewa ta samu nasarar damke mutum 14 da ake zargi da sayan kuri’u a zaben gwamna a jihohin Kogi da Imo da kuma Bayelsa.

Mai magana da yawun hukumar EFCC, Dele Oyewale shi ya bayyana hakan a lokacin tattaunawa da manema labarai kan zabukan gwamna a jihohin uku.

Ya ce an samu nasarar kwato jamillar kudade da suka kai naira 11,040, 000 da 9,310,00 da kuma 1,730,000 daga hannun masu sayan kuri’a a dukkan jihohin guda uku.

Hukumar EFCC ta ce za ta gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu da zarar ta kammala bincike.

Jam’iyyar APC ce ta samu nasarar lashe zabe a jihohin Kogi da Imo, yayin da jam’iyyar PDP ta lashe zabe a Jihar Bayelsa.

kogi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4
Manyan Labarai

Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

June 15, 2026
ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027
Manyan Labarai

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

June 15, 2026
Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato
Manyan Labarai

Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

June 15, 2026
Next Post
nijeriya

Za A Samar Wa ‘Yan Nijeriya Gida 80,000 Cikin Shekara 4

LABARAI MASU NASABA

Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya

Tunisiyya Ta Sallami Kocinta Bayan Shan Kashi 5-1 A Wasan Farko Na Kofin Duniya

June 15, 2026
Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

Kotu Ta Umarci INEC Ta Soke Rajistar ADC Da Wasu Jam’iyyu 4

June 15, 2026
ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

ADC Ta Zaɓi Amaechi A Matsayin Mataimakin Atiku A Zaɓen 2027

June 15, 2026
Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

Xi Jinping: Zan Sadaukar Da Rayuwata Don Bautawa Jama’a

June 15, 2026
Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

Annobar Ƙwalara Ta Kashe Mutane Biyar, 11 Sun Kamu A Filato

June 15, 2026
Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

Farashin Mai Ya Fadi Rigis Bayan Amurka Da Iran Sun Sasanta Kan Mashigar Hormuz

June 15, 2026
An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

An Daure Ɗan Gidan Gimbiyar Masarautar Norway Shekara 4 Kan Laifin Fyaɗe

June 15, 2026
An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

An Yi Wa Mata 600 Gwajin Cutar Sankarar Mama, An Yi Wa 50 Tiyata A Katsina

June 15, 2026
Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

Ƴansanda Sun Kashe Ƴan Bindiga Uku Yayin Zazzafar Musayar Wuta

June 15, 2026
Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

Jamus Ta Sake Yi Wa Abokiyar Karawarta Ruwan Ƙwallaye 7 A Gasar Kofin Duniya

June 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.