ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kura-kuran Da Aka Tafka A Zaben Gwamna A Kogi, Imo Da Bayelsa

by Yusuf Shuaibu
3 years ago

An samu kura-kurai masu dimbin yawa a lokacin gudanar da zaben gwamna a jihohin Kogi, Imo da Bayelsa a ranar 11 ga Nuwambar 2023.

Masu sa ido a zabukan sun bayyana yadda tashe-tashen hankula da sayan kuri’u da sauran nau’o’in magudi sunka turnike zabekan a dukkan jihohin guda uku.

  • Zaben Kogi: INEC Ta Musanta Zargin Sauya Kuri’un Da Ta Dora A Manhajar Tattara Sakamakon Zaɓe
  • San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne

Sai dai kuma hukumar yaki da cin hanci da rashawa da sauran hukumomin tsaro sun samu nasarar damke mutane da dama wadanda ake zargi da sayan kuri’u da kitsa tashe-tashen hankula a lokacin zabukan.

ADVERTISEMENT

Haka kuma an samu tangardan na’uran wajen tantance masu zabe da kuma saka sakamakon zabe. Sannan a wasu rumfuna da dama ba a samu nasarar kai kayayyakin zabe da wuri ba, wanda yakan ya kawo tsaiko wajen fara zabukan kamayar yadda aka tsara.

A cikin rahoton kungiyoyin masu saka ido a zabuka, sun bayyana cewa ‘yan siyasa da dama sun karya dokokin zabe a jihohin Kogi, Imo da Bayelsa, wanda suka dunga sayan kuri’u da kuma haddasa tashe-tashen hankula domin su samu damar cimma burikansu na siyasa.

LABARAI MASU NASABA

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

Shugabannin kungiyoyin karkashin jagorancin, Dakta Asmau Maikudi da Cynthia Mbamalu sun ce a ranar zabukan an samu tangardar na’ura wajen tantance masu zabe da kuma tura sakamakon zabe a kananan hukumomi masu yawa da ke jihohin guda uku.

A cewar rahoton masu saka idon, rumfuna da dama a zabukan an tantance mutane ne ba tare da na’ura ba kamar yadda dokar zabe ta tanada, wanda hakan ya kawo yin magudi da kuma karya dokokin zabe.

Sun dai yi kira da a gaggauta kame wadannan ‘yan siyasa da kuma jami’an hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), wadanda suka kada kai da ‘yan siyasan wajen yin magudi.

“Mun yi matukar damuwa yadda aka dunga tantance masu zabe ba tare da na’urar ba, wanda yakan ya hassasa hanyar yin masudi da sauran hanyoyin karya dokokin zabe a jihohin Kogi, Imo da kuma Bayelsa.”

Masu saka idon sun yi Allah wadai da yadda aka yi garkuwa da babban jami’in hukumar INEC a karamar hukumar Sagbama, inda suke kira da a gaggauta sako shi tare da cafke wadanda suka aikata mummunan aikin.

Rahoton masu saka idon ya bayyana cewa kashi 65 na rumfunan zabe a Bayelsa aka fara zabe da wuri, yayin aka samu kashi 80 a Jihar Imo, sabanin a Jihar Kogi da aka samu na kashi 40 wurin fara zabe a kan lokaci.

Rahoton ya ce an samu rashin fitowar masu jefa kuri’a a wasu rumfuna, inda a rumfa mai lamba ta daya da ke Orsu ta Jihar Imo, jami’an INEC sun fito tun da wuri, amma masu jefa kuri’a kalilan ne aka samu sun zo jefa kuri’a sakamakon fargabar tashin hankali.

A Jihar Bayelsa kuwa, rahoton masu saka idon ya bayyana cewa jami’an INEC da suka gudanar da zabe a rumfar ta 24 a Yenagoa, an fara zaben ne da misalin karfe 11: 37 na safe, yayin da a Oporoma da ke kudancin karamar hukumar Ijaw, jami’an INEC sun iso rumfar zaben ne da misalign karfe 12: 15, sannan a rumfa ta 10 da ke karamar hukumar Ogbia an fara zaben ne da misalin karfe 12: 40 na rana.

Haka kuma rahoton masu saka idon a Jihar Kogi ya bayyana cewa har zuwa karfe 10:54 ba a fara zabe a rumfunan zabe da ke Iluteju, Okesi, Okibo, Eni, Oshobeni da Aiyeronmi a karamar hukumar Ogori-Magongo.

A Jihar Imo ma an samu jami’an INEC da zuwa latti a mafi yawancin runfunan zabe da suka hada da Abu/Oforola, Ehime Mbano, Mbaitoli-Ezinihitie, Umuokpiriri, Umuogu, Arewacin Owerri da kuma Isiala Mbano. Rahoton ya ce sai da misalin karfe 10: 23 na safe ne aka fara gudanar da zabe a rumfunan zabe a

Ihitteoha da wasu rumfunan zabe da ke karamar hukumar Owerri ta Arewa.

Rahoton ya ce a dukkan jihohin guda uku an samu rahoton sayan kuri’a daga kan naira 5,000 zuwa 22,000 ga kowani mai kada kuri’a.

Sannan rahotanni sun bayyana cewa an samu satar akwatin zabe tare da farmakar jami’an INEC a lokacin gudanar da wannan zabuka.

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa (EFCC) ta bayyana cewa ta samu nasarar damke mutum 14 da ake zargi da sayan kuri’u a zaben gwamna a jihohin Kogi da Imo da kuma Bayelsa.

Mai magana da yawun hukumar EFCC, Dele Oyewale shi ya bayyana hakan a lokacin tattaunawa da manema labarai kan zabukan gwamna a jihohin uku.

Ya ce an samu nasarar kwato jamillar kudade da suka kai naira 11,040, 000 da 9,310,00 da kuma 1,730,000 daga hannun masu sayan kuri’a a dukkan jihohin guda uku.

Hukumar EFCC ta ce za ta gurfanar da wadanda ake zargin a gaban kotu da zarar ta kammala bincike.

Jam’iyyar APC ce ta samu nasarar lashe zabe a jihohin Kogi da Imo, yayin da jam’iyyar PDP ta lashe zabe a Jihar Bayelsa.

kogi
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Rahotonni

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara
Labarai

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Next Post
nijeriya

Za A Samar Wa ‘Yan Nijeriya Gida 80,000 Cikin Shekara 4

LABARAI MASU NASABA

Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.