• English
  • Business News
Friday, July 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamishinan ‘Yansandan Kano Ya Nemi Taimakon Sarakunan Gargajiya Wajen Kawo Ƙarshen Faɗan Daba

by Sadiq
3 months ago
in Manyan Labarai
0
Kwamishinan ‘Yansandan Kano Ya Nemi Taimakon Sarakunan Gargajiya Wajen Kawo Ƙarshen Faɗan Daba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamishinan ‘Yan Sanda.’n Jihar Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ya roƙi sarakunan gargajiya musamman masu unguwanni da su taimaka wajen yaƙi da faɗan daba da sauran miyagun laifuka a tsakanin al’umma.

Ya yi wannan kira ne a taron masu ruwa da tsaki da aka shirya a filin wasa na Sani Abacha, wanda kwamitin daƙile matsalolin tsaro na jihar ya shirya.

  • Yaƙin Neman Zaɓe A 2027: Ƙungiya Ta Nemi A Maye Gurbin Mai Magana Da Yawun Shugaban Ƙasa
  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Yi Watsi Da Matsawa Sauran Kasashe Lamba

CP Bakori, ya ce sarakunan gargajiya suna da muhimmanci matuƙa wajen taimaka wa ‘yansanda gano matsalolin tsaro a unguwanni da kuma magance su.

Ya buƙaci su riƙa haɗa kai da jami’an ‘yansanda na yankinsu domin magance duk wata matsala tun kafin ta zama babba.

Kwamishinan ya bayyana cewa kafa kwamitin ya taimaka sosai wajen haɗin gwiwar hukumomin tsaro, wanda hakan ya ba su damar yin aiki tare da samun nasarori.

Labarai Masu Nasaba

Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

Ya ce sama da mutane 150 ne aka kama da laifin faɗan ɗaba da tashin hankali, tare da ƙwato makamai, miyagun ƙwayoyi da kayan sata.

Ya ƙara da cewa matsalolin faɗan ɗaba da shaye-shaye barazana ce ga zaman lafiyar jama’a da makomar matasa.

Duk da yake kame na da muhimmanci, Bakori ya ce dole ne a bai wa matasa damar samun ilimi, koyon sana’o’i da kuma wasu ayyuka da za su riƙa shagaltar da su zuwa hanya mafi dacewa.

Ya kuma shawarci shugabannin ‘yansanda na ƙananan hukumomi da su riƙa haɗa kai da sarakunan gargajiya da al’ummar yankinsu wajen gano matsalolin tsaro a yankunansu.

“Idan muka haɗa kai da goyon bayan jama’a, babu yadda ‘yan daba za su ci gaba da addabar Kano,” in ji CP Bakori.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: 'YansandaFaɗan DabakanoKwamishina
ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Ta Gurfanar Da Ɗan China A Kotu Kan Bayar Da Bayanan Ƙarya

Next Post

Gwamnatin Kano Za Ta Sake Buɗe Makarantun Kwana 10 Don Inganta Ilimin Yara Mata

Related

Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu
Manyan Labarai

Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

9 hours ago
Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ
Tsaro

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

12 hours ago
Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ƙi Karɓar Cin Hancin Miliyan 13 Daga Ƴan Ta’adda A Filato

14 hours ago
Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC
Manyan Labarai

Dele Momodu Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP Zuwa ADC

18 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Fara Yaƙi Da Masu Damfara A Intanet

21 hours ago
Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila
Manyan Labarai

Buhari Ya Taimake Ni Lokacin Da Wasu Ke Ƙoƙarin Ruguza Majalisar Tarayya — Gbajabiamila

23 hours ago
Next Post
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamnatin Kano Za Ta Sake Buɗe Makarantun Kwana 10 Don Inganta Ilimin Yara Mata

LABARAI MASU NASABA

Raya Hulda Tsakanin Sin Da Australia Ya Dace Da Yanayin Zamanin Da Ake Ciki

Raya Hulda Tsakanin Sin Da Australia Ya Dace Da Yanayin Zamanin Da Ake Ciki

July 17, 2025
Shugaba Tinubu Zai Ziyarci Kano Don Ta’aziyyar Ɗantata

Shugaba Tinubu Zai Ziyarci Kano Don Ta’aziyyar Ɗantata

July 17, 2025
Gudummawar Sin Ga Tattaunawa Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai Da Dunkulewar Duniya

Gudummawar Sin Ga Tattaunawa Tsakanin Mabanbantan Wayewar Kai Da Dunkulewar Duniya

July 17, 2025
Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

Natasha Ta Rubuta Wa Majalisa, Tana Neman A Yi Biyayya Ga Umarnin Kotu

July 17, 2025
Binciken Jin Ra’ayoyin Jama’a Na CGTN: Rahoton Matsayar Japan Kan Tsaro Na Takala Na Nuna Hatsari Mai Girma Game Da Tsaro

Binciken Jin Ra’ayoyin Jama’a Na CGTN: Rahoton Matsayar Japan Kan Tsaro Na Takala Na Nuna Hatsari Mai Girma Game Da Tsaro

July 17, 2025
Direban Da Ya Murƙushe Furen Gwamnati A Kano Ya Shiga Hannu

Direban Da Ya Murƙushe Furen Gwamnati A Kano Ya Shiga Hannu

July 17, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Mai Fafutukar Inganta Ci Gaban Duniya A Koyaushe

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Mai Fafutukar Inganta Ci Gaban Duniya A Koyaushe

July 17, 2025
Sojoji Sun Kama Jami’an NURTW 2, Da Mai Karɓar Harajin IPOB

Sojoji Sun Kama Jami’an NURTW 2, Da Mai Karɓar Harajin IPOB

July 17, 2025
Roy Jakobs: Ba Za A Iya Rabuwa Da Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Sin Ba

Roy Jakobs: Ba Za A Iya Rabuwa Da Tsarin Samar Da Kayayyaki Na Sin Ba

July 17, 2025
Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

Babu Wata Sabuwar Ƙungiyar  Ƴan Ta’adda Mai Suna Fethulla A Nijeriya – DHQ

July 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.