• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamitin Majalisa Ya Himmatu Wajen Kammala Hanyar Abuja- Kaduna Zuwa Kano

bySharfaddeen Sidi Umar, Sokoto
2 years ago
Abuja

Kwamitin Majalisar Wakilai na wucin- gadi kan binciken dalilin tsaikon da aka samu wajen kammala tagwayen hanyar mota kilomita 375 daga Abuja- Kaduna- Kano ya fara gudanar da aikinsa tare da alwashin ganin an kammala aikin cikin lokaci.

Shugaban kwamitin na wucin-gadi, Hon. Abdussamad Dasuki ya bayyana cewar ko kadan ba su da manufar bita- da- kulli ga kowa a binciken illa domin shawo kan kalubalen da ke akwai na tsaikon kammala hanyar wadda Gwamnatin Tarayya ta sake bayar da kwangilar shimfidawa a 2020.

  • Gwamnatin Kaduna Za Ta Yi Bincike Kan Ruftawar Masallacin Fadar Zazzau
  • Majalisar Dokokin Kaduna Ta Amince Da Kwamishinoni 13

Hon. Dasuki wanda ya jagoranci manbobin kwamitin a ziyarar gani da ido a babbar muhimmiyar hanyar, ya kuma bayyana cewar binciken na da manufar ganin an aiwatar da dukkanin sharuda da ka’idojin da aka shata a kwangilar.

LEADERSHIP Hausa ta labarto cewar a yayin rangadin, kwamitin karara ya nuna rashin gamsuwa kan yadda akin ke tafiya da nuna damuwa kan yiyuwar kammala aikin a sabon wa’adin 2025 da Ma’aikatar Ayyuka ta ayyana.

Tun da farko, kwamitin ya gayyaci kamfanin Julius Berger da ke aiwatar da kwangilar da jami’an Ma’aikatar Ayyuka domin jin ta bakin su kan dalilin da yasa duk da makuddan kudaden da aka fitar kan aikin, amma aikin yana nesa ga wa’adin kammalawa. Jami’in kamfanin ya bayyana cewar aikin ya samu tsaiko ne a dalilin rashin tsaro da ke akwai a hanyar.

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

A zaman tattaunawa da jami’an Ma’aikatar Ayyuka da kwamitin ya gudanar a karkashin jagorancin Hon. Dasuki, Babbar Sakataren Ma’aikatar, Mamuda Mamman ya bayyanawa kwamitin cewar an kusa kammala aikin sashe na 2 da na 3 na hanyar.

Ya bayyana cewar aikin hanyar a sashen Abuja- Kaduna ya fuskanci matsalar aiwatarwa ta kudi da matsalolin tsaro. Ya ce kusan kashi 20% ne a ka kammala a sashe na 1 daga Abuja zuwa Kaduna, amma ya baiwa kwamitin tabbacin kammala aikin a Mayu 2025.

A yanzu haka dai Kwamitin dai na wucin-gadi yana ci-gaba da aiwatar da aikinsa tare da tsammanin kai rahoto ga Majalisar Wakilai a cikin wa’adin makwanni hudu da majalisa ta baiwa kwamitin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Duniya Ba Ta Bukatar Wani Sabon “Yakin Mummuke”

Duniya Ba Ta Bukatar Wani Sabon “Yakin Mummuke”

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version