• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamoti B Laori Ya Kaddamar Da Ajujuwa 3 A Mazabar Kodomti A Numan

by Muh'd Shafi'u Saleh
1 year ago
in Labarai
0
Kwamoti B Laori Ya Kaddamar Da Ajujuwa 3 A Mazabar Kodomti A Numan
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kokarin da yake yi na inganta harkar ilmi da ababen more rayuwa a mazabarsa, dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Demsa/Numan/Lamurde a majalisar tarayya ya kaddamar da rukunin ajujuwa 3 a unguwar Kodomti da ke karamar hukumar Numan.

Da yake jawabi a ranar Laraba a wajen taron, dan majalisar ya koka kan matsalar karancin ababen more rayuwa a mafi yawan al’ummar mazabar, inda ya jaddada kudirinsa na ganin an inganta ilimi a lokacin mulkinsa.

  • Kotu Ta Raba Auren Shekaru 7 Saboda Rashin Soyayya
  • Wata Mata Ta Sace Jariri Sabuwar Haihuwa A Asibiti A Nasarawa

Dan majalisar ya bayyana cewa ingantaccen yanayin koyon karatu yana da muhimmanci ga rayuwar yara, don gudanar da ingantaccen koyo.

Bayan bayar da tallafin karatu ga dalibai a matakai daban-daban na ilimi, ya jaddada cewa tare da ilimi ya zo da ‘yanci, tare da yin alkawarin kara tsoma baki a fannin.

Kwamoti

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Dan majalisar ya yi amfani da wannan damar wajen nuna godiya ga irin goyon bayan da ya samu daga jama’ar mazabarsa tare da yin alkawarin ba zai taba bata ba su kunya ba.

Al’ummar mazabar Kodomti karkashin jagorancin su Ndewodi Kodomti da Ha Shaforon, sun cika da farin cikin bisa kaddamar da ginin ajujuwa.

Kwamoti

Jama’a da dama sun fito don nuna godiya ga dan majalisar, sun yi addu’ar Allah ya taimaki dan majalisar ya samu nasara a duk kokarin da yake aikin inganta rayuwar al’ummar mazabarsa.

Al’ummar Kodomti ta yi fice wajen noma da kamun kifi, sun gabatar da kyautar kifi katann guda ga dan majalisar, a matsayin alamar kauna da godiya.

Abubuwan da suka fi daukar hankali a taron sun hada da gabatar da al’adu da al’ummar Kodomti da Bandawa suka nuna.

Kwamoti

A nasu bangaren, daliban makarantar firamare ta Kodomti sun gabatar da jawabai da dama cikin wakoki da kasidu domin nuna godiya ga dan majalisar tarayyar.

Cikin manyan bakin da suka halarci bikin sun hada da Ndewodi Kodomti, Ha Shaforon, Hon. Pwamwakaino Makondo, shugabannin kananan hukumomin Numan da Lamurde.

Shugabannin jam’iyyarsa da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP a Numan, Demsa Lamurde duk sun halarci taro.

Kwamoti

Haka kuma dan majalisa Kwamoti B La’ori, ya ziyarci kasuwar Numan, domin jajanta wa ‘yan kasuwar da iftila’in gobara ya kone musu shaguna kurmus.

Ya yi fatan Allah ya tsayar da lamarin haka, sannan ya yi alkawarin tallafa musu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AjujuwaDan MajalisaIlimiNuman
ShareTweetSendShare
Previous Post

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Satar Jariri A Nasarawa

Next Post

Sin Na Fatan Taimakawa Ghana Kan Matsalar Basusukan Da Ake Bin Ta

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

3 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

5 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

6 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

6 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

8 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

10 hours ago
Next Post
Sin Na Fatan Taimakawa Ghana Kan Matsalar Basusukan Da Ake Bin Ta

Sin Na Fatan Taimakawa Ghana Kan Matsalar Basusukan Da Ake Bin Ta

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.