• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamoti B Laori Ya Kaddamar Da Ajujuwa 3 A Mazabar Kodomti A Numan

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Kwamoti

A kokarin da yake yi na inganta harkar ilmi da ababen more rayuwa a mazabarsa, dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Demsa/Numan/Lamurde a majalisar tarayya ya kaddamar da rukunin ajujuwa 3 a unguwar Kodomti da ke karamar hukumar Numan.

Da yake jawabi a ranar Laraba a wajen taron, dan majalisar ya koka kan matsalar karancin ababen more rayuwa a mafi yawan al’ummar mazabar, inda ya jaddada kudirinsa na ganin an inganta ilimi a lokacin mulkinsa.

  • Kotu Ta Raba Auren Shekaru 7 Saboda Rashin Soyayya
  • Wata Mata Ta Sace Jariri Sabuwar Haihuwa A Asibiti A Nasarawa

Dan majalisar ya bayyana cewa ingantaccen yanayin koyon karatu yana da muhimmanci ga rayuwar yara, don gudanar da ingantaccen koyo.

Bayan bayar da tallafin karatu ga dalibai a matakai daban-daban na ilimi, ya jaddada cewa tare da ilimi ya zo da ‘yanci, tare da yin alkawarin kara tsoma baki a fannin.

Kwamoti

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

Dan majalisar ya yi amfani da wannan damar wajen nuna godiya ga irin goyon bayan da ya samu daga jama’ar mazabarsa tare da yin alkawarin ba zai taba bata ba su kunya ba.

Al’ummar mazabar Kodomti karkashin jagorancin su Ndewodi Kodomti da Ha Shaforon, sun cika da farin cikin bisa kaddamar da ginin ajujuwa.

Kwamoti

Jama’a da dama sun fito don nuna godiya ga dan majalisar, sun yi addu’ar Allah ya taimaki dan majalisar ya samu nasara a duk kokarin da yake aikin inganta rayuwar al’ummar mazabarsa.

Al’ummar Kodomti ta yi fice wajen noma da kamun kifi, sun gabatar da kyautar kifi katann guda ga dan majalisar, a matsayin alamar kauna da godiya.

Abubuwan da suka fi daukar hankali a taron sun hada da gabatar da al’adu da al’ummar Kodomti da Bandawa suka nuna.

Kwamoti

A nasu bangaren, daliban makarantar firamare ta Kodomti sun gabatar da jawabai da dama cikin wakoki da kasidu domin nuna godiya ga dan majalisar tarayyar.

Cikin manyan bakin da suka halarci bikin sun hada da Ndewodi Kodomti, Ha Shaforon, Hon. Pwamwakaino Makondo, shugabannin kananan hukumomin Numan da Lamurde.

Shugabannin jam’iyyarsa da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP a Numan, Demsa Lamurde duk sun halarci taro.

Kwamoti

Haka kuma dan majalisa Kwamoti B La’ori, ya ziyarci kasuwar Numan, domin jajanta wa ‘yan kasuwar da iftila’in gobara ya kone musu shaguna kurmus.

Ya yi fatan Allah ya tsayar da lamarin haka, sannan ya yi alkawarin tallafa musu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma
Labarai

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
tinubu
Labarai

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Next Post
Sin Na Fatan Taimakawa Ghana Kan Matsalar Basusukan Da Ake Bin Ta

Sin Na Fatan Taimakawa Ghana Kan Matsalar Basusukan Da Ake Bin Ta

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.