ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamoti B Laori Ya Kaddamar Da Ajujuwa 3 A Mazabar Kodomti A Numan

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Kwamoti

A kokarin da yake yi na inganta harkar ilmi da ababen more rayuwa a mazabarsa, dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Demsa/Numan/Lamurde a majalisar tarayya ya kaddamar da rukunin ajujuwa 3 a unguwar Kodomti da ke karamar hukumar Numan.

Da yake jawabi a ranar Laraba a wajen taron, dan majalisar ya koka kan matsalar karancin ababen more rayuwa a mafi yawan al’ummar mazabar, inda ya jaddada kudirinsa na ganin an inganta ilimi a lokacin mulkinsa.

  • Kotu Ta Raba Auren Shekaru 7 Saboda Rashin Soyayya
  • Wata Mata Ta Sace Jariri Sabuwar Haihuwa A Asibiti A Nasarawa

Dan majalisar ya bayyana cewa ingantaccen yanayin koyon karatu yana da muhimmanci ga rayuwar yara, don gudanar da ingantaccen koyo.

ADVERTISEMENT

Bayan bayar da tallafin karatu ga dalibai a matakai daban-daban na ilimi, ya jaddada cewa tare da ilimi ya zo da ‘yanci, tare da yin alkawarin kara tsoma baki a fannin.

Kwamoti

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dan majalisar ya yi amfani da wannan damar wajen nuna godiya ga irin goyon bayan da ya samu daga jama’ar mazabarsa tare da yin alkawarin ba zai taba bata ba su kunya ba.

Al’ummar mazabar Kodomti karkashin jagorancin su Ndewodi Kodomti da Ha Shaforon, sun cika da farin cikin bisa kaddamar da ginin ajujuwa.

Kwamoti

Jama’a da dama sun fito don nuna godiya ga dan majalisar, sun yi addu’ar Allah ya taimaki dan majalisar ya samu nasara a duk kokarin da yake aikin inganta rayuwar al’ummar mazabarsa.

Al’ummar Kodomti ta yi fice wajen noma da kamun kifi, sun gabatar da kyautar kifi katann guda ga dan majalisar, a matsayin alamar kauna da godiya.

Abubuwan da suka fi daukar hankali a taron sun hada da gabatar da al’adu da al’ummar Kodomti da Bandawa suka nuna.

Kwamoti

A nasu bangaren, daliban makarantar firamare ta Kodomti sun gabatar da jawabai da dama cikin wakoki da kasidu domin nuna godiya ga dan majalisar tarayyar.

Cikin manyan bakin da suka halarci bikin sun hada da Ndewodi Kodomti, Ha Shaforon, Hon. Pwamwakaino Makondo, shugabannin kananan hukumomin Numan da Lamurde.

Shugabannin jam’iyyarsa da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar PDP a Numan, Demsa Lamurde duk sun halarci taro.

Kwamoti

Haka kuma dan majalisa Kwamoti B La’ori, ya ziyarci kasuwar Numan, domin jajanta wa ‘yan kasuwar da iftila’in gobara ya kone musu shaguna kurmus.

Ya yi fatan Allah ya tsayar da lamarin haka, sannan ya yi alkawarin tallafa musu.

Kwamoti
Muh'd Shafi'u Saleh
+ postsBio
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Shahararren Malamin Addinin Islama A Adamawa Sheikh Ibrahim Abubakar Daware Ya Rasu
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    An Yi Wa ‘Yansanda 110 Ƙarin Girma A Adamawa
  • Muh'd Shafi'u Saleh
    https://hausa.leadership.ng/author/muhd-shafiu-saleh/
    Gwamna Fintiri Ya Nada Sabbin Sarakuna 7 A Jihar Adamawa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Sin Na Fatan Taimakawa Ghana Kan Matsalar Basusukan Da Ake Bin Ta

Sin Na Fatan Taimakawa Ghana Kan Matsalar Basusukan Da Ake Bin Ta

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.