• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamoti La’ori ya Kaddamar Da Dakin Zana Jarabawa A GDSS Gamadio

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
in Labarai
0
Kwamoti La’ori ya Kaddamar Da Dakin Zana Jarabawa A GDSS Gamadio
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wannan lokaci ne na murna ga dalibai, iyaye, da al’ummar yankin raya karkara ta gundumar Vulpi a Karamar Hukumar Numan a Jihar Adamawa, yayin da dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Demsa/Numan/Lamurde ya gina musu dakin zana jarabawa.

Da yake gabatar da jawabi a taron, shugaban makarantar GDSS Gamadio, Mista Zacheaus, wanda ya nuna farin cikinsa, ya bayyana yadda daliban ke tafiya kananan hukumomin Lamurde da Demsa makwabciyarsu domin rubuta jarrabawar WAEC da NECO.

  • Shekarau Ga Tinubu: Ka Rage Yawan Ministocinka Domin Rage Kashe Kudade
  • An Gano Dukiyar Iyalan Masarautar Saudiyya Ta Fi Ta Masu Arzikin Duniya Biyu Yawa

Ya bayyana cewa ko da aka kafa cibiyoyin WAEC da NECO a shekarar 2019, dole ne a dakatar da darusa don barin ajujuwan da za a yi amfani da su har tsawon lokacin zana jarrabawar, saboda matsalar rashin dakin zana jarabawar da za a yi wa dalibai.

Shugaban ya kuma yi kira ga dan majalisar da ya kara kaimi, a fannin dakunan gwaje-gwaje na kimiyya da na’ura mai kwakwalwa gami da inganta ajujuwan makarantun domin bai wa dalibai damar karatu mai inganci.

Shi ma da yake jawabi a taron, dan majalisar, Kwamoti La’ori, ya tabbatar wa al’ummar yankin zai ci gaba da jajircewa na ganin sun kai ga morar mulkin dimokuradiyya.

Labarai Masu Nasaba

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Kwamoti dan majalisa ne da ke kyakkyawar niyya don isar da ayyukan more rayuwa ga al’umma a fadin unguwani 30 na mazabarsa, aikin da masu jawabai da dama a taron suka bayyana da cewa “ba a taba ganin dan majalisa kamar sa ba a tarihin mazabarsa da Jihar Adamawa”.

Dan majalisar bai gushe ba sai da ya bayyana aniyarsa ta ci gaba da inganta fannin ilimi da kuma kudurin kawo sauyi a rayuwar al’ummarsa.

A yayin jawabinsa, ya nuna jin dadinsa ga jama’a bisa goyon bayan da suke ba shi a kowane lokaci.

Shugabannin kananan hukumomin Numan da Lamurde da sarakunan gargajiya da shugabannin jam’iyyun siyasa da masu ruwa da tsaki sun gabatar da jawabin fatan alheri, inda suka yaba da salon shugabancin dan majalisar.

Dalibai da daukacin mahalarta taron sun nuna anshuwa da jin dadinsu a cikin jawabai da kasidu da raye-raye da kuma wakokin yabo ga Allah da ya ba su Honorable Kwamoti La’ori, a matsayin wakilinsu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Shekarau Ga Tinubu: Ka Rage Yawan Ministocinka Domin Rage Kashe Kudade

Next Post

ICPC Da NITDA Sun Kulla Alakar Aiki Don Yaki Da Rashawa Ta Hanyar Fasaha

Related

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

8 minutes ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

9 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

12 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

14 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

15 hours ago
‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki
Labarai

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

17 hours ago
Next Post
ICPC Da NITDA Sun Kulla Alakar Aiki Don Yaki Da Rashawa Ta Hanyar Fasaha

ICPC Da NITDA Sun Kulla Alakar Aiki Don Yaki Da Rashawa Ta Hanyar Fasaha

LABARAI MASU NASABA

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Kwamoti

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.