• English
  • Business News
Thursday, October 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwamoti La’ori ya Kaddamar Da Dakin Zana Jarabawa A GDSS Gamadio

by Muh'd Shafi'u Saleh
2 years ago
Kwamoti

Wannan lokaci ne na murna ga dalibai, iyaye, da al’ummar yankin raya karkara ta gundumar Vulpi a Karamar Hukumar Numan a Jihar Adamawa, yayin da dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Demsa/Numan/Lamurde ya gina musu dakin zana jarabawa.

Da yake gabatar da jawabi a taron, shugaban makarantar GDSS Gamadio, Mista Zacheaus, wanda ya nuna farin cikinsa, ya bayyana yadda daliban ke tafiya kananan hukumomin Lamurde da Demsa makwabciyarsu domin rubuta jarrabawar WAEC da NECO.

  • Shekarau Ga Tinubu: Ka Rage Yawan Ministocinka Domin Rage Kashe Kudade
  • An Gano Dukiyar Iyalan Masarautar Saudiyya Ta Fi Ta Masu Arzikin Duniya Biyu Yawa

Ya bayyana cewa ko da aka kafa cibiyoyin WAEC da NECO a shekarar 2019, dole ne a dakatar da darusa don barin ajujuwan da za a yi amfani da su har tsawon lokacin zana jarrabawar, saboda matsalar rashin dakin zana jarabawar da za a yi wa dalibai.

Shugaban ya kuma yi kira ga dan majalisar da ya kara kaimi, a fannin dakunan gwaje-gwaje na kimiyya da na’ura mai kwakwalwa gami da inganta ajujuwan makarantun domin bai wa dalibai damar karatu mai inganci.

Shi ma da yake jawabi a taron, dan majalisar, Kwamoti La’ori, ya tabbatar wa al’ummar yankin zai ci gaba da jajircewa na ganin sun kai ga morar mulkin dimokuradiyya.

LABARAI MASU NASABA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Kwamoti dan majalisa ne da ke kyakkyawar niyya don isar da ayyukan more rayuwa ga al’umma a fadin unguwani 30 na mazabarsa, aikin da masu jawabai da dama a taron suka bayyana da cewa “ba a taba ganin dan majalisa kamar sa ba a tarihin mazabarsa da Jihar Adamawa”.

Dan majalisar bai gushe ba sai da ya bayyana aniyarsa ta ci gaba da inganta fannin ilimi da kuma kudurin kawo sauyi a rayuwar al’ummarsa.

A yayin jawabinsa, ya nuna jin dadinsa ga jama’a bisa goyon bayan da suke ba shi a kowane lokaci.

Shugabannin kananan hukumomin Numan da Lamurde da sarakunan gargajiya da shugabannin jam’iyyun siyasa da masu ruwa da tsaki sun gabatar da jawabin fatan alheri, inda suka yaba da salon shugabancin dan majalisar.

Dalibai da daukacin mahalarta taron sun nuna anshuwa da jin dadinsu a cikin jawabai da kasidu da raye-raye da kuma wakokin yabo ga Allah da ya ba su Honorable Kwamoti La’ori, a matsayin wakilinsu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 
Manyan Labarai

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC
Manyan Labarai

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Next Post
ICPC Da NITDA Sun Kulla Alakar Aiki Don Yaki Da Rashawa Ta Hanyar Fasaha

ICPC Da NITDA Sun Kulla Alakar Aiki Don Yaki Da Rashawa Ta Hanyar Fasaha

LABARAI MASU NASABA

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

Sheikh Gumi Ya Yabi Tinubu Kan Afuwar Da Ya Yi Wa Maryam Sanda 

October 30, 2025
Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

Yadda Ta Gudana A Taron Karɓar Ƴan Majalisa Shida Da Suka Koma APC

October 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

Majalisar Dattawa Ta Tabbatar Da Bernard Doro A Matsayin Ministan Harkokin Jin Ƙai

October 30, 2025
Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

Wata 3 Da Naɗin Shugaban APC, Sunan Yilwatda Har Yanzu Na Nan A Matsayin Minista A Shafin Ma’aikatar

October 30, 2025
Tinubu Ya Nada Musa Aliyu A Matsayin Shugaban ICPC

Tinubu Ya Amince Da Ƙara Harajin Shigo Da Man Fetur Da Dizal Zuwa Kashi 15

October 30, 2025
Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

Sin Za Ta Harba Kumbon Shenzhou-21

October 30, 2025
Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

Xi Jinping: Sin Da Amurka Za Su Iya Hada Kai Don Sauke Nauyin Dake Wuyansu Na Manyan Kasashe Da Daukar Ainihin Matakai

October 30, 2025
Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

Sojoji Sun Ceto Wani Mutum Da Aka Sace A Taraba

October 30, 2025
Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

Majalisar Dokokin Kano Ta Ce An Yi Rashin Adalci Wajen Ɗaukar Aikin Kwastam A Nijeriya

October 30, 2025
Kwamoti

Bai Kamata Gwamnati Ta Ke Ciyo Bashi Bayan Cire Tallafin Man Fetur Ba – Sanusi II

October 30, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.