• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwastam Ta Kama Kayan Fasa-Kwauri Na Miliyan 46 A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
Kwastam

Hukumar Hana Fasa-Kwauri ta Kasa (Kwastam) a Jihar Kebbi ta samu nasarar kama wasu kayan sawa na hannu na kimanin Naira miliyan 36 da kuma samar da Naira miliyan 127 a matsayin kudin shiga a watan Nuwamba.

Shugaban Hukumar Kwastam, Kwanturola Joseph Attah ne, ya bayyana hakan ga manema labarai a Birnin Kebbi, yayin da yake baje kolin kayayyakin da hukumar ta kama a watan da ya gabata.

  • Kyawawan Halaye 2: Wasu Annabawa Da Sauran Bayin Allah Da Suka Yi Magana A Tsummar Jego
  • Shugaban Kasar Sin Ya Yi Shawarwari Da Manyan Shugabannin Kasar Saudiyya Da Kuma Gana Da Shugabannin Wasu Kasashen Larabawa Bi da Bi

Da yake ba da cikakken bayani kan ayyukan rundunar, Attah ya ce, rundunar ta samu kudi miliyan dari da ashirin da bakwai, da dubu dari takwas da talatin da tara, da naira dari uku da casa’in (127,839,390.75) a matsayin kudaden shiga daga shigo da kayan fasa-kwauri a kan hanyar iyakar Kamba da ke Jamhuriyar Nijar daga Jihar kebbi.

A bangaren yaki da fasa-kwauri, ya bayyana cewa, a yayin da ake ci gaba da sintiri a fadin Jihar Kebbi, rundunar ta samu nasarar kame wasu kayayyaki da suka hada da dila 303 da buhu 94 na tufafin gwanjo guda 94, mota kirar BMW guda daya, lita mai 2,375 a cikin jarkoki da kuma buhunan shinkafa 58 na kasar waje mai nauyin kilo 50 kowanne; da sauran wadanda kudin harajinsu ya kai miliyan arba’in da shida, da dubu dari bakwai da shida, da naira dari bakwai da casa’in da biyar (46,706,795.00).

Haka kuma, Kwanturola Joseph Attah, ya ba da tabbacin cewa jami’ansa a shirye suke su dakile ayyukan masu fasa-kwauri saboda rundunar tana da kayan aikin da suka dace don gudanar da aikin a kowane lokaci.

LABARAI MASU NASABA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

“Daga bayanan da muka samu, an samu karuwar kayan fasa-kwauri a cikin watanni biyu da suka gabata.”

“Idan za a tuna cewa an kuma kama dilar gwanjo 139 a watan Oktoba.

“Masu fasa-kwaurin suna biyan bukatun mutane masu kauri irin su cardigans a wannan lokacin na sanyi don safarar wadannan tufafin da aka yi amfani da su, ba tare da la’akari da tasirin kiwon lafiya ba har zuwa karshen amfani da su.

“Ba mu san daga ina kayan suka fito ba ko kuma na karshe masu amfani da tufafin, yanayin lafiyarsu da sauransu.

“Don guje wa shakku, tufafin hannu na biyu sun fado a karkashin jadawalin kasuwanci na (CET) 2022-2026, wanda aka haramta shigo da shi a kasan lafiya. Batun fasa kwaurinta ya ci karo da sashe na 46 na dokar hukumar kwastam (CEMA) CAP C. 45 LFN, 2004 (kamar wadda aka yi wa kwaskwarima).

“Hakkin hukumar kwastam ne ta tabbatar da cewa ba a bar wani abu da zai iya cutar da mutanen kasa ba. Mun kuduri aniyar yin hakan,” in ji shi.

Hukumar ta yaba da tallafin da hukumar ke bayarwa ta hanyar samar da dabaru kuma ta kuduri aniyar tunkarar masu fasa-kwauri a jahohin kasar nan.

Hukumar ta CAC ta yi kira ga duk masu hannu da shuni da su tallafa wa rundunar ofishin Kwastam na Jihar Kebbi ta hanyar samar da bayanai masu inganci don samun nasarorin gudanar da ayyukan dakile fasa-kwauri.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Kwastam
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Next Post
An Mikawa Kamfanin China Eastern Jirgin Sama Kiran C919 Na Farko Da Kasar Sin Ta Kera Da Kanta

An Mikawa Kamfanin China Eastern Jirgin Sama Kiran C919 Na Farko Da Kasar Sin Ta Kera Da Kanta

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Kwastam

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.