• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Sama Da Miliyan 23 A Kebbi

by Umar Faruk
2 years ago
in Labarai
0
Kwastam Ta Kama Kayayyakin Sama Da Miliyan 23 A Kebbi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kwastam reshen jihar Kebbi ta kama wasu kayayyaki na fasa kwabri da harajinsu ya kai Naira Miliyan ashirin da uku, da dubu dari da arba’in da daya, da naira dari takwas da uku (23,141,803) a wurare daban-daban na jihar.

Shugaban yankin, Dakta Ben Oramalugo ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai a a hedikwatar ofishin hukumar da ke Birnin Kebbi.

  • NIS Na Saukaka Samun Fasfo A Ribas, Ta Samar Da Fasfo 6,000 A Wata Guda

 

Shugaban Kwastam din, ya ce a cikin watanni biyu da suka wuce ne ya karbi ragamar shugabancin ofishin jihar , inda ya samu gagarumar nasara a fannin samun kudaden shiga, yayin da ya jaddada cewa a cikin watan Maris hukumar ta samu jimillar kudi Naira Miliyan dari da arba’in da hudu, da dubu dari takwas da sittin da biyu, da naira dari uku da saba’in da biyu (N144, 862,372).

Kwastam

Labarai Masu Nasaba

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

“Muna da fatan cimma kudurin hukumar na tara kudaden shiga na shekara- shekara na reshen Kebbi da ya kai Naira biliyan daya da miliyan hamsin da takwas, da dubu dari bakwai da biyu da dari hudu da sittin da shida (N 1, 058,702,466). Sannan za a magance babban kalubalen da masu ruwa da tsakinmu suka gano na biyan haraji da yawa daga kasashen da ke makwabtaka da mu kafin kayayyakinsu su isa iyakar kasa da ke a garin Kamba, wadda ita ce daya tilo da ake budewa a halin yanzu a cikin jihar”, in ji shi.

Ya kara da cewa, kayayyakin da aka kama sun hada da: Fetur lita 16, 375, katan na spaghetti 210 na kasar waje, bale 34 na kayan sawa na hannu da kuma katan 109 na kayan zaki da dai sauransu.

Kwastam

Haka kuma ya kara da cewa “mun samu sahihin bayanan sirri na ayyukan fasakwauri na Fetur a gidan man AP da ke Yauri a karamar hukumar Yauri a jihar, an tura tawagar jami’an hukumar zuwa wurin kuma nan take aka kama su.

“Mun iya kwashe kilogiram dari uku da hudu (304) na Fetur mai lita 25 kowanne, tare da rufe gidan man da ke karamar hukumar da muka ambata tare da tankokin mai gudu shida a cikin gidan man, yanza hakan muna kan bincike kan lamarin.

“Har ilayau masu fasa kwauri da kansu suka dawo tare da wasu ‘yan baranda da nufin hana kwace man na fasa kwauri, amma mutanen mu sun tsaya tsayin daka har zuwa lokacin da muka samu agajin sojojin Nijeriya wadanda suka taimaka mana wajen tarwatsa masu fasa kwaurin.”

Kwastam

Kazalika Shugaban hukumar, Dokta Ben Oramalugo ya gargadi masu fasa kwauri da masu taimaka musu a fadin jihar da su guji aikata munanan ayyukan. Domin a cewarsa, “Ba za mu nade hannu ba, mu bar duk wani gidan man da za a yi amfani da shi a matsayin bututun fitar Fetur daga kasar nan ba, gwamnatinmu na biyan makudan kudade wajen ba da tallafa mai ga ‘yan kasar, wanda hakan ya sa ya zama abin zargi da rashin bin doka ga wasu mutane kalilan su karkatar da man, don bunkasa kansu, inji shi”.

Ya kuma ba da tabbacin hukumar kwastam ta Nijeriya, reshen jihar Kebbi, za ta ci gaba da jajircewa wajen dakile ayyukan fasakwauri ba bisa ka’ida ba, kasancewar suna da kayan aiki. “Bugu da kari muna da horo wajen dakile duk ayyukansu”. Ya bayyana.

Daga nan ya gode wa duk ’yan kasa musamman na jihar da ke taimakawa Kwastam da bayanai masu amfani wajen dakile fasakwaurin da ake yi a jihar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Fasa KwauriFeturKebbiKwastam
ShareTweetSendShare
Previous Post

Saurin Farfadowar Tattalin Arzikin Sin Yana Kara Habaka Ci Gaban Yankin Asiya Da Duniya Baki Daya

Next Post

Shirin Mika Mulki: Buhari Da Gwamnoni Za Su Sake Bayyana Kadarorinsu

Related

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

2 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

3 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

4 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

5 hours ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

6 hours ago
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara
Tsaro

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

6 hours ago
Next Post
Shirin Mika Mulki: Buhari Da Gwamnoni Za Su Sake Bayyana Kadarorinsu

Shirin Mika Mulki: Buhari Da Gwamnoni Za Su Sake Bayyana Kadarorinsu

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

Matasa Sun Nemi A Tura Sojoji Don Korar Ƴan Bindiga Daga Kwara

August 23, 2025
Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

Hotuna: Shettima Ya Wakilci Shugaba Tinubu Wajen Jana’izar Sarkin Zuru

August 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gwamnatin Tarayya Ta Sha Alwashin Kama Waɗanda Suka Kashe Masallata A Malumfashi 

August 23, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

Gwamnatin Tarayya Na Hasashen Samun Naira Biliyan 300 Kan Noman Dabino A Yobe

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.