ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Sama Da Miliyan 23 A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
Kwastam

Hukumar kwastam reshen jihar Kebbi ta kama wasu kayayyaki na fasa kwabri da harajinsu ya kai Naira Miliyan ashirin da uku, da dubu dari da arba’in da daya, da naira dari takwas da uku (23,141,803) a wurare daban-daban na jihar.

Shugaban yankin, Dakta Ben Oramalugo ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai a a hedikwatar ofishin hukumar da ke Birnin Kebbi.

  • NIS Na Saukaka Samun Fasfo A Ribas, Ta Samar Da Fasfo 6,000 A Wata Guda

 

ADVERTISEMENT

Shugaban Kwastam din, ya ce a cikin watanni biyu da suka wuce ne ya karbi ragamar shugabancin ofishin jihar , inda ya samu gagarumar nasara a fannin samun kudaden shiga, yayin da ya jaddada cewa a cikin watan Maris hukumar ta samu jimillar kudi Naira Miliyan dari da arba’in da hudu, da dubu dari takwas da sittin da biyu, da naira dari uku da saba’in da biyu (N144, 862,372).

Kwastam

LABARAI MASU NASABA

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

“Muna da fatan cimma kudurin hukumar na tara kudaden shiga na shekara- shekara na reshen Kebbi da ya kai Naira biliyan daya da miliyan hamsin da takwas, da dubu dari bakwai da biyu da dari hudu da sittin da shida (N 1, 058,702,466). Sannan za a magance babban kalubalen da masu ruwa da tsakinmu suka gano na biyan haraji da yawa daga kasashen da ke makwabtaka da mu kafin kayayyakinsu su isa iyakar kasa da ke a garin Kamba, wadda ita ce daya tilo da ake budewa a halin yanzu a cikin jihar”, in ji shi.

Ya kara da cewa, kayayyakin da aka kama sun hada da: Fetur lita 16, 375, katan na spaghetti 210 na kasar waje, bale 34 na kayan sawa na hannu da kuma katan 109 na kayan zaki da dai sauransu.

Kwastam

Haka kuma ya kara da cewa “mun samu sahihin bayanan sirri na ayyukan fasakwauri na Fetur a gidan man AP da ke Yauri a karamar hukumar Yauri a jihar, an tura tawagar jami’an hukumar zuwa wurin kuma nan take aka kama su.

“Mun iya kwashe kilogiram dari uku da hudu (304) na Fetur mai lita 25 kowanne, tare da rufe gidan man da ke karamar hukumar da muka ambata tare da tankokin mai gudu shida a cikin gidan man, yanza hakan muna kan bincike kan lamarin.

“Har ilayau masu fasa kwauri da kansu suka dawo tare da wasu ‘yan baranda da nufin hana kwace man na fasa kwauri, amma mutanen mu sun tsaya tsayin daka har zuwa lokacin da muka samu agajin sojojin Nijeriya wadanda suka taimaka mana wajen tarwatsa masu fasa kwaurin.”

Kwastam

Kazalika Shugaban hukumar, Dokta Ben Oramalugo ya gargadi masu fasa kwauri da masu taimaka musu a fadin jihar da su guji aikata munanan ayyukan. Domin a cewarsa, “Ba za mu nade hannu ba, mu bar duk wani gidan man da za a yi amfani da shi a matsayin bututun fitar Fetur daga kasar nan ba, gwamnatinmu na biyan makudan kudade wajen ba da tallafa mai ga ‘yan kasar, wanda hakan ya sa ya zama abin zargi da rashin bin doka ga wasu mutane kalilan su karkatar da man, don bunkasa kansu, inji shi”.

Ya kuma ba da tabbacin hukumar kwastam ta Nijeriya, reshen jihar Kebbi, za ta ci gaba da jajircewa wajen dakile ayyukan fasakwauri ba bisa ka’ida ba, kasancewar suna da kayan aiki. “Bugu da kari muna da horo wajen dakile duk ayyukansu”. Ya bayyana.

Daga nan ya gode wa duk ’yan kasa musamman na jihar da ke taimakawa Kwastam da bayanai masu amfani wajen dakile fasakwaurin da ake yi a jihar.

Kwastam
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnatin Kebbi Ta Amince Da ₦2.07bn Alawus-alawus Ga Ma’aikatan Manyan Makarantu
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Maye Gurbin Mataimakinsa Da Ibrahim Augie A Zaɓen 2027
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Matashi Ya Shiga Hannu Kan Zargin Wulaƙanta Alƙur’ani A Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Miƙa Yara 5 Da Aka Ceto Daga Hannun Masu Safarar Mutane Ga Iyayensu

MASU ALAKA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja
Labarai

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
'Yan Bindiga
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Next Post
Shirin Mika Mulki: Buhari Da Gwamnoni Za Su Sake Bayyana Kadarorinsu

Shirin Mika Mulki: Buhari Da Gwamnoni Za Su Sake Bayyana Kadarorinsu

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.