ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kwastam Ta Kama Kayayyakin Sama Da Miliyan 23 A Kebbi

by Umar Faruk
3 years ago
Kwastam

Hukumar kwastam reshen jihar Kebbi ta kama wasu kayayyaki na fasa kwabri da harajinsu ya kai Naira Miliyan ashirin da uku, da dubu dari da arba’in da daya, da naira dari takwas da uku (23,141,803) a wurare daban-daban na jihar.

Shugaban yankin, Dakta Ben Oramalugo ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai a a hedikwatar ofishin hukumar da ke Birnin Kebbi.

  • NIS Na Saukaka Samun Fasfo A Ribas, Ta Samar Da Fasfo 6,000 A Wata Guda

 

ADVERTISEMENT

Shugaban Kwastam din, ya ce a cikin watanni biyu da suka wuce ne ya karbi ragamar shugabancin ofishin jihar , inda ya samu gagarumar nasara a fannin samun kudaden shiga, yayin da ya jaddada cewa a cikin watan Maris hukumar ta samu jimillar kudi Naira Miliyan dari da arba’in da hudu, da dubu dari takwas da sittin da biyu, da naira dari uku da saba’in da biyu (N144, 862,372).

Kwastam

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

“Muna da fatan cimma kudurin hukumar na tara kudaden shiga na shekara- shekara na reshen Kebbi da ya kai Naira biliyan daya da miliyan hamsin da takwas, da dubu dari bakwai da biyu da dari hudu da sittin da shida (N 1, 058,702,466). Sannan za a magance babban kalubalen da masu ruwa da tsakinmu suka gano na biyan haraji da yawa daga kasashen da ke makwabtaka da mu kafin kayayyakinsu su isa iyakar kasa da ke a garin Kamba, wadda ita ce daya tilo da ake budewa a halin yanzu a cikin jihar”, in ji shi.

Ya kara da cewa, kayayyakin da aka kama sun hada da: Fetur lita 16, 375, katan na spaghetti 210 na kasar waje, bale 34 na kayan sawa na hannu da kuma katan 109 na kayan zaki da dai sauransu.

Kwastam

Haka kuma ya kara da cewa “mun samu sahihin bayanan sirri na ayyukan fasakwauri na Fetur a gidan man AP da ke Yauri a karamar hukumar Yauri a jihar, an tura tawagar jami’an hukumar zuwa wurin kuma nan take aka kama su.

“Mun iya kwashe kilogiram dari uku da hudu (304) na Fetur mai lita 25 kowanne, tare da rufe gidan man da ke karamar hukumar da muka ambata tare da tankokin mai gudu shida a cikin gidan man, yanza hakan muna kan bincike kan lamarin.

“Har ilayau masu fasa kwauri da kansu suka dawo tare da wasu ‘yan baranda da nufin hana kwace man na fasa kwauri, amma mutanen mu sun tsaya tsayin daka har zuwa lokacin da muka samu agajin sojojin Nijeriya wadanda suka taimaka mana wajen tarwatsa masu fasa kwaurin.”

Kwastam

Kazalika Shugaban hukumar, Dokta Ben Oramalugo ya gargadi masu fasa kwauri da masu taimaka musu a fadin jihar da su guji aikata munanan ayyukan. Domin a cewarsa, “Ba za mu nade hannu ba, mu bar duk wani gidan man da za a yi amfani da shi a matsayin bututun fitar Fetur daga kasar nan ba, gwamnatinmu na biyan makudan kudade wajen ba da tallafa mai ga ‘yan kasar, wanda hakan ya sa ya zama abin zargi da rashin bin doka ga wasu mutane kalilan su karkatar da man, don bunkasa kansu, inji shi”.

Ya kuma ba da tabbacin hukumar kwastam ta Nijeriya, reshen jihar Kebbi, za ta ci gaba da jajircewa wajen dakile ayyukan fasakwauri ba bisa ka’ida ba, kasancewar suna da kayan aiki. “Bugu da kari muna da horo wajen dakile duk ayyukansu”. Ya bayyana.

Daga nan ya gode wa duk ’yan kasa musamman na jihar da ke taimakawa Kwastam da bayanai masu amfani wajen dakile fasakwaurin da ake yi a jihar.

Kwastam
Umar Faruk
+ postsBio
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Sace ‘Yan Makarantar Mata Ta Kebbi: Abubuwan Da Ba A Fada Ba
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Dakatar da Kwamishinan Ma’aikatar Lafiya Biyo Bayan Sakaci A Aiki
  • Umar Faruk
    https://hausa.leadership.ng/author/umar-faruk/
    Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

MASU ALAKA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna
Labarai

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Next Post
Shirin Mika Mulki: Buhari Da Gwamnoni Za Su Sake Bayyana Kadarorinsu

Shirin Mika Mulki: Buhari Da Gwamnoni Za Su Sake Bayyana Kadarorinsu

LABARAI MASU NASABA

Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.