• English
  • Business News
Monday, July 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Na Saukaka Samun Fasfo A Ribas, Ta Samar Da Fasfo 6,000 A Wata Guda

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
NIS Na Saukaka Samun Fasfo A Ribas, Ta Samar Da Fasfo 6,000 A Wata Guda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kula da shige da fice ta kasa (NIS) reshen jihar Ribas ta himmatu wajen fito da tsare-tsaren da suke saukakawa da shawo kan matsalolin da ake samu na jinkirin samar da fasfo domin kauce wa matsin lamba na bukatar fasfon.

NIS a karkashin jagorancin CIS James Sunday a jihar ta Ribas ta samar da littafin fasfot har guda 6,000 a cikin wata daya tak da ya taimaka sosai wajen rage tulin bukatun fasfo da jama’a ke gabatawa da kuma saukaka samar wa mutane da fasfo din.

Sabon jami’in kula da harkokin fasfo, mai mukamim mataimakin Kwanturola, Audi Musa Maisudan sa’ilin da ke bayani wa Kwanturolan hukumar na jihar, James Sunday a lokacin ziyarar aiki zuwa ofishin aikin fasfo da ke Mile 1 a garin Fatakwal, ya ce, sabon tsarin ya rage jinkirin da ake samu wajen samar wa jama’a da fasfon a lokacin da suka bukata.

  • Magoya Bayan PDP Sun Yi Zanga-Zanga Dauke Da Kayan Tsafi A Ribas

 

A nasa bangaren, Kwanturola James Sunday, ya jinjina wa sabon jami’in tare da tawagarsa bisa himmar da suka nuna wajen biyayya ga umarnin ministan harkokin cikin gida Ogbeni Rauf Aregbesola da Kwanturol Janar na hukumar NIS, CGI Isah Jere Idris na cewa kada a bari samar wa jama’a da Fasfo ya zama abun damuwa ko wahala ga ‘yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

Sanata Dickson Ya BuÆ™aci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi YaÆ™i Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Ya ce, umarnin ya taimaka matuka wajen saukaka hanyoyin da ake bi wajen samar da fasfon ta yadda ake biya wa masu bukatun fasfot din bukatun su ba tare da wani tarnaki ba.

A cewarsa, “Tsarin ya taimaka wajen rage koma baya da shan wahala, kuma duk mai bukata da ya bi ka’ida yana samun fasfo din sa a ranakun da aka gindaya wanda ya rage caza kwakwalwa, da kawo saukin aiki.”

“Na kawo ziyarar ce domin gani da idona kan ko an bi umarnin Minista da Kwanturola Janar, kuma na gamsu da yadda na ga Jami’ai sun dukufa wajen inganta aiki. Kuma dole ne a mutunta jama’a a samar musu da fasfo kan lokaci kuma bisa sauki ba tare da sai sun sha wahala ba.

“Mun kuma kwashi tsoffin hannu wadanda suka jima mun sauya musu sashi illa iyaka kwararrun da ake da bukatar aikinsu matuka, yin hakan zai ba da dama wadanda suka dace kuma suke da karsashin aikin su ne za su rika tafiyar da lamuran domin saukaka samar da fasfo ga jama’a.”

Daga bisani ya gargadi masu sako-sako da aiki ko kauce wa ka’idar aiki su shiga taitayinsu domin hukumar ta NIS ba za ta lamunci sakaci da aiki ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikiFasfonNIS
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Fitar Da Rahoton Farko Game Da Cika Shekaru 10 Da Kaddamar Da Shawarar Kafa Al’umma Mai Makomar Bai Daya Ga Dukkanin Bil Adama

Next Post

A Ci Gaba Da Wanzar Da Ruhin Mazan Jiya, In Ji Xi Jinping

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Da É—umi-É—uminsa

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

9 hours ago
Sanata Dickson Ya BuÆ™aci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi YaÆ™i Da Matsalar Sayen Ƙuri’a
Labarai

Sanata Dickson Ya BuÆ™aci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi YaÆ™i Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

10 hours ago
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya ÆŠaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson
Labarai

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya ÆŠaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

11 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Ranar Talata Mai Zuwa Zan Koma Zauren Majalisar Dattawa – Sanata Natasha

14 hours ago
Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da ÆŠaliban Kaduna Kyauta A Bas
Labarai

Za A Fara Sufurin Ma’aikata Da ÆŠaliban Kaduna Kyauta A Bas

17 hours ago
Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos
Labarai

Mutane 8 Sun Mutu A Wani Mummunan Hatsari A Hanyar Lagos

18 hours ago
Next Post
A Ci Gaba Da Wanzar Da Ruhin Mazan Jiya, In Ji Xi Jinping

A Ci Gaba Da Wanzar Da Ruhin Mazan Jiya, In Ji Xi Jinping

LABARAI MASU NASABA

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Tunisiya Da Ci 3-0 A Moroko

July 6, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Boko Haram Sun Kashe Mutane 9, Tare Da Jikkata Wasu Mutum 4 A Borno

July 6, 2025
Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

Mataimakin Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Sabbin Fasahohin Kimiyya A Fannin Aikin Gona Da Kiwon Lafiya

July 6, 2025
Sanata Dickson Ya BuÆ™aci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi YaÆ™i Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

Sanata Dickson Ya BuÆ™aci ‘Yan Nijeriya Da Su Yi YaÆ™i Da Matsalar Sayen Ƙuri’a

July 6, 2025
Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

Xi Ya Ba Da Amsar Wasikar Matasan Amurka ’Yan Wasan Kwallon Pickle Bisa Ziyartar Sin

July 6, 2025
Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya ÆŠaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

Yankin Kudu-Maso-Kudu Zai Cimma Matsaya ÆŠaya Kan Gyaran Kundin Tsarin Mulki – Sanata Dickson

July 6, 2025
Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

Sin Za Ta Fadada Hadin Gwiwa Da Brazil A Fannin Tattalin Arzikin Fasahar Zamani Da Sha’anin Jiragen Sama

July 6, 2025
Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

Hadimin Gwamnan Yobe Ya Fice Daga APC Ya Koma Jam’iyyar ADC

July 6, 2025
Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

Masanin Kenya: Kasashe Masu Tasowa Suna Bukatar Kasar Sin

July 6, 2025
Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

Ba Ni Da Niyyar Barin APC Zuwa Wata Jam’iyyar — Gwamna Zulum

July 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.