ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Na Saukaka Samun Fasfo A Ribas, Ta Samar Da Fasfo 6,000 A Wata Guda

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Fasfo

Hukumar kula da shige da fice ta kasa (NIS) reshen jihar Ribas ta himmatu wajen fito da tsare-tsaren da suke saukakawa da shawo kan matsalolin da ake samu na jinkirin samar da fasfo domin kauce wa matsin lamba na bukatar fasfon.

NIS a karkashin jagorancin CIS James Sunday a jihar ta Ribas ta samar da littafin fasfot har guda 6,000 a cikin wata daya tak da ya taimaka sosai wajen rage tulin bukatun fasfo da jama’a ke gabatawa da kuma saukaka samar wa mutane da fasfo din.

Sabon jami’in kula da harkokin fasfo, mai mukamim mataimakin Kwanturola, Audi Musa Maisudan sa’ilin da ke bayani wa Kwanturolan hukumar na jihar, James Sunday a lokacin ziyarar aiki zuwa ofishin aikin fasfo da ke Mile 1 a garin Fatakwal, ya ce, sabon tsarin ya rage jinkirin da ake samu wajen samar wa jama’a da fasfon a lokacin da suka bukata.

ADVERTISEMENT
  • Magoya Bayan PDP Sun Yi Zanga-Zanga Dauke Da Kayan Tsafi A Ribas

 

A nasa bangaren, Kwanturola James Sunday, ya jinjina wa sabon jami’in tare da tawagarsa bisa himmar da suka nuna wajen biyayya ga umarnin ministan harkokin cikin gida Ogbeni Rauf Aregbesola da Kwanturol Janar na hukumar NIS, CGI Isah Jere Idris na cewa kada a bari samar wa jama’a da Fasfo ya zama abun damuwa ko wahala ga ‘yan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Ya ce, umarnin ya taimaka matuka wajen saukaka hanyoyin da ake bi wajen samar da fasfon ta yadda ake biya wa masu bukatun fasfot din bukatun su ba tare da wani tarnaki ba.

A cewarsa, “Tsarin ya taimaka wajen rage koma baya da shan wahala, kuma duk mai bukata da ya bi ka’ida yana samun fasfo din sa a ranakun da aka gindaya wanda ya rage caza kwakwalwa, da kawo saukin aiki.”

“Na kawo ziyarar ce domin gani da idona kan ko an bi umarnin Minista da Kwanturola Janar, kuma na gamsu da yadda na ga Jami’ai sun dukufa wajen inganta aiki. Kuma dole ne a mutunta jama’a a samar musu da fasfo kan lokaci kuma bisa sauki ba tare da sai sun sha wahala ba.

“Mun kuma kwashi tsoffin hannu wadanda suka jima mun sauya musu sashi illa iyaka kwararrun da ake da bukatar aikinsu matuka, yin hakan zai ba da dama wadanda suka dace kuma suke da karsashin aikin su ne za su rika tafiyar da lamuran domin saukaka samar da fasfo ga jama’a.”

Daga bisani ya gargadi masu sako-sako da aiki ko kauce wa ka’idar aiki su shiga taitayinsu domin hukumar ta NIS ba za ta lamunci sakaci da aiki ba.

Fasfo
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
A Ci Gaba Da Wanzar Da Ruhin Mazan Jiya, In Ji Xi Jinping

A Ci Gaba Da Wanzar Da Ruhin Mazan Jiya, In Ji Xi Jinping

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.