ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Na Saukaka Samun Fasfo A Ribas, Ta Samar Da Fasfo 6,000 A Wata Guda

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Fasfo

Hukumar kula da shige da fice ta kasa (NIS) reshen jihar Ribas ta himmatu wajen fito da tsare-tsaren da suke saukakawa da shawo kan matsalolin da ake samu na jinkirin samar da fasfo domin kauce wa matsin lamba na bukatar fasfon.

NIS a karkashin jagorancin CIS James Sunday a jihar ta Ribas ta samar da littafin fasfot har guda 6,000 a cikin wata daya tak da ya taimaka sosai wajen rage tulin bukatun fasfo da jama’a ke gabatawa da kuma saukaka samar wa mutane da fasfo din.

Sabon jami’in kula da harkokin fasfo, mai mukamim mataimakin Kwanturola, Audi Musa Maisudan sa’ilin da ke bayani wa Kwanturolan hukumar na jihar, James Sunday a lokacin ziyarar aiki zuwa ofishin aikin fasfo da ke Mile 1 a garin Fatakwal, ya ce, sabon tsarin ya rage jinkirin da ake samu wajen samar wa jama’a da fasfon a lokacin da suka bukata.

ADVERTISEMENT
  • Magoya Bayan PDP Sun Yi Zanga-Zanga Dauke Da Kayan Tsafi A Ribas

 

A nasa bangaren, Kwanturola James Sunday, ya jinjina wa sabon jami’in tare da tawagarsa bisa himmar da suka nuna wajen biyayya ga umarnin ministan harkokin cikin gida Ogbeni Rauf Aregbesola da Kwanturol Janar na hukumar NIS, CGI Isah Jere Idris na cewa kada a bari samar wa jama’a da Fasfo ya zama abun damuwa ko wahala ga ‘yan Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Ya ce, umarnin ya taimaka matuka wajen saukaka hanyoyin da ake bi wajen samar da fasfon ta yadda ake biya wa masu bukatun fasfot din bukatun su ba tare da wani tarnaki ba.

A cewarsa, “Tsarin ya taimaka wajen rage koma baya da shan wahala, kuma duk mai bukata da ya bi ka’ida yana samun fasfo din sa a ranakun da aka gindaya wanda ya rage caza kwakwalwa, da kawo saukin aiki.”

“Na kawo ziyarar ce domin gani da idona kan ko an bi umarnin Minista da Kwanturola Janar, kuma na gamsu da yadda na ga Jami’ai sun dukufa wajen inganta aiki. Kuma dole ne a mutunta jama’a a samar musu da fasfo kan lokaci kuma bisa sauki ba tare da sai sun sha wahala ba.

“Mun kuma kwashi tsoffin hannu wadanda suka jima mun sauya musu sashi illa iyaka kwararrun da ake da bukatar aikinsu matuka, yin hakan zai ba da dama wadanda suka dace kuma suke da karsashin aikin su ne za su rika tafiyar da lamuran domin saukaka samar da fasfo ga jama’a.”

Daga bisani ya gargadi masu sako-sako da aiki ko kauce wa ka’idar aiki su shiga taitayinsu domin hukumar ta NIS ba za ta lamunci sakaci da aiki ba.

Fasfo
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Zaɓen Fidda Gwani Na Gwamna: Ba Za Mu Lamunci Kaƙaba Mana Ɗan Takara A Bauchi Ba – Mambobin APC
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Sanata Buba Ya Janye Daga Takarar Fidda Gwani Ta Gwamnan APC A Bauchi, Ya Zargi Cewa ‘Ɗauki Ɗaura Ake Yi Ba Zaɓe Ba”
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Shugaban Kwamitin Yaɗa Labarai Na Aikin Hajjin Bana Na Bauchi Ya Rasu A Saudiyya
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Na Bar Harƙoƙin Siyasa Gaba Ɗaya – Ɗan Takarar Gwamnan Bauchi, Air Marshal Saddique Baba

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
A Ci Gaba Da Wanzar Da Ruhin Mazan Jiya, In Ji Xi Jinping

A Ci Gaba Da Wanzar Da Ruhin Mazan Jiya, In Ji Xi Jinping

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.