• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyan Alkawari Cikawa

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
alkawari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanakin nan ne, sakataren harkokin wajen kasar Amurka Antony Blinken ya ziyarci kasashen Cape Verde da Cote d’Ivoire da Nijeriya da kuma Angola, a yunkurin nuna yadda Amurka ke sanya kasashen Afirka a cikin jerin kasashen da take baiwa fifiko a harkokin diplomasiyya. Duk da cewa jami’an gwamnatin Amurka sun yi ta bayyana cewa, ziyarar ba ta da alaka da takarar da take yi da kasar Sin, amma kafofin yada labarai na kasar ta Amurka da dama, suna ci gaba da alakanta ziyarar da batun “dakile tasirin kasashen Sin da Rasha a nahiyar” . Jaridar New York Times a wata makalar da ta wallafa a ranar 22 ga wata, ta bayyana cewa, Afirka nahiya ce da Amurka ke takara da Sin da Rasha, kuma Mista Blinken na “wani kokarin samo wasu kyawawan labarai daga Afirka”.

A hakika, dalilin da ya sa kafofin yada labarai na kasar Amurka suka alakanta ziyarar mista Blinken a Afirka da kasar Sin, shi ne sabo da yadda ’yan siyasar kasar suka dade suna bayyana kasar Sin a matsayin “Babbar dadaddiyar abokiyar takara” a Afirka, wadanda suke ganin cewa, cikin shekaru 20 da suka gabata, tasirin kasar Sin a nahiyar Afirka sai kara karuwa yake yi, don haka, dole ne Amurka ta “dauki matakai na dakile wannan tasiri”.

  • Sin Ta Ba Da Rahoton Fadada Shigo Da Kayayyakin Gona Da Na Abinci A Shekarar 2023
  • Shirin Cusa Ɗa’a Da Kishin Ƙasa: An Fitar Da Daftarin Yaɗa Kyawawan Ɗabi’un Farfaɗo da Martabar Nijeriya

Wannan ya sa, Amurka a cikin ’yan shekarun baya ta kara daukar matakan siyasa a kan Afirka. Idan ba mu manta ba, a karshen shekarar 2022, Amurka ta kira taron shugabannin Amurka da kasashen Afirka karo na biyu, tsawon shekaru 8 bayan taron da aka gudanar a karo na farko, inda shugaba Joe Biden ya yi alkawarin “yin iyakacin kokarin tabbatar da makomar Afirka”, kuma ya bayyana cewa, zai ziyarci Afirka a shekarar 2023. Amma abin takaici shi ne, shekarar 2023 tuni ta zama tarihi, amma har yanzu shugaban bai ziyarci Afirka ba, kuma ita Amurka din ma ba ta “yi wani kokari na tabbatar da makomar Afirka” kamar yadda ta alkawarta ba, lamarin da ya shaida cewa, Amurka ba ta mai da Afirka a matsayin harkar da take ba wa fifiko ba.

Me ya sa Amurka ke son daukar alkawura a gaban kasashen Afirka amma ba tare da cikawa ba? In mun yi nazari, za mu ga cewa ainihin abin da ya sa take bunkasa alakarta da kasashen Afirka shi ne don su ba ta taimako a ja-in-ja da take da wasu manyan kasashe, a maimakon a ce ta mai da su abokan hadin gwiwa na zaman daidaito da kuma cin moriyar juna, ballantana ta mai da hankali a kan daidaita matsalolin da ke ci musu tuwo a kwarya. Wannan shi ne dalilin da ya sa gwamnatin Biden ta dade tana cewa, za ta yi kokarin bunkasa alakarta da kasashen Afirka, amma kuma ba tare da cimma wani hakikanin sakamako ba. Madam Oge Onubogu,darektar kula da shirin Afirka a cibiyar masana ta kasa da kasa ta Woodrow Wilson da ke birnin Washington na kasar Amurka, ita ma ta bayyana cewa, a ziyarar da ta kai kasashen Afirka, ta gano dimbin manyan ababen more rayuwa da aka samar sakamakon shirin kasar Sin na bunkasa tattalin arziki a kasashen Afirka, amma kasashen Afirka ba su san me kasar Amurka ta iya yi musu ba.

A zahiri dai, bambamcin burin da ake neman cimmawa, ya sa an dauki mabambantan matakai, kuma hakan ya haifar da mabambantan sakamako.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Akasin yadda kasar Amurka ke tsara manufofinta a kan Afirka a yunkurin “yin takara da wasu”, kasar Sin na hulda da kasashen Afirka ne don neman cin moriyar juna, don haka, Sin da kasashen Afirka ke aiwatar da hadin gwiwarsu ta fannin bunkasa tattalin arziki da zaman al’umma, amma ba tare da tsoma baki a harkokin cikin gidan juna ba, haka kuma ba a gindaya sharudan siyasa ba. Sakamakon hadin gwiwarsu, an gudanar da jerin shirye-shirye na kyautata rayuwar jama’a, kuma manyan ababen more rayuwa na kasashen Afirka ma sun inganta a zahiri. Kafofin yada labarai na kasar Amurka sun kuma lura da cewa, a kasar Cape Verde, Mista Blinken ya sauka ne a wani ginin da kasar Sin ta gina, a yayin ziyararsa a Cote d’Ivoire kuma, ya je kallon gasar wasan kwallon kafa ta cin kofin kasashen Afirka a filin wasan Alassane Ouattara, wanda kasar Sin ce ta ba da gudummawar gina shi.

A hakika, kullum kasar Sin na ganin cewa, ya kamata nahiyar Afirka ta kasance dandalin hadin gwiwar kasa da kasa, a maimakon fagen takara a tsakaninsu. Kasashen Afirka yanzu haka na fuskantar kalubale ta fannonin farfadowar tattalin arziki da tabarbarewar harkokin tsaro da sauyin yanayi da makamantansu, don haka, akwai abubuwa da dama da Amurka take iya taimakawa. Kasar Sin na son ganin kasa da kasa sun aiwatar da hadin gwiwar cin moriyar juna bisa daidaito da kasashen Afirka, su samar da taimako na zahiri ga kasashen Afirka a maimakon furta kalaman da ba su dace ba.(Lubabatu Lei)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaSinUkraine
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tsadar Magunguna Na Barazana Ga Rayukan Majinyata A Nijeriya

Next Post

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Zai Tattauna Da Mashawarcin Shugaban Amurka Kan Tsaro Yayin Ziyararsa A Thailand

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

4 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

5 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

7 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

8 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

15 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

16 hours ago
Next Post
sin

Ministan Harkokin Wajen Kasar Sin Zai Tattauna Da Mashawarcin Shugaban Amurka Kan Tsaro Yayin Ziyararsa A Thailand

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.