• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyautatawa Al’umma Ita Ce Kashin Bayan Ci Gaban Ko Wacce Kasa

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Kyautatawa Al’umma Ita Ce Kashin Bayan Ci Gaban Ko Wacce Kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A yau Talata ne aka bude taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar Kasar Sin, inda firaministan kasar, Li Qiang ya gabatar da rahoton aikin gwamnati a bara. Cikin rahoton ya bayyana cewa, “Gwamnati ta cimma nasarar samun ci gaba mai inganci, da tabbatar da zaman lafiyar al’umma, lamarin da ya sa aka sami gagarumin ci gaba a fannin gina zamantakewar al’umma ta zamani bisa tsarin gurguzu a dukkanin fannoni.”

Dukkan ci gaban kasar Sin baya rasa nasaba da irin tsarin shugabancin da ta zabarwa kanta. Tsarin gurguzu mai sigar musamman ta kasar Sin, shi ne tushe kuma sirrin ci gaban kasar. Sin ta yi abun da ba kasafai a kan gani ba, wato ta duba yanayinta, ta kuma fadawa kan ta gaskiya, inda ta rika aiwatar da manufofi da dabarun da suka dace da yanayinta, maimakon zama ’yar a bi Yarima a sha kida.

  • Xi Jinping Ya Halarci Taron Tattaunawa A Yayin Taron Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

Na saba da jin ana cewa, “in dambu ya yi yawa baya jin mai” wato idan mutane suka yi yawa, to da wuya kowa ya ci gajiyar wata manufa ko shirin kyautatawa al’umma. Sai dai, zan iya cewa, duk da dimbin jama’a da kasar Sin take da shi, ba na jin ana irin wannan furuci, har kullum manufofin kasar kan isa ga wadanda aka yi domin su.

Wani batu shi ne, Kishin Kasa. Ana yawaita samun rikicin addini ko kabilanci a cikin gidan kasashen duniya da dama, amma duk da yawan kabilu da addinai dake a kasar Sin, ba ka jin tashin irin wadannan rigingimu. Abun da na lura da shi da al’ummar kasar shi ne, duk da cewa akwai kabilu daban daban, tuna cewa kai Basine ne, shi ne abu na farko kuma mafi muhimmanci kafin komai. Wato an dasawa Sinawa kishin kasa da kaunar kasa kafin komai, wanda ya zama tushen zaman lafiya da zaman jituwa da hakuri da juna da ake samu tsakanin al’ummun kasar daga mabambantan kabilu.

Jawabin nasa ya kuma tabo ci gaban da aka samu a bangarorin tattalin arziki da fasahohi da kirkire kirkire, amma na mayar da hankali ne kan yanayin zaman takewar jama’a da irin ci gaban da suke samu, saboda yadda hakan ke ja hankalina matuka, kuma saboda ina kwadayin ganin an samu irin hakan a kasata da sauran sassan duniya. Duk wani yunkuri ko manufa da kasa za ta aiwatar, ba za su taba yin tasiri ba idan babu jama’a. Haka ma, duk burin samun ci gaban da take da shi, ba za ta iya cimmawa ba, muddun al’ummarta na cikin  kuncin rayuwa ko rikici da juna.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

A matsayin wadda ta shaida yanayin rayuwar Sinawa, tabbas zan iya cewa ci gaban kasar ya samo asali ne daga yadda ta mayar da hankali kan raya jama’arta da kyautata rayuwarsu da tabbatar da daidaito da girmama juna tsakanin mabanbantan kabilu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ci GabafasahohiKasakirkire-kirkireKishin KasaTattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ana Kokarin Rantsar Da ‘Yan APC 16 A Majalisar Filato Ta Barauniyar Hanya – Gwamnatin Jihar

Next Post

Alkaluman Sun Shaida Cewa Dole A Fahimci Ci Gaba Yayin Da Ake Kokarin Samar Da Shi

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

13 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

13 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

15 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

18 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

20 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

21 hours ago
Next Post
Alkaluman Sun Shaida Cewa Dole A Fahimci Ci Gaba Yayin Da Ake Kokarin Samar Da Shi

Alkaluman Sun Shaida Cewa Dole A Fahimci Ci Gaba Yayin Da Ake Kokarin Samar Da Shi

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.