ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Alkaluman Sun Shaida Cewa Dole A Fahimci Ci Gaba Yayin Da Ake Kokarin Samar Da Shi

by CGTN Hausa
2 years ago
ci gaba

Yawan GDPn kasar Sin cikin kason yawan GDPn kasar Amurka, ya dade yana zama muhimmin batun da jama’a ke tattaunawa, musamman tun bayan da ita Sin din ta zama kasa mafi karfin tattalin arziki ta biyu a duniya. A shekara ta 2023, wannan adadi ya ragu. To, da aka gano wannan sauyi, tare kuma da yin la’akari da yadda Amurka take yi wa kasar Sin kangiya da danniya, mutane da yawa na ganin cewa, shin tattalin arzikin kasar Sin zai tawaya?

Amma wannan gaskiya ce?

Bari mu duba wannan adadi, wato kidayar yawan GDP na wata kasa, wanda ya shafi fannoni daban-daban, ciki har da farashin kayan masarufi da darajar kudi da sauransu. A shekaru ukun da suka gabata, Amurka ta gabatar da wasu tsauraran manufofin hada-hadar kudi, al’amarin da ya janyo mummunar matsalar hauhawar farashin kaya a kasar, kuma hakan ya habaka yawan GDPn kasar.

ADVERTISEMENT

Alal misali, a shekara ta 2022, yawan CPI da yawan PPI na kasar Amurka, sun karu da kaso 8 bisa dari, da kaso 16.5 bisa dari, yayin da yawan CPI da yawan PPI na kasar Sin, suka karu da kaso 2 bisa dari, da kaso 4.1 bisa dari. Ke nan ana iya fahimtar irin “gibi” da aka samu, yayin da aka kidaya su.

  • Labaran Karyar Cewa “Tattalin Arzikin Sin Na Dakushewa” Ba sa Tasiri A zukatan Jama’a 

Ban da farashin kaya, yayin da ake kwatanta yawan GDPn kasashe daban-daban, a kan kuma yi la’akari da darajar kudin musanya. Wato idan ana son kwatanta yawan GDPn Sin da na Amurka, ya kamata a sauya yawan GDPn kasar Sin da aka kidaya da kudin kasar wato Yuan, zuwa dalar Amurka. Tun daga shekaru biyu da suka wuce, Amurka ta fara sabon zagayen kara kudin ruwa, inda tun daga watan Maris din shekara ta 2022 zuwa watan Yulin shekara ta 2023, har sau 11 ne babban bankin Amurka ya kara kudin ruwa. Kuma hakan ya kan kara darajar kudin musanya na dala. A sabili da haka, darajar kudin musanya, ita ma ta fadada irin wannan “gibin” dake tsakanin yawan GDPn Sin da Amurka.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Muna da yakinin sosai game da bunkasar tattalin arzikin kasar Sin, ba don kwatantawa da na sauran kasashe ba. Mun san cewa, ya kamata tattalin arzikin kasar Sin ya shawo kan wahalhalu da kalubaloli da dama, amma a wadannan shekaru, kasar ta samu ci gaba sosai a yayin da take kokarin shawo kan matsaloli iri-iri. Haye wahalhalu, da shawo kan matsaloli, shi ne abun dake karfafa gwiwarmu ga bunkasar tattalin arzikin kasar Sin. (Murtala Zhang)

 

 

ci gaba
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
EFCC Ta Cafke Motoci 21 Makare Da Abincin Da Aka Yi Fasa-kwauri Zuwa Kasashe Makwabta

EFCC Ta Cafke Motoci 21 Makare Da Abincin Da Aka Yi Fasa-kwauri Zuwa Kasashe Makwabta

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.