ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Kyautatawa Al’umma Ita Ce Kashin Bayan Ci Gaban Ko Wacce Kasa

by CGTN Hausa
2 years ago
al'umma

A yau Talata ne aka bude taron shekara-shekara na majalisar wakilan jama’ar Kasar Sin, inda firaministan kasar, Li Qiang ya gabatar da rahoton aikin gwamnati a bara. Cikin rahoton ya bayyana cewa, “Gwamnati ta cimma nasarar samun ci gaba mai inganci, da tabbatar da zaman lafiyar al’umma, lamarin da ya sa aka sami gagarumin ci gaba a fannin gina zamantakewar al’umma ta zamani bisa tsarin gurguzu a dukkanin fannoni.”

Dukkan ci gaban kasar Sin baya rasa nasaba da irin tsarin shugabancin da ta zabarwa kanta. Tsarin gurguzu mai sigar musamman ta kasar Sin, shi ne tushe kuma sirrin ci gaban kasar. Sin ta yi abun da ba kasafai a kan gani ba, wato ta duba yanayinta, ta kuma fadawa kan ta gaskiya, inda ta rika aiwatar da manufofi da dabarun da suka dace da yanayinta, maimakon zama ’yar a bi Yarima a sha kida.

  • Xi Jinping Ya Halarci Taron Tattaunawa A Yayin Taron Majalisar Wakilan Jama’ar Kasar Sin

Na saba da jin ana cewa, “in dambu ya yi yawa baya jin mai” wato idan mutane suka yi yawa, to da wuya kowa ya ci gajiyar wata manufa ko shirin kyautatawa al’umma. Sai dai, zan iya cewa, duk da dimbin jama’a da kasar Sin take da shi, ba na jin ana irin wannan furuci, har kullum manufofin kasar kan isa ga wadanda aka yi domin su.

ADVERTISEMENT

Wani batu shi ne, Kishin Kasa. Ana yawaita samun rikicin addini ko kabilanci a cikin gidan kasashen duniya da dama, amma duk da yawan kabilu da addinai dake a kasar Sin, ba ka jin tashin irin wadannan rigingimu. Abun da na lura da shi da al’ummar kasar shi ne, duk da cewa akwai kabilu daban daban, tuna cewa kai Basine ne, shi ne abu na farko kuma mafi muhimmanci kafin komai. Wato an dasawa Sinawa kishin kasa da kaunar kasa kafin komai, wanda ya zama tushen zaman lafiya da zaman jituwa da hakuri da juna da ake samu tsakanin al’ummun kasar daga mabambantan kabilu.

Jawabin nasa ya kuma tabo ci gaban da aka samu a bangarorin tattalin arziki da fasahohi da kirkire kirkire, amma na mayar da hankali ne kan yanayin zaman takewar jama’a da irin ci gaban da suke samu, saboda yadda hakan ke ja hankalina matuka, kuma saboda ina kwadayin ganin an samu irin hakan a kasata da sauran sassan duniya. Duk wani yunkuri ko manufa da kasa za ta aiwatar, ba za su taba yin tasiri ba idan babu jama’a. Haka ma, duk burin samun ci gaban da take da shi, ba za ta iya cimmawa ba, muddun al’ummarta na cikin  kuncin rayuwa ko rikici da juna.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

A matsayin wadda ta shaida yanayin rayuwar Sinawa, tabbas zan iya cewa ci gaban kasar ya samo asali ne daga yadda ta mayar da hankali kan raya jama’arta da kyautata rayuwarsu da tabbatar da daidaito da girmama juna tsakanin mabanbantan kabilu.

al'umma
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

MASU ALAKA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa
Daga Birnin Sin

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Next Post
Alkaluman Sun Shaida Cewa Dole A Fahimci Ci Gaba Yayin Da Ake Kokarin Samar Da Shi

Alkaluman Sun Shaida Cewa Dole A Fahimci Ci Gaba Yayin Da Ake Kokarin Samar Da Shi

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

Kotu Ta Yanke Wa Wani Hukuncin Ɗaurin Shekara 7 Kan Tallan Wiwi A Kafafen Sada Zumunta

July 16, 2026
Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.