Mayaƙan ƙungiyar Lakurawa sun shiga garuruwa fiye da 10 a ƙaramar hukumar Augie ta Jihar Kebbi, inda suka gargaɗi jama’a da ka da su ƙara sayar da shanunsu don siyan injinan huɗa da ke amfani da fetur.
Sun ce duk wanda ya sayar da shanunsa zai iya baƙuntar lahira.
- Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Sin Sun Samar Da Sabuwar Hanyar Sufuri Ga Al’Ummun Kasashen Shiyyar Tsakiyar Asiya
- Wasu ‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Gidan Sanata Natasha A Kogi
Manoma da dama suna sayar da dabbobinsu ne don su kare kansu daga sace-sacen da ‘yan bindiga ke yi, amma yanzu sun shiga tsaka mai wuya bayan wannan barazana.
Wani mazaunin yankin ya shaida cewa suna sayar da shanun ne domin su sayi motar noman shinkafa, amma yanzu ba su da zaɓin da ya fi su bi umarnin ‘yan bindigar, saboda gwamnati ma ta gaza kare su.
“Idan suka shigo gari a kan mashin, uku ne a kan kowanne, bindiga a hannu, kuma sukan kwashe dabbobi har da kaji, mutum kuma baya iya cewa uffan,” in ji wani da ya nemi a ɓoye sunansa.
Yanzu haka fargaba ta karaɗe yankin, yayin da jama’a ke roƙon gwamnati da hukumomin tsaro su tashi tsaye domin kawo ƙarshen wannan matsala da ta dabaibaye rayuwarsu da amfanin gonarsu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp