• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lalong Ya Yi Allah-wadai Da Kashe-kashen Da Aka Yi A Filato, Ya Bukaci A Gurfanar Da Masu Laifin

bySadiq
3 years ago
Filato

Gwamna Simon Lalong na Jihar Filato, ya yi Allah-wadai da harin da aka kai a daren ranar Talata a unguwar Maikatako da ke gundumar Butura ta karamar hukumar Bokkos, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane 11 tare da jikkata wasu mutane takwas.

A wata sanarwa da Daraktan yada labarai da hulda da jama’a na Jihar, Makut Machan ya fitar, Lalong ya bukaci jami’an tsaro a jihar da su kamo wadanda suka aikata wannan aika-aika domin gurfanar da su a gaban kuliya.

  • Sin Za Ta Kara Raya Sana’o’in Dake Shafar Kasuwar Sinadarin Carbon
  • Dakarun Soji A Jihar Kaduna Sun Kara Kashe Wani Jagoran ‘Yan Bindiga Gudau Kachalla

Gwamnan wanda ya jajantawa iyalan wadanda harin ya rutsa da su, ya nanata cewa gwamnatinsa ba za ta bari ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga su kai hari a wani yanki na jihar ba saboda an umarci dukkanin hukumomin tsaro da su tabbatar da ta yi maganin duk wani mutum ko kungiyar da ta kai harin. .

A cewarsa, yawaitar hare-hare da lalata amfanin gonaki, dabbobi, da sauran dukiyoyi a karamar hukumar ta Bokkos, na zama abin damuwa, kuma dole ne a duba su cikin gaggawa.

Wasu da ake zargin makiyaya ne sun afkawa al’ummar yankin da misalin karfe 11 na daren ranar Talata, inda suka kona gidaje hudu a harin, sannan suka fara harbi ba kakkautawa bayan da suka mamaye ‘yan banga da ke sintiri.

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

An ce guda tara daga cikin wadanda abin ya shafa an kona su ne ta yadda ba za a iya gane su ba a wani waje, yayin da sauran kuma aka same su da sanyin safiyar Laraba a gidajensu da suka kone bayan an harbe su.

Wani dan unguwar ya tuna cewa harin ba gaira ba dalili ya fara ne bayan ranar kasuwar Litinin ta mako-mako inda aka harbe wani yaro a Hilltop, wanda ke da tazarar kilomita daga Maikatako.

Rahotanni sun ce lamarin harbin ya haifar da tashin hankali a tsakanin al’ummar a ranar Talata duk da cewa ‘yan banga sun yi kokarin fatattakar maharan.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Filato, Alfred Alabo, ya ce har yanzu bai samu cikakken bayanin lamarin ba.

Sai dai kwamandan rundunar ‘Operation Safe Haven’ Manjo-Janar Ibrahim Ali, ya bayyana cewa rundunar tsaron da aka bai wa alhakin kula da al’amuran tsaro a Filato, da kuma wasu sassan jihohin Bauchi da Kaduna, sun kasance a kasa don shirin ko ta kwana.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
Duk Bayan Shekaru 8 Ya Kamata Ake Sauya Fasalin Naira – Shugaban EFCC

Duk Bayan Shekaru 8 Ya Kamata Ake Sauya Fasalin Naira - Shugaban EFCC

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version