• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lamunin Naira Biliyan 5 Ga ‘Yan Fim: Yaushe Kannywood Za Ta Samu Nata?

by Sulaiman and Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
in Nishadi
0
kannywood
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A tsakiyar makon da ya gabata ne aka samu labarin cewa gwamnatin tarayya ta bayar da karin wani kaso daga tallafin naira biliyan 5 ga masana’antar Nollywood, wanda labarin ya karade kafofin yada labarai a kasar nan.

Gwamnatin tarayyar ta ce wannan shi ne rukuni na biyu da ta bayar da irin wannan tallafi ga masana’antar Nollywood da ke shirya fina-finai da harshen Turanci a Nijeriya.

  • Biyan Sabon Haraji: Gwamnati Ta Tsame Kananan Kamfanoni Da Manoma
  • Ma’aikatan Ruwa Na Jihar Kaduna Sun Yi Zanga-zangar Rashin Albashi

Gwamnatin tarayya tare da hadin gwiwar bankin Probidus sun bayar da kaso na biyu na kudaden da aka ware domin bunkasa harkokin masana’antun nishadi a Nijeriya, wanda kudin ya kai naira biliyan 5. An kafa wannan asusu ne a watan Disambar 2023, domin tallafawa da kuma bunkasa fannin kirkire-kirkire a Nijeriya.

Mataimaki na musamman ga ofishin mataimakin shugaban kasa kan fasahar tattalin arzikin zamani, Fegho Umunubo, ya sanar da labarin a cikin wani sakonsa a kafar sada zumanta ta ‘Instagram’ da ya wallafa.
Ya ce karkashin sabon tsarin sabunta fata na Shugaba kasa, Bola Ahmed Tinubu, “Mun yi nasarar kaddamar da kashi na biyu na susun tallafa wa masana’antar kirkire-kirkire ta Nijeriya da naira biliyan 5 tare da hadin gwiwar bankin Probidus da kuma otel din Eko Hotels and Suites a ranar Juma’ar da ta gabata.

“Bayan nasarar raba naira biliyan 1.5 ga ’yan wasa hudu da masu shirya fina-finai a masana’antar Nollywood, har yanzu kofa a bude take ga duk masu bukatar tallafi domin bunkasa harkokinsu na nishadi da kirkire-kirkire,” ya rubuta.

Labarai Masu Nasaba

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

A watan Mayu na wannan shekarar aka raba kason farko na naira biliyan 1.5 ga jarumai da masu shirya fina-finai hudu.

Sai dai Fegho ya ce kudaden ba kyauta ba ne, domin ana sa ran wadanda suka amfana za su mayar da kashi 30 cikin 100 na kudaden da suka samu zuwa bankin Probidus a dan kankanin lokaci.

Hakan ya sa mutane da dama suke sha’awar ganin takwarar masana’antar Nollywood, wadda take shirya fina-finanta da harshen Hausa wato Kannywood ita ma ta samu kwatankwacin irin wannan tallafin, duba da cewa a lokuta da dama kamar dai Nollywood ita ma masana’antar Kannywood takan rasa wasu kudaden da za ta gudanar da wani abu wanda zai janyo mata ci gaba ya kuma daukaka sunan Nijeriya a idon duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ali NuhuKannywoodNishadi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mataimakin Shugaban Sin Ya Yi Jawabi A Dandalin Tattaunawar Zaman Lafiyar Duniya Karo Na 12

Next Post

Kasar Ingila Ta Tsallaka Zuwa Matakin Semi Final A Gasar EURO Ta 2024

Related

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan
Nishadi

Ina Fatan Watsi Da Harkar Fim Nan Gaba —Umar Hassan

2 days ago
Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango
Nishadi

Ban Taɓa Nadamar Shiga Fim Ba – Kabiru Nakwango

4 days ago
Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)
Nishadi

Duk Wanda Ya Girme Ni Ubangidana Ne A Harkar Fim – Hauwa Garba (2)

1 week ago
Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba
Nishadi

Masana’antar Kannywood Na Tsananin Buqatar Addu’a – Hauwa Garba

2 weeks ago
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah
Nishadi

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

3 weeks ago
Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

1 month ago
Next Post
Kasar Ingila Ta Tsallaka Zuwa Matakin Semi Final A Gasar EURO Ta 2024

Kasar Ingila Ta Tsallaka Zuwa Matakin Semi Final A Gasar EURO Ta 2024

LABARAI MASU NASABA

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.