• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lamunin Naira Biliyan 5 Ga ‘Yan Fim: Yaushe Kannywood Za Ta Samu Nata?

by Sulaiman and Rabilu Sanusi Bena
1 year ago
in Nishadi
0
kannywood
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A tsakiyar makon da ya gabata ne aka samu labarin cewa gwamnatin tarayya ta bayar da karin wani kaso daga tallafin naira biliyan 5 ga masana’antar Nollywood, wanda labarin ya karade kafofin yada labarai a kasar nan.

Gwamnatin tarayyar ta ce wannan shi ne rukuni na biyu da ta bayar da irin wannan tallafi ga masana’antar Nollywood da ke shirya fina-finai da harshen Turanci a Nijeriya.

  • Biyan Sabon Haraji: Gwamnati Ta Tsame Kananan Kamfanoni Da Manoma
  • Ma’aikatan Ruwa Na Jihar Kaduna Sun Yi Zanga-zangar Rashin Albashi

Gwamnatin tarayya tare da hadin gwiwar bankin Probidus sun bayar da kaso na biyu na kudaden da aka ware domin bunkasa harkokin masana’antun nishadi a Nijeriya, wanda kudin ya kai naira biliyan 5. An kafa wannan asusu ne a watan Disambar 2023, domin tallafawa da kuma bunkasa fannin kirkire-kirkire a Nijeriya.

Mataimaki na musamman ga ofishin mataimakin shugaban kasa kan fasahar tattalin arzikin zamani, Fegho Umunubo, ya sanar da labarin a cikin wani sakonsa a kafar sada zumanta ta ‘Instagram’ da ya wallafa.
Ya ce karkashin sabon tsarin sabunta fata na Shugaba kasa, Bola Ahmed Tinubu, “Mun yi nasarar kaddamar da kashi na biyu na susun tallafa wa masana’antar kirkire-kirkire ta Nijeriya da naira biliyan 5 tare da hadin gwiwar bankin Probidus da kuma otel din Eko Hotels and Suites a ranar Juma’ar da ta gabata.

“Bayan nasarar raba naira biliyan 1.5 ga ’yan wasa hudu da masu shirya fina-finai a masana’antar Nollywood, har yanzu kofa a bude take ga duk masu bukatar tallafi domin bunkasa harkokinsu na nishadi da kirkire-kirkire,” ya rubuta.

Labarai Masu Nasaba

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

A watan Mayu na wannan shekarar aka raba kason farko na naira biliyan 1.5 ga jarumai da masu shirya fina-finai hudu.

Sai dai Fegho ya ce kudaden ba kyauta ba ne, domin ana sa ran wadanda suka amfana za su mayar da kashi 30 cikin 100 na kudaden da suka samu zuwa bankin Probidus a dan kankanin lokaci.

Hakan ya sa mutane da dama suke sha’awar ganin takwarar masana’antar Nollywood, wadda take shirya fina-finanta da harshen Hausa wato Kannywood ita ma ta samu kwatankwacin irin wannan tallafin, duba da cewa a lokuta da dama kamar dai Nollywood ita ma masana’antar Kannywood takan rasa wasu kudaden da za ta gudanar da wani abu wanda zai janyo mata ci gaba ya kuma daukaka sunan Nijeriya a idon duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ali NuhuKannywoodNishadi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mataimakin Shugaban Sin Ya Yi Jawabi A Dandalin Tattaunawar Zaman Lafiyar Duniya Karo Na 12

Next Post

Kasar Ingila Ta Tsallaka Zuwa Matakin Semi Final A Gasar EURO Ta 2024

Related

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya
Nishadi

Na Hadu Da Azzalumai Da Mayaudara Farkon Shigata Kannywood – Dan’duniya

7 days ago
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
Nishadi

Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu

2 weeks ago
Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya
Nishadi

Na Yi Lokacin Da Idan Aka Gan Ni Ake Gudu A Masana’antar Kannywood – Mai Dawayya

2 weeks ago
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna
Nishadi

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

2 weeks ago
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ
Nishadi

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

3 weeks ago
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami
Nishadi

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

3 weeks ago
Next Post
Kasar Ingila Ta Tsallaka Zuwa Matakin Semi Final A Gasar EURO Ta 2024

Kasar Ingila Ta Tsallaka Zuwa Matakin Semi Final A Gasar EURO Ta 2024

LABARAI MASU NASABA

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

August 23, 2025
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

August 23, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

August 23, 2025
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

August 23, 2025
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.