• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lamunin Naira Biliyan 5 Ga ‘Yan Fim: Yaushe Kannywood Za Ta Samu Nata?

by Sulaiman and Rabilu Sanusi Bena
11 months ago
in Nishadi
0
kannywood
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A tsakiyar makon da ya gabata ne aka samu labarin cewa gwamnatin tarayya ta bayar da karin wani kaso daga tallafin naira biliyan 5 ga masana’antar Nollywood, wanda labarin ya karade kafofin yada labarai a kasar nan.

Gwamnatin tarayyar ta ce wannan shi ne rukuni na biyu da ta bayar da irin wannan tallafi ga masana’antar Nollywood da ke shirya fina-finai da harshen Turanci a Nijeriya.

  • Biyan Sabon Haraji: Gwamnati Ta Tsame Kananan Kamfanoni Da Manoma
  • Ma’aikatan Ruwa Na Jihar Kaduna Sun Yi Zanga-zangar Rashin Albashi

Gwamnatin tarayya tare da hadin gwiwar bankin Probidus sun bayar da kaso na biyu na kudaden da aka ware domin bunkasa harkokin masana’antun nishadi a Nijeriya, wanda kudin ya kai naira biliyan 5. An kafa wannan asusu ne a watan Disambar 2023, domin tallafawa da kuma bunkasa fannin kirkire-kirkire a Nijeriya.

Mataimaki na musamman ga ofishin mataimakin shugaban kasa kan fasahar tattalin arzikin zamani, Fegho Umunubo, ya sanar da labarin a cikin wani sakonsa a kafar sada zumanta ta ‘Instagram’ da ya wallafa.
Ya ce karkashin sabon tsarin sabunta fata na Shugaba kasa, Bola Ahmed Tinubu, “Mun yi nasarar kaddamar da kashi na biyu na susun tallafa wa masana’antar kirkire-kirkire ta Nijeriya da naira biliyan 5 tare da hadin gwiwar bankin Probidus da kuma otel din Eko Hotels and Suites a ranar Juma’ar da ta gabata.

“Bayan nasarar raba naira biliyan 1.5 ga ’yan wasa hudu da masu shirya fina-finai a masana’antar Nollywood, har yanzu kofa a bude take ga duk masu bukatar tallafi domin bunkasa harkokinsu na nishadi da kirkire-kirkire,” ya rubuta.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

A watan Mayu na wannan shekarar aka raba kason farko na naira biliyan 1.5 ga jarumai da masu shirya fina-finai hudu.

Sai dai Fegho ya ce kudaden ba kyauta ba ne, domin ana sa ran wadanda suka amfana za su mayar da kashi 30 cikin 100 na kudaden da suka samu zuwa bankin Probidus a dan kankanin lokaci.

Hakan ya sa mutane da dama suke sha’awar ganin takwarar masana’antar Nollywood, wadda take shirya fina-finanta da harshen Hausa wato Kannywood ita ma ta samu kwatankwacin irin wannan tallafin, duba da cewa a lokuta da dama kamar dai Nollywood ita ma masana’antar Kannywood takan rasa wasu kudaden da za ta gudanar da wani abu wanda zai janyo mata ci gaba ya kuma daukaka sunan Nijeriya a idon duniya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Ali NuhuKannywoodNishadi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mataimakin Shugaban Sin Ya Yi Jawabi A Dandalin Tattaunawar Zaman Lafiyar Duniya Karo Na 12

Next Post

Kasar Ingila Ta Tsallaka Zuwa Matakin Semi Final A Gasar EURO Ta 2024

Related

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu
Nishadi

Yadda Jarumai A Masana’antar Kannywood Ke Auren Junansu

3 days ago
Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 
Nishadi

Ban Dauki Harkar Fim Da Wasa Ba -Hauwa Ayawa 

2 weeks ago
Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
Nishadi

Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani

2 weeks ago
Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa
Nishadi

Ban Ɗauki Harkar Fim Da Wasa Ba – Hauwa Ayawa

2 weeks ago
Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro
Nishadi

Har Yanzu Da Bazar Mahaifina Nake Rawa -Hanafi Ibro

3 weeks ago
Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage
Nishadi

Rashin Hadin Kai Ke Dakile Ci Gaban Masana’antar Kannywood -Ayatullahi Tage

3 weeks ago
Next Post
Kasar Ingila Ta Tsallaka Zuwa Matakin Semi Final A Gasar EURO Ta 2024

Kasar Ingila Ta Tsallaka Zuwa Matakin Semi Final A Gasar EURO Ta 2024

LABARAI MASU NASABA

DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Yanzu-yanzu: Gwamnatin Neja Ta Soke Hawan Sallah Sakamakon Ambaliyar Ruwan Mokwa

June 4, 2025
katsina

Gwamnan Katsina Ya Bukaci Hadin Gwiwa Da ‘Yan Kasuwa Domin Cigaban Jihar

June 4, 2025
Ambaliya: Gwamna Zulum Ya Kaddamar Da Rabon Kayan Agaji A Borno

Zulum Ya Yaba Wa Sojoji Kan Kashe Babban Kwamandan ISWAP Abu Fatima

June 4, 2025
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.