• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lauyoyi Mata Sun Koka Kan Cin Zarafin Da Alkalai Maza Ke Yi Musu A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
1 year ago
in Labarai
0
Lauyoyi Mata Sun Koka Kan Cin Zarafin Da Alkalai Maza Ke Yi Musu A Adamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar lauyoyi Mata ta kasa (NBA) reshen jihar Adamawa, ta koka da halayyar wasu alkalai da jami’an ma’aikatan kotu a jihar kan cin zarafin mambobin kungiyar.

Duk da dai matan ba su fadi irin cin zarafin da mazan alkalan ke musu ba, amma tuni kungiyar ta kai kara ga babbar alkalin alkalai ta jihar , Mai shari’a Hafsat Abdulrahaman, ta kuma bukaci Mai shari’ar da ta gudanar da bincike kan lamarin tare da gurfanar da wadanda aka samu da laifi.

  • PCRC Ta Zabi Sabbin Shugabanni A Adamawa
  • Gwamna Fintiri Ya Maka Dakataccen Kwamishinan INEC Na Adamawa, Hudu Ari A Kotu

Barista Fatima Raji Bello, ita ce shugabar Kungiyar Mata Lauyoyi ta Jihar, ta bayyana haka lokacin da su ka kai ziyarar goyon baya ga babbar mai shari’ar, Hafsat Abdulrrahaman, domin tunawa da ranar mata ta duniya a jihar.

Ta ce tuni “Kungiyar ta gabatar da koken cin zarafin da wasu alkalai mazan da jami’an kotuna ga ofsin babbar mai shari’ar.

“Muna kuma bukatar da ku binciki zargin domin ku hukunta duk wadanda ke da hannu a ciki, Muna kira da a horar da dukkan ma’aikatan shari’a kan keta ka’idojin lalata da cin zarafin mata” inji Raji.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

Haka kuma shugabar kungiyar ta shaidawa Mai shari’a Hafsat, cewa sun kuma kawo mata ziyarar ne domin jin ta bakinta game da ayyukan da su ka fara a shekarar 2022, sannan ta bukace ta a matsayin uwar Lauya da Bench da su shiga kungiyar ta NBA domin ba su horo da matasa da masu neman zama lauyoyi mata a harkar sana’a a jihar.

Ta kuma yi amfani da ziyarar wajen yabawa babban mai shari’a, Hafsat AbdulRahman da kwamishinan shari’a da kuma babban lauyan gwamnatin jihar, Barista Jingi Afraimu, da ya dauki nauyin lauyoyi 14 domin halartar taro na 2, 3 da 4 na kungiyar matan NBA da aka gudanar a jihar Legas da Abuja.

Da take mayar da martani, babbar mai shari’a, Hafsat Abdulrahaman, ta bayar da hakuri ga duk wani nau’in cin zarafin da alkalai ke yi wa mata lauyoyin, sannan ta yi alkawarin tabbatar da gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

Ta kuma nuna jin dadi da yadda mata ke samun gagarumin tasiri a kowane fanni na al’amura da sana’o’in da su ka sa a gaba, ta kuma yaba wa alkalai mata musamman wajen yin tasiri sosai kan hukunce-hukunce, tare da bayyana kyakkyawan fata na cewa dandalin Mata lauyoyin zai iya yin abin da ya dace wajen tallafa wa juna.

Mai shari’ar ta kuma yaba tare da godewa shugabanni da mambobin kungiyar bisa wannan ziyara, inda ta bukace su da su kara himma domin aikin lauya ya na bukatar a kula da da’a, kwazon, aiki tukuru da kuma tsafta da ado.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdamawaLauyoyi MataMata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ramadan: Sanata Yari Ya Buƙaci Musulmi Da Su Yi Wa Shugaba Tinubu Addu’a

Next Post

Da Azumi A Bakina Lokacin Da Na Zurawa Liverpool Kwallon Karshe -Amad Diallo

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

6 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

7 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

8 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

9 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

10 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

13 hours ago
Next Post
Da Azumi A Bakina Lokacin Da Na Zurawa Liverpool Kwallon Karshe -Amad Diallo

Da Azumi A Bakina Lokacin Da Na Zurawa Liverpool Kwallon Karshe -Amad Diallo

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.