• English
  • Business News
Wednesday, July 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lauyoyi Mata Sun Koka Kan Cin Zarafin Da Alkalai Maza Ke Yi Musu A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
1 year ago
in Labarai
0
Lauyoyi Mata Sun Koka Kan Cin Zarafin Da Alkalai Maza Ke Yi Musu A Adamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar lauyoyi Mata ta kasa (NBA) reshen jihar Adamawa, ta koka da halayyar wasu alkalai da jami’an ma’aikatan kotu a jihar kan cin zarafin mambobin kungiyar.

Duk da dai matan ba su fadi irin cin zarafin da mazan alkalan ke musu ba, amma tuni kungiyar ta kai kara ga babbar alkalin alkalai ta jihar , Mai shari’a Hafsat Abdulrahaman, ta kuma bukaci Mai shari’ar da ta gudanar da bincike kan lamarin tare da gurfanar da wadanda aka samu da laifi.

  • PCRC Ta Zabi Sabbin Shugabanni A Adamawa
  • Gwamna Fintiri Ya Maka Dakataccen Kwamishinan INEC Na Adamawa, Hudu Ari A Kotu

Barista Fatima Raji Bello, ita ce shugabar Kungiyar Mata Lauyoyi ta Jihar, ta bayyana haka lokacin da su ka kai ziyarar goyon baya ga babbar mai shari’ar, Hafsat Abdulrrahaman, domin tunawa da ranar mata ta duniya a jihar.

Ta ce tuni “Kungiyar ta gabatar da koken cin zarafin da wasu alkalai mazan da jami’an kotuna ga ofsin babbar mai shari’ar.

“Muna kuma bukatar da ku binciki zargin domin ku hukunta duk wadanda ke da hannu a ciki, Muna kira da a horar da dukkan ma’aikatan shari’a kan keta ka’idojin lalata da cin zarafin mata” inji Raji.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

Haka kuma shugabar kungiyar ta shaidawa Mai shari’a Hafsat, cewa sun kuma kawo mata ziyarar ne domin jin ta bakinta game da ayyukan da su ka fara a shekarar 2022, sannan ta bukace ta a matsayin uwar Lauya da Bench da su shiga kungiyar ta NBA domin ba su horo da matasa da masu neman zama lauyoyi mata a harkar sana’a a jihar.

Ta kuma yi amfani da ziyarar wajen yabawa babban mai shari’a, Hafsat AbdulRahman da kwamishinan shari’a da kuma babban lauyan gwamnatin jihar, Barista Jingi Afraimu, da ya dauki nauyin lauyoyi 14 domin halartar taro na 2, 3 da 4 na kungiyar matan NBA da aka gudanar a jihar Legas da Abuja.

Da take mayar da martani, babbar mai shari’a, Hafsat Abdulrahaman, ta bayar da hakuri ga duk wani nau’in cin zarafin da alkalai ke yi wa mata lauyoyin, sannan ta yi alkawarin tabbatar da gudanar da cikakken bincike kan lamarin.

Ta kuma nuna jin dadi da yadda mata ke samun gagarumin tasiri a kowane fanni na al’amura da sana’o’in da su ka sa a gaba, ta kuma yaba wa alkalai mata musamman wajen yin tasiri sosai kan hukunce-hukunce, tare da bayyana kyakkyawan fata na cewa dandalin Mata lauyoyin zai iya yin abin da ya dace wajen tallafa wa juna.

Mai shari’ar ta kuma yaba tare da godewa shugabanni da mambobin kungiyar bisa wannan ziyara, inda ta bukace su da su kara himma domin aikin lauya ya na bukatar a kula da da’a, kwazon, aiki tukuru da kuma tsafta da ado.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdamawaLauyoyi MataMata
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ramadan: Sanata Yari Ya Buƙaci Musulmi Da Su Yi Wa Shugaba Tinubu Addu’a

Next Post

Da Azumi A Bakina Lokacin Da Na Zurawa Liverpool Kwallon Karshe -Amad Diallo

Related

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

18 minutes ago
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara
Manyan Labarai

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

3 hours ago
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

13 hours ago
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang
Labarai

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

14 hours ago
Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu
Labarai

Matashi Ya Kashe Surukarsa Saboda Shigarta Cikin Sha’anin Aurensu

16 hours ago
Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara
Labarai

Birtaniya Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Mutane 33 A Zamfara

17 hours ago
Next Post
Da Azumi A Bakina Lokacin Da Na Zurawa Liverpool Kwallon Karshe -Amad Diallo

Da Azumi A Bakina Lokacin Da Na Zurawa Liverpool Kwallon Karshe -Amad Diallo

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

July 30, 2025
Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

July 30, 2025
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

July 30, 2025
Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

Sin Da Benin Da Thailand Za Su Aiwatar Da Matakan Saukaka Tantance Kaya Na Kwastam

July 29, 2025
Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana

July 29, 2025
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

July 29, 2025
Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

Sojojin Sin Sun Bi Sahun Shiga Ayyukan Ba Da Agajin Ambaliyar Ruwa

July 29, 2025
Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

Babu Wata Karamar Hukumar Da Ke Ƙarƙashin Ikon Ƴan Ta’adda A Filato -Gwamna Mutfwang

July 29, 2025
Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa

July 29, 2025
Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

Morocco Ta Shigar Da Ƙara Kan Nasarar Super Falcons A Gasar WAFCON

July 29, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.