• English
  • Business News
Friday, August 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

by Khalid Idris Doya
4 hours ago
in Labarai
0
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wani dan kasar Tanzania da ya je asibiti da korafin diwa na yawan fita daga cikin nononsa na dama, ya shiga cikin dimuwa da gigicewa yayin da ya fahimci yana rayuwa da wani katon wuka a cikin kirjinsa ba tare da ya sani ba na tsawon shekaru har takwas, kafar yada labarai ta kasar ce ta rawaito. 

Likitoci a babban asibitin Muhimbili da ke Tanzania a baya-bayan nan suka wallafa rahoton wani jinya wanda ba a saba samun irinsa ba, wanda ya zo da ban mamaki matuka.

  • EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
  • Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sun rubuta cewa, wani mutum dan shekara 44 a duniya da ke cikin rayuwa da koshin lafiyarsa, ya kawo musu korafin cewa cikin kwanaki goma yana ganin farin ruwan diwa na fita daga nononsa na dama.

Sai dai ya ce shi baya jin wani zafi a cikin kirjinsa, ko wahalar jan numfashi, tari ko zazzabi, da aka tambaye shi ko yana da wani abu na daman da zai iya fada wa likitocin, sai ya tuna cewar a shekaru takwas da suka wuce sun taba yin fada, wanda a lokacin ya samu yanka (raunuka) a fuskantasa, kirji da kuma cikinsa.

Ya tabbatar da cewa tun a can lokacin likitoci sun dinke ramuka da raunukan da ya samu kuma ya ci gaba da rayuwarsa samul-garau, har sai lokacin da nononsa ya fara fitar da farin ruwa na diwa.

Labarai Masu Nasaba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

Bayan da likitocin suka kasa gane wacce irin cuta ce take janyo masa wannan fitar da diwan, likitocin sun umarci a je a dauki hoton kirjinsa, inda a nan ne suka gano katoton wukan da aka burma a cikin mutumin.

Likitocin sun rubuta cikin rahoton binciken nasu cewa hoton farko da aka dauka ya nuna zanen wani abu da ke kwance cikin kirjin mutumin, wanda daga bisani aka gano balo-balo wuka ne.

Sai dai sun gano cewa wukan tun lokacin da aka burma shi bai zaga ko lalata wasu sassan gabobin mutumin ba.

A lokacin da aka sanya masa wukar shekaru takwas da suka wuce, asibitin da suka masa dinkin, ba su ga wani alami ko dalilin da zai sanya su zurfafa bincike ba saboda bai musu korafin jin wani zafi ba, illa ya nuna garau yake ji, don haka a wancan lokacin babu bukatar zurfafa bincike, a cewar rahoton.

Sai dai rahoton ya nuna mamakin yadda mutumin dan shekara 44 ya ci gaba da rayuwarsa ba tare da wata matsala ba, duk kuwa da cewa diwan ya fito ne sakamakon matattun nama da suka kewaye jikin wukar.

Bayan gano wukar a kirjin mutumin, likitocin sun yi tiyata tare da ciro wukar da sauran naman da suka lalace da fitar da diwan baki daya.

Majinyacin ya kwashe awanni 24 a sashin kulawa ta musamman kafin daga bisani aka maida shi zuwa dakin jinya na tsawon kwanaki goma. Ya samu lafiya sosai ya kuma ci gaba da rayuwarsa ba tare da jin wani zafi ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Wuka
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

Next Post

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

Related

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba
Labarai

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

46 minutes ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

3 hours ago
Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina
Labarai

Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

5 hours ago
Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet
Labarai

Za A Yi Ruwan Sama Na Kwanaki 3 A Jere A Wasu Jihohin Nijeriya – NiMet

5 hours ago
An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato
Labarai

An Ceto Mutane 41, 4 Sun Rasu A Hatsarin Kwale-Kwale A Sakkwato

8 hours ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

10 hours ago
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Jagororin 'Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

LABARAI MASU NASABA

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

Manyan Jami’an JKS Sun Ziyarci Jami’ai Da Mazauna Birnin Lhasa

August 22, 2025
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

August 22, 2025
Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

August 22, 2025
Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

Jihar Xizang Ta Baiwa Duniya Mamaki Da “Canji Mai Girma” Da Ta Samu a Cikin Shekaru 60 Da Suka Gabata 

August 22, 2025
Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

Hukumar Kwastam Ta Kama Kayan Maye Na Miliyan 680 A Katsina

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.