ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

by Khalid Idris Doya
3 months ago
Wuka

Wani dan kasar Tanzania da ya je asibiti da korafin diwa na yawan fita daga cikin nononsa na dama, ya shiga cikin dimuwa da gigicewa yayin da ya fahimci yana rayuwa da wani katon wuka a cikin kirjinsa ba tare da ya sani ba na tsawon shekaru har takwas, kafar yada labarai ta kasar ce ta rawaito. 

Likitoci a babban asibitin Muhimbili da ke Tanzania a baya-bayan nan suka wallafa rahoton wani jinya wanda ba a saba samun irinsa ba, wanda ya zo da ban mamaki matuka.

  • EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
  • Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sun rubuta cewa, wani mutum dan shekara 44 a duniya da ke cikin rayuwa da koshin lafiyarsa, ya kawo musu korafin cewa cikin kwanaki goma yana ganin farin ruwan diwa na fita daga nononsa na dama.

ADVERTISEMENT

Sai dai ya ce shi baya jin wani zafi a cikin kirjinsa, ko wahalar jan numfashi, tari ko zazzabi, da aka tambaye shi ko yana da wani abu na daman da zai iya fada wa likitocin, sai ya tuna cewar a shekaru takwas da suka wuce sun taba yin fada, wanda a lokacin ya samu yanka (raunuka) a fuskantasa, kirji da kuma cikinsa.

Ya tabbatar da cewa tun a can lokacin likitoci sun dinke ramuka da raunukan da ya samu kuma ya ci gaba da rayuwarsa samul-garau, har sai lokacin da nononsa ya fara fitar da farin ruwa na diwa.

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Bayan da likitocin suka kasa gane wacce irin cuta ce take janyo masa wannan fitar da diwan, likitocin sun umarci a je a dauki hoton kirjinsa, inda a nan ne suka gano katoton wukan da aka burma a cikin mutumin.

Likitocin sun rubuta cikin rahoton binciken nasu cewa hoton farko da aka dauka ya nuna zanen wani abu da ke kwance cikin kirjin mutumin, wanda daga bisani aka gano balo-balo wuka ne.

Sai dai sun gano cewa wukan tun lokacin da aka burma shi bai zaga ko lalata wasu sassan gabobin mutumin ba.

A lokacin da aka sanya masa wukar shekaru takwas da suka wuce, asibitin da suka masa dinkin, ba su ga wani alami ko dalilin da zai sanya su zurfafa bincike ba saboda bai musu korafin jin wani zafi ba, illa ya nuna garau yake ji, don haka a wancan lokacin babu bukatar zurfafa bincike, a cewar rahoton.

Sai dai rahoton ya nuna mamakin yadda mutumin dan shekara 44 ya ci gaba da rayuwarsa ba tare da wata matsala ba, duk kuwa da cewa diwan ya fito ne sakamakon matattun nama da suka kewaye jikin wukar.

Bayan gano wukar a kirjin mutumin, likitocin sun yi tiyata tare da ciro wukar da sauran naman da suka lalace da fitar da diwan baki daya.

Majinyacin ya kwashe awanni 24 a sashin kulawa ta musamman kafin daga bisani aka maida shi zuwa dakin jinya na tsawon kwanaki goma. Ya samu lafiya sosai ya kuma ci gaba da rayuwarsa ba tare da jin wani zafi ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja
Manyan Labarai

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
Manyan Labarai

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Jagororin 'Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

LABARAI MASU NASABA

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

Laftanal Yarima Ya Tsallake Rijiya Da Baya A Abuja

November 16, 2025
Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

November 16, 2025
Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

Fasinjojin Da Kasar Sin Ta Yi Jigilarsu Ta Jirgin Kasa Daga Janairu Zuwa Oktoba Sun Kai Biliyan 3.95

November 16, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.