ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 20, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

by Khalid Idris Doya
10 months ago
Wuka

Wani dan kasar Tanzania da ya je asibiti da korafin diwa na yawan fita daga cikin nononsa na dama, ya shiga cikin dimuwa da gigicewa yayin da ya fahimci yana rayuwa da wani katon wuka a cikin kirjinsa ba tare da ya sani ba na tsawon shekaru har takwas, kafar yada labarai ta kasar ce ta rawaito. 

Likitoci a babban asibitin Muhimbili da ke Tanzania a baya-bayan nan suka wallafa rahoton wani jinya wanda ba a saba samun irinsa ba, wanda ya zo da ban mamaki matuka.

  • EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
  • Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sun rubuta cewa, wani mutum dan shekara 44 a duniya da ke cikin rayuwa da koshin lafiyarsa, ya kawo musu korafin cewa cikin kwanaki goma yana ganin farin ruwan diwa na fita daga nononsa na dama.

ADVERTISEMENT

Sai dai ya ce shi baya jin wani zafi a cikin kirjinsa, ko wahalar jan numfashi, tari ko zazzabi, da aka tambaye shi ko yana da wani abu na daman da zai iya fada wa likitocin, sai ya tuna cewar a shekaru takwas da suka wuce sun taba yin fada, wanda a lokacin ya samu yanka (raunuka) a fuskantasa, kirji da kuma cikinsa.

Ya tabbatar da cewa tun a can lokacin likitoci sun dinke ramuka da raunukan da ya samu kuma ya ci gaba da rayuwarsa samul-garau, har sai lokacin da nononsa ya fara fitar da farin ruwa na diwa.

LABARAI MASU NASABA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Bayan da likitocin suka kasa gane wacce irin cuta ce take janyo masa wannan fitar da diwan, likitocin sun umarci a je a dauki hoton kirjinsa, inda a nan ne suka gano katoton wukan da aka burma a cikin mutumin.

Likitocin sun rubuta cikin rahoton binciken nasu cewa hoton farko da aka dauka ya nuna zanen wani abu da ke kwance cikin kirjin mutumin, wanda daga bisani aka gano balo-balo wuka ne.

Sai dai sun gano cewa wukan tun lokacin da aka burma shi bai zaga ko lalata wasu sassan gabobin mutumin ba.

A lokacin da aka sanya masa wukar shekaru takwas da suka wuce, asibitin da suka masa dinkin, ba su ga wani alami ko dalilin da zai sanya su zurfafa bincike ba saboda bai musu korafin jin wani zafi ba, illa ya nuna garau yake ji, don haka a wancan lokacin babu bukatar zurfafa bincike, a cewar rahoton.

Sai dai rahoton ya nuna mamakin yadda mutumin dan shekara 44 ya ci gaba da rayuwarsa ba tare da wata matsala ba, duk kuwa da cewa diwan ya fito ne sakamakon matattun nama da suka kewaye jikin wukar.

Bayan gano wukar a kirjin mutumin, likitocin sun yi tiyata tare da ciro wukar da sauran naman da suka lalace da fitar da diwan baki daya.

Majinyacin ya kwashe awanni 24 a sashin kulawa ta musamman kafin daga bisani aka maida shi zuwa dakin jinya na tsawon kwanaki goma. Ya samu lafiya sosai ya kuma ci gaba da rayuwarsa ba tare da jin wani zafi ba.

Wuka
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

MASU ALAKA

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa
Manyan Labarai

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Rahotonni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro
Labarai

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Jagororin 'Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Abinci

Yadda Gwamnatin Kano Ta Samu Nasarar Kashi 80 A Fannin Aikin Noma

June 19, 2026
Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

Hakimi Zai Gurfana A Kotu Kan Zargin Aikata Fyaɗe A Faransa

June 19, 2026
Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

Jarin Waje Ya Inganta Hada-hadar Zuba Jari A Kasar Sin

June 19, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni

June 19, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

Sin Ta Yi Kira Da A Cimma Cikakkiyar Matsayar Kawo Karshen Fada A Gaza

June 19, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

Sin Na Fatan Inganta Tuntuba Da Tsare-tsare Tsakaninta Da Membobin BRICS

June 19, 2026
Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

Dattawan Arewa Sun Buƙaci Tinubu Ya Ayyana Dokar Ta-baci Kan Tabarbarewar Tsaro

June 19, 2026
Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

Sin Na Kira Da A Ingiza Matakan Siyasa A Kasar Libya

June 19, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.