ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Likitoci Sun Gano Wuka Da Aka Burma A Kirjin Wani Mutum Tsawon Shekara 8 

by Khalid Idris Doya
11 months ago
Wuka

Wani dan kasar Tanzania da ya je asibiti da korafin diwa na yawan fita daga cikin nononsa na dama, ya shiga cikin dimuwa da gigicewa yayin da ya fahimci yana rayuwa da wani katon wuka a cikin kirjinsa ba tare da ya sani ba na tsawon shekaru har takwas, kafar yada labarai ta kasar ce ta rawaito. 

Likitoci a babban asibitin Muhimbili da ke Tanzania a baya-bayan nan suka wallafa rahoton wani jinya wanda ba a saba samun irinsa ba, wanda ya zo da ban mamaki matuka.

  • EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
  • Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

Sun rubuta cewa, wani mutum dan shekara 44 a duniya da ke cikin rayuwa da koshin lafiyarsa, ya kawo musu korafin cewa cikin kwanaki goma yana ganin farin ruwan diwa na fita daga nononsa na dama.

ADVERTISEMENT

Sai dai ya ce shi baya jin wani zafi a cikin kirjinsa, ko wahalar jan numfashi, tari ko zazzabi, da aka tambaye shi ko yana da wani abu na daman da zai iya fada wa likitocin, sai ya tuna cewar a shekaru takwas da suka wuce sun taba yin fada, wanda a lokacin ya samu yanka (raunuka) a fuskantasa, kirji da kuma cikinsa.

Ya tabbatar da cewa tun a can lokacin likitoci sun dinke ramuka da raunukan da ya samu kuma ya ci gaba da rayuwarsa samul-garau, har sai lokacin da nononsa ya fara fitar da farin ruwa na diwa.

LABARAI MASU NASABA

‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

Bayan da likitocin suka kasa gane wacce irin cuta ce take janyo masa wannan fitar da diwan, likitocin sun umarci a je a dauki hoton kirjinsa, inda a nan ne suka gano katoton wukan da aka burma a cikin mutumin.

Likitocin sun rubuta cikin rahoton binciken nasu cewa hoton farko da aka dauka ya nuna zanen wani abu da ke kwance cikin kirjin mutumin, wanda daga bisani aka gano balo-balo wuka ne.

Sai dai sun gano cewa wukan tun lokacin da aka burma shi bai zaga ko lalata wasu sassan gabobin mutumin ba.

A lokacin da aka sanya masa wukar shekaru takwas da suka wuce, asibitin da suka masa dinkin, ba su ga wani alami ko dalilin da zai sanya su zurfafa bincike ba saboda bai musu korafin jin wani zafi ba, illa ya nuna garau yake ji, don haka a wancan lokacin babu bukatar zurfafa bincike, a cewar rahoton.

Sai dai rahoton ya nuna mamakin yadda mutumin dan shekara 44 ya ci gaba da rayuwarsa ba tare da wata matsala ba, duk kuwa da cewa diwan ya fito ne sakamakon matattun nama da suka kewaye jikin wukar.

Bayan gano wukar a kirjin mutumin, likitocin sun yi tiyata tare da ciro wukar da sauran naman da suka lalace da fitar da diwan baki daya.

Majinyacin ya kwashe awanni 24 a sashin kulawa ta musamman kafin daga bisani aka maida shi zuwa dakin jinya na tsawon kwanaki goma. Ya samu lafiya sosai ya kuma ci gaba da rayuwarsa ba tare da jin wani zafi ba.

Wuka
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda
Labarai

‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

July 9, 2026
Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

July 9, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

July 9, 2026
Next Post
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi

’Yansanda Sun Kama Jagororin 'Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

LABARAI MASU NASABA

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

July 9, 2026
Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

July 9, 2026
‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

July 9, 2026
Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

July 9, 2026
Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

July 9, 2026
Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

July 9, 2026
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

July 9, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

July 9, 2026
An Gabatar Da Shirin Fadar Potala Ta Kafar CMG

An Gabatar Da Shirin Fadar Potala Ta Kafar CMG

July 9, 2026
kebbi

Makarantu Za Su Ci Gaba Da Zama A Rufe Har Sai Yanayin Tsaro Ya Inganta – Gwamnatin Kebbi

July 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.