• English
  • Business News
Wednesday, July 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Likitoci Sun Ja Hankali Kan Yiwuwar Barkewar Cututtuka Masu Yaduwa A Kaduna

by Sadiq
9 months ago
in Labarai
0
Likitoci Sun Ja Hankali Kan Yiwuwar Barkewar Cututtuka Masu Yaduwa A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Likitocin Nijeriya reshen Jihar Kaduna, ta yi jan hankali game da cututtuka masu saurin yaduwa kamar su cutar kyandar biri, Ebola da kuma zazzabin Lassa a Nijeriya. 

A yayin wani taron manema labarai a bikin makon likitoci, shugaban kungiyar, Dokts Hassan Salihu, ya jaddada muhimmancin tattaunawa game da barkewar cututtuka tare da daukar matakan kariya.

  • Muna Fama Da Taɓarɓarewar Tattalin Arziƙi Da Wutar Lantarki – Gwamnonin Arewa Da Sarakuna
  • Abubuwan Da Ka Tattaunawa A Taron Gwamnoni da Sarakunan Arewa

Ya bayyana cewa, ko da yake ba a samu rahoton bullar kyandar biri a Kaduna ba zuwa yanzu.

Dokts Salihu ya bayyana matakan da jama’a za su bi don kare kansu, kamar tsaftar jiki, cin abinci mai gina jiki, da kuma kaucewa nau’in wasu dabbobi.

Kungiyar na aiki don dakile yaduwar cututtuka don tabbatar da lafiyar al’umma a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

Sun kuma shirya gangamin wayar da kan jama’a, yin allurar rigakafi, da inganta cibiyoyin kiwon lafiya.

Dokta Salihu ya bayyana mawuyacin halin da likitoci ke ciki a Kaduna, inda ya ce rashin ingantaccen albashi, rashin kayan aiki, da matsalolin tsaro, musamman a yankunan karkara, suna sa likitoci na barin Nijeriya.

A cewarsa wannan matsala ta shafi kiwon lafiya yayin da ma’aikatan lafiya ke neman guraben aiki a kasashen waje.

Kungiyar ta yi kira da a tabbatar da an daidaita albashinsu a fadin Nijeriya domin taimakawa wajen ci gaba da rike kwararrun ma’aikatan lafiya da rage gibin kiwon lafiya.

Dokts Salihu ya bayar da shawarar kafa dokar kasa don sanya mafi karancin albashi ga ma’aikatan lafiya a duk jihohi don a ci gaba da rike kwararru ma’aikatan fannin.

Har wa yau, ya bayyana damuwarsa kan lalacewar wutar lantarki a Arewacin Nijeriya, wanda ke barazana ga rayuwar marasa lafiya.

Kazalika, ya yi kira ga gwamnati ta yi kokari wajen ganin an sako likitar da aka sace, Dokta Ganiyat Popoola.

Likitar ta shafe wata 10 a hannun maharan da suka sace ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jan HankaliKadunaKungiyaLikitociTaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Next Post

Sin Za Ta Harba Kumbon “Shenzhou-19” Mai Daukar ’Yan Sama Jannati 3

Related

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
Manyan Labarai

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

1 hour ago
Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

3 hours ago
’Yansanda Sun Gano Gawar Ɗan Jaridar Da Aka Kashe A Jihar Kogi
Labarai

’Yansanda Sun Gano Gawar Ɗan Jaridar Da Aka Kashe A Jihar Kogi

4 hours ago
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

5 hours ago
Shugaban Hukumar Zaɓe Ta Bauchi, Ahmad Makama, Ya Rasu
Labarai

Shugaban Hukumar Zaɓe Ta Bauchi, Ahmad Makama, Ya Rasu

5 hours ago
Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki
Labarai

Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki

6 hours ago
Next Post
Sin Za Ta Harba Kumbon “Shenzhou-19” Mai Daukar ’Yan Sama Jannati 3

Sin Za Ta Harba Kumbon “Shenzhou-19” Mai Daukar ’Yan Sama Jannati 3

LABARAI MASU NASABA

Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar

Rashin Nasarar DPP A Zagayen Farko Na Kuri’ar Kiranye Ya Nuna Rashin Amincewar Al’ummar Taiwan Da Salon Mulkin Jami’yyar

July 30, 2025
Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

July 30, 2025
Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

July 30, 2025
’Yansanda Sun Gano Gawar Ɗan Jaridar Da Aka Kashe A Jihar Kogi

’Yansanda Sun Gano Gawar Ɗan Jaridar Da Aka Kashe A Jihar Kogi

July 30, 2025
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

July 30, 2025
Shugaban Hukumar Zaɓe Ta Bauchi, Ahmad Makama, Ya Rasu

Shugaban Hukumar Zaɓe Ta Bauchi, Ahmad Makama, Ya Rasu

July 30, 2025
Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki

Gwamnan Kaduna Ya Sauke Kwamishinan Yaɗa Labarai, Ya Maye Gurbinsa Da Maiyaki

July 30, 2025
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

July 30, 2025
Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

Zaɓen 2027: Arewa Za Ta Sake Mara Wa Tinubu Baya — Gwamna Inuwa

July 30, 2025
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku Miƙa Wuya – Ribadu Ya Gargaɗi ‘Yan Bindiga

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.