• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Likitoci Sun Ja Hankali Kan Yiwuwar Barkewar Cututtuka Masu Yaduwa A Kaduna

by Sadiq
7 months ago
in Labarai
0
Likitoci Sun Ja Hankali Kan Yiwuwar Barkewar Cututtuka Masu Yaduwa A Kaduna
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Likitocin Nijeriya reshen Jihar Kaduna, ta yi jan hankali game da cututtuka masu saurin yaduwa kamar su cutar kyandar biri, Ebola da kuma zazzabin Lassa a Nijeriya. 

A yayin wani taron manema labarai a bikin makon likitoci, shugaban kungiyar, Dokts Hassan Salihu, ya jaddada muhimmancin tattaunawa game da barkewar cututtuka tare da daukar matakan kariya.

  • Muna Fama Da Taɓarɓarewar Tattalin Arziƙi Da Wutar Lantarki – Gwamnonin Arewa Da Sarakuna
  • Abubuwan Da Ka Tattaunawa A Taron Gwamnoni da Sarakunan Arewa

Ya bayyana cewa, ko da yake ba a samu rahoton bullar kyandar biri a Kaduna ba zuwa yanzu.

Dokts Salihu ya bayyana matakan da jama’a za su bi don kare kansu, kamar tsaftar jiki, cin abinci mai gina jiki, da kuma kaucewa nau’in wasu dabbobi.

Kungiyar na aiki don dakile yaduwar cututtuka don tabbatar da lafiyar al’umma a jihar.

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Sun kuma shirya gangamin wayar da kan jama’a, yin allurar rigakafi, da inganta cibiyoyin kiwon lafiya.

Dokta Salihu ya bayyana mawuyacin halin da likitoci ke ciki a Kaduna, inda ya ce rashin ingantaccen albashi, rashin kayan aiki, da matsalolin tsaro, musamman a yankunan karkara, suna sa likitoci na barin Nijeriya.

A cewarsa wannan matsala ta shafi kiwon lafiya yayin da ma’aikatan lafiya ke neman guraben aiki a kasashen waje.

Kungiyar ta yi kira da a tabbatar da an daidaita albashinsu a fadin Nijeriya domin taimakawa wajen ci gaba da rike kwararrun ma’aikatan lafiya da rage gibin kiwon lafiya.

Dokts Salihu ya bayar da shawarar kafa dokar kasa don sanya mafi karancin albashi ga ma’aikatan lafiya a duk jihohi don a ci gaba da rike kwararru ma’aikatan fannin.

Har wa yau, ya bayyana damuwarsa kan lalacewar wutar lantarki a Arewacin Nijeriya, wanda ke barazana ga rayuwar marasa lafiya.

Kazalika, ya yi kira ga gwamnati ta yi kokari wajen ganin an sako likitar da aka sace, Dokta Ganiyat Popoola.

Likitar ta shafe wata 10 a hannun maharan da suka sace ta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Jan HankaliKadunaKungiyaLikitociTaro
ShareTweetSendShare
Previous Post

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Next Post

Sin Za Ta Harba Kumbon “Shenzhou-19” Mai Daukar ’Yan Sama Jannati 3

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

2 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

4 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

5 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

6 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

7 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

9 hours ago
Next Post
Sin Za Ta Harba Kumbon “Shenzhou-19” Mai Daukar ’Yan Sama Jannati 3

Sin Za Ta Harba Kumbon “Shenzhou-19” Mai Daukar ’Yan Sama Jannati 3

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.