ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Fama Da Taɓarɓarewar Tattalin Arziƙi Da Wutar Lantarki – Gwamnonin Arewa Da Sarakuna

by Sulaiman
2 years ago
Arewa

Arewa ce ta fi fama da matsalar taɓarɓarewar tattalin arziki a Nijeriya, kamar yadda gwamnoni da sarakunan yankin suka bayyana a ranar Litinin 28 ga watan Oktoba.

 

Sun bayyana haka ne a yayin taron gaggawa na gwamnonin jihohin Arewa (NSGF) da sarakunan gargajiya da aka yi a Gidan Gwamnatin Kaduna (Sir. Kashim Ibrahim House) don magance matsalolin da yankin ke fuskanta.

ADVERTISEMENT
  • Bangarorin Masana’antu Da Kasuwancin Kasar Sin Sun Bayyana Adawa Da Matakan Kariyar Ciniki Da Kasar Amurka Ta Dauka
  • APC Ce Za Ta Lashe Zaɓen Gwamnan Ondo – Ganduje

Taron ya samu halartar Gwamnonin Arewa daban-daban da sarakunan gargajiya karkashin jagorancin Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III da babban hafsan hafsoshin tsaro, Janar Christopher Musa.

 

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Da yake jawabi a yayin taron, shugaban kungiyar kuma Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ce a matsayinsu na shugabannin Arewa, dole ne Gwamnonin su dauki matakan rage radadin talauci da mafi yawancin mazauna yankin ke fama da shi ta hanyar wanzar da shirye-shiryen walwalar jama’a, tallafawa kanana da matsakaitan masana’antu da kuma nemo masu saka hannun jari zuwa yankin.

 

ArewaYa yi kira da a samar da cikakken garambawul a dukkanin cibiyoyi, yana mai cewa, a halin yanzu suna ci gaba da yin kwaskwarima a manufofi da tsare-tsaren NSGF domin karfafa ayyukan kungiyar, wanda zai ba ta damar magance kalubalen da ake fuskanta yadda ya kamata.

 

Kungiyar ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da Hukumomin da abin ya shafa da su gaggauta magance matsalar wutar lantarki da ke addabar yawancin Jihohin Arewa sakamakon lalata turakun layin wutar lantarki da bata-gari suka yi.

 

Kungiyar ta amince cewa, Arewacin Nijeriya yana da dimbin albarkatun noma, wanda idan aka yi amfani da shi yadda yakamata, zai rage yunwa da bunkasar tattalin arziki. Don cimma wannan buri, kungiyar ta kuduri aniyar bayar da tallafin da ya dace ga manoma, da suka hada da samar da kudade, dabarun noman zamani da ababen more rayuwa kamar tituna da samar da ruwa don noman rani. Ba wai kawai a kalli noma a matsayin hanyar ciyar da al’ummarmu ba, har ma a matsayin hanyar samar da masana’antu da samar da ayyukan yi a fadin yankin. Za a iya cimma hakan ta hanyar sake farfado da masana’antun tufafi a Arewa

 

Sarkin Musulmi kuma Shugaban Majalisar Sarakunan Gargajiya ta Arewa, Alhaji Muhammad Sa’ad Abubakar III ya ce, yankin bai rasa wani rahoto ko mafita ba kan kalubalen da yake fuskanta, sai dai rashin aiwatar da shawarwarin da aka bayar kan magance kalubalen da aka gano.

Arewa

Sarkin Musulmi ya umarci shugabannin yankin da su marawa shirin gwamnatin tarayya baya na magance matsalar Almajirci da yaran da ba sa zuwa makaranta.

 

Babban hafsan hafsoshin tsaron Nijeriya, Janar Christopher Musa, wanda ya yi jawabi a wurin taron NSGF, ya ce dakarun sojin suna aiki tukuru domin magance matsalar rashin tsaro da ke addabar yankin Arewa da ma sauran sassan kasar nan.

 

Musa ya yabawa gwamnonin Arewa da sarakunan gargajiya bisa goyon baya da hadin kai da suke bayarwa don magance matsalolin tsaro da suka addabi yankin Arewa.

 

A karshe, kungiyar NSGF ta yabawa mai girma shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu da babban kwamandan rundunar sojojin tarayyar Nijeriya, Janar Christopher Musa bisa shirin kawo sauyi a bangaren kiwon dabbobi tare da amincewa da bayar da duk wani abu da ake bukata wajen tabbatar da nasarar gwamnatin tarayya wajen shirin bunkasa kiwon.

Arewa
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed
  • Sulaiman
    Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
  • Sulaiman
    Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Gyara Wutar Lantarkin Arewa Cikin Gaggawa

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.