Allah ya yi wa babban limamin masallacin Juma’a da ke kan titin Maiduguri a Jihar Kaduna, Sheikh Dahiru Lawal Abubakar, rasuwa.
Sheikh Dahiru, ya rasu da safiyar yau Laraba, za a yi Jana’izarsa da misalin karfe 1:00 na rana yau Laraba a masallacin da yake limanci da ke kan titin Maiduguri a Jihar Kaduna.
Muna Addu’ar Allah ya gafarta masa, ya kyauta karshenmu, idan tamu ta zo yasa mu cika da imani, Amin.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp