• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Lokaci Ya Yi Da Za A Mayar Da Kayayyakin Tagulla Na Daular Benin Gida

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Lokaci Ya Yi Da Za A Mayar Da Kayayyakin Tagulla Na Daular Benin Gida
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gidan adana kayayyakin tarihi na Burtaniya, wato the British Museum a Turance, ya kasance daya daga cikin gidajen adana kayayyakin tarihi mafi girma kuma mafi dadadden tarihi a duniya, sai dai da yawa daga cikin kayayyaki sama da miliyan 8 da ke gidan, an kwato ko sato su ne daga kasa da kasa a lokacin da Birtaniya ke mulkin mallaka a sassan duniya. 

Misali a gidan, akwai kayayyakin tagulla kimanin 900 na daular gargajiya ta Benin wadda a zamanin da ta kasance a kudancin kasar Nijeriya, wadanda Burtaniya ta kwaso su gidan bayan da ta wawushe fadar daular a lokacin da ta kaddamar da yaki kan daular a shekarar 1897. Wadannan kayayyakin tagulla dai sun kasance masu matukar muhimmanci a tarihin fasahar Afirka, haka kuma kayayyakin tarihi masu daraja na al’ummar Nijeriya. Ban da su, a gidan, akwai sassakan marmara na Parthenon na kasar Girika, da dutsen Rosetta na kasar Masar da ma wasu kayayyakin tarihi masu daraja dubu 23 da suka fito daga kasar Sin, wadanda suka shaida mummunan tarihin mulkin mallaka na Burtaniya.

  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Kaucewa Aiwatar Da Matakan Da Ka Iya Barazana Ga Tsaronta
  • Sin Ta Bayyana Matukar Adawa Ga Amurka Game Da Batun Sayarwa Taiwan Makamai

Duk da cewa kasashen Sin da Nijeriya da Girika sun sha bukatar Burtaniya da ta mayar musu da wadannan kayayyakin tarihi, amma kullum Burtaniya ta kan ki bisa dalili na wai “kare lafiyar kayayyakin”. Amma abin kunya shi ne, a cikin kusan shekaru 30 da suka gabata, gidan adana kayayyakin tarihi na Burtaniya wanda ke daukar kanta a matsayin mai kare lafiyar kayayyakin tarihi, ya sha fuskantar sace-sace a kalla sau shida. Wani rahoton bincike na baya-bayan da gidan ya fitar, ya kuma nuna cewa, daga cikin kayayyakin da gidan bai nuna su ba, akwai kimanin 2000 da suka bace ko aka sace su ko kuma suka lalace.

A game da yanayin tsaro na kayayyakin tarihi da ke gidan, Abba Isa Tijani, babban darektan kwamitin kula da gidajen adana kayayyakin tarihi da kayayyakin tarihi na Nijeriya ya ce, “wasu kasashe da gidajen adana kayayyakin tarihi sun sha bayyana mana cewa, kayayyakin tagulla na daular Benin ba su da tsaro a Nijeriya, amma ga yadda aka sace su. Ainihin batun shi ne kayayyakin tarihi ne da aka kwashe, kuma ya kamata a mayar da su gidanjensu ko kasashensu na asali.”

Zamanin mulkin mallaka ya shude, kuma shekaru sama da 120 ke nan da aka kwace kayayyakin tagulla na daular Benin daga Nijeriya, lokaci ya yi da za a mayar da su gida. (Mai Zane: Mustapha Bulama)

Labarai Masu Nasaba

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Dokokin Kano Ta Amince Da Kasafin Biliyan 437.3 Na 2024

Next Post

Kafafen Yaɗa Labarai Ne Manyan Dirkokin Dimokraɗiyyarmu – Minista

Related

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

2 hours ago
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO
Daga Birnin Sin

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

2 hours ago
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II
Daga Birnin Sin

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

3 hours ago
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO
Daga Birnin Sin

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

5 hours ago
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”
Daga Birnin Sin

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

6 hours ago
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi
Daga Birnin Sin

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

8 hours ago
Next Post
Kafafen Yaɗa Labarai Ne Manyan Dirkokin Dimokraɗiyyarmu – Minista

Kafafen Yaɗa Labarai Ne Manyan Dirkokin Dimokraɗiyyarmu - Minista

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.