ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, November 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikata 2 Sun Shiga Hannu Kan Zargin Sace Tiraktocin Taki 9 A Nasarawa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Ma'aikata

Akanta da jami’in kula da dakin ajiye kayayyaki na ma’aikatar gona da albarkatun kasa na jihar Nasarawa sun shiga hannun da zarginsu da ake yi na karkatar da tiraktocin guda tara na Takin zamani da aka samar da zimmar raba wa manoma a sassan kananan hukumomin 13 da ke jihar.

Kwamishinan ma’aikatar gona ta jihar Hon. Nuhu Ibrahim-Oshafu, shine ya shaida hakan a lokacin da jami’an ma’aikatar gona na jihar Nasarawa da ma’aikatar bunkasa harkokin gona ta jihar (NADP) suka bayyana a gaban kwamiti domin kare kwazon kasafin kudi na 2022.

  • Wang Yi Ya Yi Tsokaci Kan Matsayar Sin A Batun Tekun Kudancin Kasar
  • Ko Kananan Sana’o’i Na Biya Wa ‘Yan Nijeriya Bukatunsu?

Ibrahim-Oshafu, ya ce, ma’aikatar ta sayo da raba tiraktoci Taki 21 da aka sayo a kan kudi naira miliyan N238 a jihar.

ADVERTISEMENT

Ya ce a lokacin da ya shiga Ofis domin kama aiki, 12 da rabin tiraktocin takin ne aka mika masa, ya ce amma da suka je dakin ajiye kayayyaki sai suka gano tiraktocin 9 sun yi baton dabo.

Ya ce an cafke Akanta da jami’in kula da dakin ajiye kayayyaki bisa zargi da hannu a bacewar takin kuma tunin aka dakatar da su a yayin da bincike ke cigaba da gudana kan lamarin.

LABARAI MASU NASABA

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

Shi kuma Manajan NADP, Mr Emmanuel Allahnana, da ya bayyana a gaban kwamitin ya ce akwai karancin malaman gona da jihar ke fama da shi don haka ya roki a dauki karin ma’aikata domin shawo kan matsalolin da ake fuskanta a fannin harkokin noma domin bunkasa harkokin abinci a jihar.

Da yake maida bayani kan batutuwan da suke akwai, Shugaban kwamitin gona na Majalisar Dokokin Jihar, Mr. Ibrahim Peter-Akwe, ya roki gwamnatin jihar ta ayyana dokar ta baci a bangaren noma, ya kuma gargadi ma’aikatan dangane da karancin Taki da manoma ke samu a jihar.

Ya ce fannin gona na da muhimmanci a jihar don haka da bukatar gwamnati ta dauki matakan shawo kan matsalolin da suke akwai a bangaren gona.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari
Kotu Da Ɗansanda

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Next Post
Kasar Sin Na Gudanar Da Atisayen Soji A Rawayen Teku Da Tekun Bohai

Kasar Sin Na Gudanar Da Atisayen Soji A Rawayen Teku Da Tekun Bohai

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Hallaka Dama-Dama

NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Hallaka Dama-Dama

November 15, 2025
Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

Masu Kokarin Kashe Kansu Na Kara Karuwa A Nijeriya

November 15, 2025
Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

Wakilai Daga Jihohi 19 Sun Isa Ibadan Don Taron PDP Na Ƙasa

November 15, 2025
Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

Daliban FUTA 240 Sun Samu Digiri Mai Daraja Ta Daya

November 15, 2025
Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

Shakirat Ta Tsallaka Mataki Na Ƙarshe Na Zama Gwarzuwar Ƴar Wasan Afrika

November 15, 2025
Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

Wasu Mahara Sun Kashe Mata 2, Tare Da da Ƙona Gidansu A Tudun Yola

November 15, 2025
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje

November 15, 2025
Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari

November 15, 2025
Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

Shugaban APC Na Kano Ya Nemi Afuwa Daga Al’ummar Fagge Kan Kalamansa

November 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Cafke Wani Da Ake Zargin Dan Ta’adda Ne A Jihar Kebbi

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.