• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Ta Fara Bitar Ayyuka Na Tsakiyar Wa’adi

by Sulaiman
1 day ago
in Labarai
0
Ma’aikatar Yaɗa Labarai Ta Fara Bitar Ayyuka Na Tsakiyar Wa’adi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai ta fara bita kan yadda ta gudanar da ayyukan ta a zangon aiki na biyu, domin tabbatar da cika manyan abubuwan da Shugaban Ƙasa ya ɗora mata ta hannun Ofishin Tsare-tsare da Bibiyar Ayyuka (CDCU) da ke Ofishin Shugaban Ƙasa.

 

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, shi ne ya jagoranci zaman bitar da aka gudanar a Abuja ranar Talata, inda ya bayyana cewa taron yana da nasaba da yarjejeniyar aiki da ya rattaba hannu a kai da shugabannin hukumomin da ke ƙarƙashin ma’aikatar a watan Agustan 2024.

  • Tattalin Arzikin Sin Tamkar Teku Ne Ba Karamin Tabki Ba
  • APC: Na Bar PDP Ne Domin Ci Gaba Da Amfana Da Ribar Ofishi Na – Kakakin Majalisar Edo

Ya ce kafin hakan ma, ya rattaba hannu kan wata yarjejeniya da Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu kan manyan abubuwan da ma’aikatar za ta cimma.

 

Labarai Masu Nasaba

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

A cewar sa, wannan bita tana da nufin tantance yadda aka samu cigaba a aiki, da kuma tabbatar da cewa hukumomin da ke ƙarƙashin ma’aikatar suna tafiya daidai da abin da aka ɗora masu a matsayin nauyi.

 

Ya ce: “Muna nan ne don sauraron shugabannin hukumomi domin mu ga yadda suka aiwatar da muhimman abubuwan da muka rattaba hannu a kai. Idan akwai ƙalubale, za mu tattauna su. Idan akwai cikas, za mu duba abin da za mu iya yi domin shawo kansu.”

 

Ministan ya bayyana wannan taro a matsayin hanyar tantance kai kafin a kai tsakiyar wa’adin gwamnatin yanzu.

 

Ya ce: “Ku tuna cewa wannan gwamnati ta fara aiki kusan shekaru biyu da suka gabata. Cikin ƙasa da wata guda daga yanzu, wannan gwamnati za ta kai rabin wa’adin ta a ranar 29 ga Mayu.

 

“Saboda haka, lokaci ya yi – kamar yadda Ofishin Shugaban Ƙasa ya nema – da kowace ma’aikata za ta fidda sakamakon aikin ta kan abubuwan da ta tsara kuma aka amince da su ta hannun ofishin CDCU da ke Ofishin Shugaban Ƙasa.”

 

Idris ya kuma jaddada cewa ma’aikatar sa na jajircewa wajen samar wa ‘yan Nijeriya da sahihan bayanai game da nasarorin gwamnati da kuma ƙalubalen da take fuskanta.

 

Ya ce: “Abin da wannan ma’aikatar ke yi shi ne tabbatar da cewa ba wai kawai muna wayar da kan ‘yan Nijeriya kan abubuwan da ke cikin hangen nesa na Shugaban Ƙasa ba, har ma muna bayyana ƙalubalen da ke akwai cikin gaskiya da riƙon amana? Tabbas, wannan ne abin da muka ɗauka tun farko kuma za mu ci gaba da bin wannan hanya.”

 

Ya ƙara da cewa babban aikin ma’aikatar shi ne tsarawa da aiwatar da dabarun sadarwa masu ma’ana domin inganta gaskiya da rarraba bayanai game da manufofi da shirye-shiryen gwamnati, yaƙi da yaɗa ƙarya, da kuma ƙarfafa wayar da kan ‘yan ƙasa bisa fifikon gwamnatin Tinubu.

 

Taron ya samu halartar shugabannin hukumomi kamar haka: Darakta Janar na Hukumar Talabijin ta Nijeriya (NTA), Kwamared Abdulhamid Dembos; Darakta Janar na Hukumar Rediyon Tarayyar Nijeriya (FRCN), Dakta Mohammed Bulama; Darakta Janar na Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA), Mista Lanre Issa Onilu; Darakta Janar na Hukumar Kula da Gidajen Rediyo da Talbijin ta Ƙasa (NBC), Mista Charles Ebuebu; Darakta Janar na Muryar Nijeriya (VON), Malam Jibrin Baba Ndace; Darakta Janar na Hukumar Kula da Tallace-tallace (ARCON), Dakta Olalekan Fadolapo; da Manajan Darakta na Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya (NAN), Malam Ali M. Ali.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sabbin Fasahohin Noma Na Zamani Na Ci Gaba Da Bayyana A Kasar Sin

Next Post

Ma’aunin Asusun Ajiyar Kudin Musayar Waje Na Sin Na Cikin Daidaito

Related

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

6 hours ago
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

9 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da ɗumi-ɗuminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

10 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

11 hours ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

13 hours ago
Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar
Labarai

Almundahana: LP Ta Nada Sanata Ireti Kingibe Domin Binciken Tsohon Shugaban Jam’iyyar

14 hours ago
Next Post
Ma’aunin Asusun Ajiyar Kudin Musayar Waje Na Sin Na Cikin Daidaito

Ma’aunin Asusun Ajiyar Kudin Musayar Waje Na Sin Na Cikin Daidaito

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

Xi Da Putin Sun Rattaba Hannu Kan Sanarwar Hadin Gwiwa A Sabon Zamani

May 8, 2025
Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

Waiwaye Game Da Gudummawar Shawarar BRI Ga Duniya

May 8, 2025
Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

Me Ya Sa ‘Yan Kasuwar Kasashen Afirka Rungumar Kudin RMB?

May 8, 2025
Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

Bisa Rokon Bangaren Amurka Ne Manyan Jami’In Kasar Sin Zai Tattauna Da Takwaransa Na Gwamnatin Amurka Kan Batun Ciniki Da Tattalin Arziki

May 8, 2025
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

May 8, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

May 8, 2025
An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

An Yi Taron Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Na Bikin Cika Shekaru 80 Da Nasarar Yakin Da Sinawa Suka Yi Kan Zaluncin Japan Da Yakin Ceton Kasa Na Tsohuwar Tarayyar Soviet

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.