ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mafi Ƙarancin Albashi: Ƙungiyar Ƙwadago Ta Yi Fatali Da Tayin Gwamnatin Tarayya Na ₦62,000

by Muhammad
1 year ago
Mafi

Ƙungiyar Ƙwadago ta bayyana cewa ba za ta sake tattaunawa kan tayin mafi karancin albashi na ₦62,000 da gwamnatin tarayya ta gabatar ba, inda ta bayyana shi a matsayin albashin zama da yunwa.

Ƙungiyar NLC da takwararta ta (TUC), sun yi gargadin cewa idan har gwamnatin tarayya da majalisar dokokin Nijeriya, suka gaza aiwatar da buƙatun ma’aikata zuwa ranar Talata, sassanta za su hadu domin yanke shawara kan batun dawo da yajin aiki a fadin ƙasarnan.

  • Yau Litinin Gwamnati Da Ƙungiyar Ƙwadago Za Su Cimma Matsaya Kan Mafi Ƙarancin Albashi
  • Ma’aikata Sun Nemi Gwamnoni Su Zaftare Albashin Su Don Biyan Mafi Karancin Albashi

Mataimakin babban sakataren Ƙungiyar NLC, Chris Onyeka, wanda ya bayyana haka a wata hira da gidan Talabijin na Channels, safiyar yau Litinin, ya ce ma’aikata za su tashi tsaye idan wa’adin mako guda da aka bai wa gwamnatin tarayya a ranar Talata, 4 ga watan Yuni, 2024, ya kare a daren Talata, Yuni 11, 2024.

ADVERTISEMENT

Da yake magana kan yiwuwar matakin Ƙungiyar Ƙwadago idan gwamnati ta dage a kan Naira 62,000, Onyeka ya ce, a bayyane yake abin da suka faɗa na sassauta yajin aikin da suka yi a fadin ƙasarnan, don haka rassan kungiyoyin kwadago za su yanke shawarar cewa ya kamata su janye wannan dakatarwar, hakan yana nufin su koma yajin aiki.

Ya jaddada cewa Ƙungiyar ƙwadago ba za ta karbi ₦62,000 ko ₦100,000 a matsayin albashi mafi ƙarancin ga ma’aikatan Nijeriya ba, inda ta dage a kan ₦250,000, kamar yadda Ƙungiyar Ƙwadago ta bukata a taron karshe na kwamitin mafi ƙarancin albashi a ranar Juma’a, a matsayin albashin ma’aikacin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Ya ƙara da cewa haƙiƙanin gaskiya shi ne farashin kaya ƙara tashi ya ke a kowacce rana tare da bayar da misali da tashin kayan abinci da sauransu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle
Manyan Labarai

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
Nazari

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Next Post
‘Yan Jarida Sun Dakatar Da Kawo Rahotanni Daga Fadar Gwamnatin Kano

‘Yan Jarida Sun Dakatar Da Kawo Rahotanni Daga Fadar Gwamnatin Kano

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.