ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mafi Ƙarancin Albashi: Ƙungiyar Ƙwadago Ta Yi Fatali Da Tayin Gwamnatin Tarayya Na ₦62,000

by Muhammad
2 years ago
Mafi

Ƙungiyar Ƙwadago ta bayyana cewa ba za ta sake tattaunawa kan tayin mafi karancin albashi na ₦62,000 da gwamnatin tarayya ta gabatar ba, inda ta bayyana shi a matsayin albashin zama da yunwa.

Ƙungiyar NLC da takwararta ta (TUC), sun yi gargadin cewa idan har gwamnatin tarayya da majalisar dokokin Nijeriya, suka gaza aiwatar da buƙatun ma’aikata zuwa ranar Talata, sassanta za su hadu domin yanke shawara kan batun dawo da yajin aiki a fadin ƙasarnan.

  • Yau Litinin Gwamnati Da Ƙungiyar Ƙwadago Za Su Cimma Matsaya Kan Mafi Ƙarancin Albashi
  • Ma’aikata Sun Nemi Gwamnoni Su Zaftare Albashin Su Don Biyan Mafi Karancin Albashi

Mataimakin babban sakataren Ƙungiyar NLC, Chris Onyeka, wanda ya bayyana haka a wata hira da gidan Talabijin na Channels, safiyar yau Litinin, ya ce ma’aikata za su tashi tsaye idan wa’adin mako guda da aka bai wa gwamnatin tarayya a ranar Talata, 4 ga watan Yuni, 2024, ya kare a daren Talata, Yuni 11, 2024.

ADVERTISEMENT

Da yake magana kan yiwuwar matakin Ƙungiyar Ƙwadago idan gwamnati ta dage a kan Naira 62,000, Onyeka ya ce, a bayyane yake abin da suka faɗa na sassauta yajin aikin da suka yi a fadin ƙasarnan, don haka rassan kungiyoyin kwadago za su yanke shawarar cewa ya kamata su janye wannan dakatarwar, hakan yana nufin su koma yajin aiki.

Ya jaddada cewa Ƙungiyar ƙwadago ba za ta karbi ₦62,000 ko ₦100,000 a matsayin albashi mafi ƙarancin ga ma’aikatan Nijeriya ba, inda ta dage a kan ₦250,000, kamar yadda Ƙungiyar Ƙwadago ta bukata a taron karshe na kwamitin mafi ƙarancin albashi a ranar Juma’a, a matsayin albashin ma’aikacin Nijeriya.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Ya ƙara da cewa haƙiƙanin gaskiya shi ne farashin kaya ƙara tashi ya ke a kowacce rana tare da bayar da misali da tashin kayan abinci da sauransu.

Mafi
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
‘Yan Jarida Sun Dakatar Da Kawo Rahotanni Daga Fadar Gwamnatin Kano

‘Yan Jarida Sun Dakatar Da Kawo Rahotanni Daga Fadar Gwamnatin Kano

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.