• English
  • Business News
Saturday, August 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Maganar Tarkon Bashi Ta Nuna Rashin Karfin Gwiwar Kasashen Yamma

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Maganar Tarkon Bashi Ta Nuna Rashin Karfin Gwiwar Kasashen Yamma
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Daga shekarar 2020 har zuwa yanzu, wasu kasashen dake nahiyar Afirka da suka hada da Zambia da Ghana sun gamu da matsalar biyan bashi, lamarin da ya janyo hankalin mutanen duniya.

Sa’an nan wasu ‘yan siyasa da kafofin watsa labaru na kasashen yamma sun yi amfani da wannan batu wajen bayyana rashin gamsuwa game da hadin gwiwar Afirka da Sin, inda suka ce rancen da kasar Sin ta samarwa kasashen Afirka “tarkon bashi” ne, wanda ke haifar wa kasashen da matsalar biyan bashi. Amma ko abun da suka fada gaskiya ne?
A hakika, abin ba hakan yake ba. Da farko dai, kasar Sin ba ta cikin bangarorin dake samar da mafi yawan bashi ga kasashen Afirka.

  • Wajibi Ne Japan Ta Sauke Nauyi Dake Wuyanta Kan Zuba Dagwalon Ruwan Nukiliya Cikin Teku

Alkaluman da bankin duniya ya samar a shekarar 2022 sun nuna cewa, cikin bashi na dalar Amurka biliyan 696 da kasashe 49 (wadanda ake iya samun alkalumansu) dake nahiyar Afirka suka ci, bashin da hukumomin kudi na kasa da kasa (irin bankin duniya) da masu bayar da bashi na kasuwanci (misali bankunan kasa da kasa masu samar da rance) suka samar ya kai kashi 3 cikin kashi 4. Hakan ya nuna cewa wadannan hukumomi da bankuna su ne manyan bangarorin dake samar da mafi yawan bashi ga kasashen Afirka.

Ban da wannan kuma, idan an yi kokarin tantance ainihin dalilan da suka haddasa matsalar biyan bashi a kasashen Afirka, za a ga suna da sarkakiya.

Dalili na farko shi ne, mafi yawan kasashen dake nahiyar Afirka suna dogaro kan fitar da ma’adinai da sauran danyun kayayyaki wajen samun kudin shiga. Saboda haka, farashin kayayyakin da suke samar a kasuwannin duniya ya yi tasiri soai kan kudin da kasashen ke samu. Idan kudin da wata kasa ke samu ya yi yawa, to, za ta ci karin bashi. Amma zuwa lokacin da kudin shiga ya ragu, to, kasar za ta fuskanci matsala wajen biyan bashin da ta ci a baya.

Labarai Masu Nasaba

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Sa’an nan dalili na 2 shi ne, wasu manyan bankunan zuba jari (irin Citi Group) sun samu damar daukar nauyin aikin sayar da takardun bashi da gwamnatocin kasashen Afirka suka samar, inda suke kokarin daga kudin ruwa don neman karin riba. Sai dai lamarin ya zama tushen matsalar biyan bashi, saboda wasu kasashen dake nahiyar Afirka sun riga sun fara yin amfani da mafi yawan kudin da suke samu wajen biyan kudin ruwan bashin da ake binsu.

Dalili na 3 shi ne, bayan shekarar 2016, farashin danyun kayayyaki a kasuwannin duniya ya ragu. Batun nan ya kara da annobar COVID-19, lamari da ya sa dimbin kasashen dake nahiyar Afirka gamuwa da matsalar koma bayan tattalin arziki. Sai dai a wannan lokaci, baitulmalin kasar Amurka ya yi kokarin daga ruwan kudin ajiya har sau da dama, lamarin da ya haifar da karuwar darajar dalar Amurka a kasuwannin kasa da kasa, da sanya dimbin jari kwarara zuwa cikin kasar Amurka da sauran kasashe masu sukuni. Kuma a hannu na daban, batun ya sa darajar kudin kasashen Afirka ta ragu sosai, da haifar musu da karin matsin lamba a fannin biyan bashi.

Ta haka muna iya ganin cewa, bai kamata a dora wa kasar Sin laifi da cewa wai ta sa kasashen Afirka gamuwa da matsalar biyan bashi ba. Amma me ya sa wasu mutanen kasashen yamma suke fadin haka?
Dalili shi ne, domin kasar Sin ba ta son yin biyayya ga kasashen yamma. Kullum kasashe masu sukuni na yammacin duniya suna kallon kansu a matsayin masu tsara ka’idoji a duniya, inda suke bukatar kasar Sin da sauran kasashen da tattalin arzikinsu ke tasowa da su bin tsare-tsarensu wajen ba da bashi. Sai dai kasar Sin na da ra’ayin kanta.
Bayan da muka shiga cikin karni na 21, hukumomin kasashen yamma sun fara rage bashin da suke samarwa kasashen Afirka kai tsaye. A nata bangare, kasar Sin ta lura da yanayin da kasashen Afirka suke ciki na fama da koma bayan tattalin arziki, kuma ta samar da tsarin samar da rance don taimakawa kasashen Afirka raya kasa, bisa fasahohin da ta samu a fannin raya kanta. Inda a wani bangare kasar Sin ta samar da dimbin bashi masu tsawon wa’adi, wadanda ruwansu ba shi da yawa, ga kasashen Afirka kai tsaye, yayin da a bangare na daban, kasar Sin da kasashen Afirka suke hadin gwiwa a kokarin gina kayayyakin more rayuwa a Afirka, bisa yin amfani da rancen da kasar Sin ta samar. Wadannan al’amura sun nuna ra’ayin kasar Sin na kokarin amfanawa kowa yayin da ake hadin gwiwa, da neman samun ci gaban kasa mai dorewa.

Ban da haka, kasar Sin ta halarci shirin kungiyar G20 na baiwa kasashen da suke da matsalar bashi damar dakatar da biyan bashi. A sa’i daya, ba ta dauki dabarar kasashen yamma ta rage bashi bisa sanya wa kasashen Afirka wasu sharuda ba. Maimakon haka, Sin ta fi yin amfani da dabarar dakatar da biyan bashi da kudin ruwa dake tare da bashin, da tsawaita wa’adin bashi ta hanyar shawarwari, wajen taimakawa kasashen da suke da bukata, dabarar da ta yi amfani gami da samar da sakamako mai kyau, yayin da ake kokarin gwada ta.

Kasar Sin tana yin amfani da dabaru da fasahohin da ta samu, yayin da take raya tattalin arzikinta, a fannin hada-hadar kudi, wajen taimakawa kasashen Afirka fid da kansu daga wata da’irar faduwa ta yawan cin bashi amma ba tare da samun ci gaban kasa ba, da dogaro kan matakan yafe bashi, ta hanyar kyautata dabarun yin amfani da kudin da aka samu, da inganta tsare-tsaren aiki.

Sai dai a ganin kasashen yamma, matakin tamkar wata barazana ce ga babakeren da suka kafa a fannin hada-hadar kudi. Bayan da aka tabbatar da cewa tsare-tsaren da kasashen yamma suka samar ba su da amfani wajen taimakawa kasashen Afirka samun ci gaba, kasashe na yammacin duniya na ci gaba da kin amincewa da sabbin dabarun da sauran kasashe suka gabatar. Wannan mataki na taurin kai ya nuna cewa kasashen yamma sun gamu da matsalar rashin karfin gwiwa game da turbarsu ta neman ci gaba. (Bello Wang)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yanzu-Yanzu: Tinubu Ya Gana Da Kyari, Emefiele Kan Cire Tallafin Man Fetur

Next Post

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Kawo Karshen Rikicin Ukraine A Siyasance

Related

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya
Daga Birnin Sin

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

31 minutes ago
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya
Daga Birnin Sin

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

1 hour ago
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing
Daga Birnin Sin

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

2 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Amurka Dangane Da Batun Ukraine

21 hours ago
Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kadu Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Wa Hukumomi Da Jami’an Falasdinu

22 hours ago
Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana
Daga Birnin Sin

Sin Ta Samu Bunkasar Tafiye-Tafiye Cikin Gida Da Kashi 20.6% A Rabin Farko Na Bana

23 hours ago
Next Post
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Kawo Karshen Rikicin Ukraine A Siyasance

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Kawo Karshen Rikicin Ukraine A Siyasance

LABARAI MASU NASABA

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

Fim Na Kisan Kiyashin Nanjing Ya Mamaye Kasuwar Fina-Finan Sin Bisa Samun Kudin Shiga Yuan Biliyan Daya

August 2, 2025
Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

Kashi 40 Na Ƙananan Yara A Nijeriya Ke Fuskantar Barazanar Yunwa — Rahoto

August 2, 2025
Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

Yadda Kwamishinan Kano Ya Karɓi Dala $30,000 Domin Yin Belin Dilan Ƙwaya A Kotu – Rahoto

August 2, 2025
Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

Babban Jami’in MDD: Kokarin Sin A Fannin Samun Ci Gaba Mai Dorewa Na Da Matukar Alfanu Ga Yanayin Duniya

August 2, 2025
An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

An Dawo Da Wutar Lantarki A Dukkan Kauyukan Da Aka Tafka Ruwa Da Iska A Beijing

August 2, 2025
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

August 2, 2025
Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

Gwamna Fintiri Ya Karrama Kocin Super Falcons, Madugu Da Naira Miliyan 50

August 2, 2025
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

August 2, 2025
Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

Sauya Sheƙa: Sanatoci Biyu APC Ke Buƙata Wajen Samun Kashi Biyu Cikin Uku A Majalisar Dattawa

August 2, 2025
An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo

An Sake Kashe Wata Ɗalibar Jami’ar Ondo

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.