• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Kawo Karshen Rikicin Ukraine A Siyasance

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Kawo Karshen Rikicin Ukraine A Siyasance
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kasar Sin ta hannun wakilinta na musammam mai kula da harkokin Turai da Asia, Li Hui, ta yi tuntuba mai zurfi da ma musayar ra’ayi da dukkan bangarori, game da warware rikicin Ukraine a siyasance.

A ra’ayina, wannan yunkuri ya sake tabbatar da matsayin kasar Sin na son ganin tabbatuwar zaman lafiya a duniya da kaucewa goyon bayan wani bangare ko ruruta wutar rikicin.

Zuwa yanzu, an ga yadda mummunan tasirin rikicin na Ukraine ya bazu zuwa sassan duniya, tare da jefa al’ummomin da ba su ji ba, ba su gani ba cikin rudani.

Tun bayan barkewar rikicin, ake kokarin shafawa kasar Sin bakin fenti, cewa wai ta na goyon bayan wani bangare, sai dai, muradin Sin a ko da yaushe shi ne, tabbatar da wanzuwar zaman lafiya. Kuma ziyarar Li Hui kasashen Ukraine da Poland da Faransa da Jamus da Rasha da hedkwatar EU, ya tabbatar da hakan, domin ya tuntubi dukkan bangarori ba tare da ware wani ba. Adalci shi ne sauraron ra’ayin kowanne bangare tare da kokarin samar da maslahar da za ta karbu ga kowa, cikin ruwan sanyi ba tare da zubar jini ba.

Maimakon marawa Sin baya wajen yi wa tufkar hanci tare da fitar da duniya daga halin da ta shiga, kasashen duniya dake kiran kansu manya, sun nuna karara cewa, ba sa kaunar zaman lafiya ko kwanciyar hankalin duniya. An ga yadda tun bayan barkewar rikicin, Amurka da kawayenta ke ci gaba da samar da makaman yaki ga Ukraine, tare da kakabawa Rasha takunkumai.

Labarai Masu Nasaba

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Ko a baya bayan nan, sun tashi taron kungiyar G7 da matakan kara sabbin takunkumai kan Rasha.

Shi wannan ba bangaranci ba ne? Shin makaman da suke samarwa ba zubar da jini da asarar rayuka za su haifar ba? Shin takunkuman da suke sanyawa, ba kunchin rayuwa za su haifar ga al’umma ba?.

Ba sai an fada ba, hanyar da kasar Sin ta dauka ita ce za ta kai ga samar da zaman lafiya da takaita asarar rayuka da dukiya. Yayin da tallafin soji da takunkumai za su kai ga ci gaban yaki da asarar rayuka da kara dagula yanayin duniya. (Fa’iza Mustapha)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Maganar Tarkon Bashi Ta Nuna Rashin Karfin Gwiwar Kasashen Yamma

Next Post

Na Gaji Bashin Biliyoyin Kudi -Sabon Gwamnan Zamfara

Related

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa
Daga Birnin Sin

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

10 hours ago
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

11 hours ago
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

13 hours ago
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya
Daga Birnin Sin

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

14 hours ago
FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”
Daga Birnin Sin

FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”

15 hours ago
An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama
Daga Birnin Sin

An Fitar Da Sanarwar Beijing Bayan Taron Ministocin Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Wayewar Kan Bil Adama

16 hours ago
Next Post
Na Gaji Bashin Biliyoyin Kudi -Sabon Gwamnan Zamfara

Na Gaji Bashin Biliyoyin Kudi -Sabon Gwamnan Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.