• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Magoya Bayan Atiku Su Ka Hana Taron Gwamnonin PDP ‘Yan G5 Armashi A Legas

by Sulaiman
3 years ago
Atiku

Taron hasalallun gwamnonin PDP biyar masu neman a cire Shugaban PDP, Iyorchia Ayu, ya samu tangarɗa.

 

Taron wanda aka gudanar a ofishin tsohon mataimakin shugaban PDP na ƙasa, Olabode George a Ikeja, ya samu halartar dukkan gwamnoni biyar masu adawa da shugabancin Iyorchia Ayu.

  • Wike Ya Karbi Bakoncin Kwankwaso Don Kaddamar Da Bude Wasu Aiyuka A Jihar Ribas

Rashin amincewar su da Ayu ne ya kai su ga ƙaurace wa rangadin neman zaɓen shugaban ƙasa da Atiku Abubakar ya fara.

 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

Gwamnonin biyar sun haɗa da Nyesom Wike na Ribas, Samuel Ortom na Bennwai, Seyi Makinde na Oyo, Ifeanyi Ugwuanyi na Enugu da Okezie Ikpeazu na Abiya.

 

A ranar Litinin ce su ka yi sanarwar kafa ƙungiyar G5, kuma su ka kira ta da ‘Integrity Group’, wadda su ka kafa da niyyar “saita PDP kan turbar yin adalci”, a cewar su.

 

Sai dai kuma wasu gungun magoya bayan Atiku Abubakar da PDP sun hana taron gwamnonin biyar masu adawa da takarar Atiku yin armashi.

 

A wurin taron dai magoya bayan ɗan takarar sun riƙa rera take da kirarin Atiku! Atiku! Atiku! Haka su ka riƙa furtawa da ƙarfi, daidai lokacin da George ya fara bayanin cewa ba za su yi zaɓen shugaban ƙasa da na gwamnonin PDP ba, amma za su yi zaɓen ‘yan majalisar dattawa da na majalisar wakilai ta ƙasa.

 

Mambobin PDP na jihar Legas sun halarci taron, saboda sun gano akwai maƙarƙashiyar da ake zargin Bode George ya shirya, domin ya karya lagon Atiku.

 

Ɗaya daga cikin mambobin PDP a Legas mai suna Kunle Folorunsho, ya saki wani bidiyon da ke tabbatar da cewa ya halarci taron, kuma akwai hayaniyar da ta kaure wurin taron duk a cikin gajeren bidiyon.

 

Ya ce yayin da George ya ke cikin bayanin cewa su ba za su zaɓi Atiku ba, nan da nan sai shi kuma ya miƙe tsaye ya ƙalubalance shi cewa ai PDP ta na da ɗan takarar ta Atiku Abubakar, kuma shi za su zaɓa.

 

Folorunsho ya ce tun bai gama rufe baki ba sai magoya bayan George su ka dira kan sa, su ka kekketa masa riga. “Da kyar wasu magoya bayan Atiku su ka cece ni daga hannun magoya bayan Bode George,” inji shi.

 

Yayin da gwamnonin ke shirin fita daga ɗakin taro, Folorunsho ya ce dandazon jama’ar da ke waje ba su samu shiga ba sun riƙa rera “sai Atiku, sai Atiku, sai Atiku.”

 

Hakan da aka yi a cewar Folorunsho ya nuna hasalallun gwamnonin biyar ba za su iya raba kawunan ‘yan PDP a jihar Legas ba.

 

Gwamnonin biyar masu kiran kan su G5 su da sauran hasalallun magoya bayan su, sun shafe sama da awa uku, su na tattauna matakin da za su ɗauka a gaba.

 

Tsohon gwamnan Filato Jonah Jang ne ya yi magana a madadin sauran gwamnonin, kuma ya ce har yanzu su na kan matsayar da su ka cimma a taron su na Fatakwal, inda su ka ce “ƙofar yin zaman sulhu da mu a buɗe ta ke.”

 

Sauran waɗanda su ka halarci taron na Legas kuma masu goyon bayan G5 har da Sanata Olaka Nwogu, Sanata Ohuabuwa, Sanata Nazifi Suleiman, Bello Adoke, Segun Mimiko, Ayo Fayose, Donald Duke da sauran su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027
Siyasa

Tsohon Ɗan Majalisar Bayelsa Ya Shawarci Jonathan Ya Guji Neman Takara A 2027

October 17, 2025
Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu
Siyasa

Gwamnan Edo Ya Umarci Kwamishinoni Su Riƙa Sanya Hular Tinubu

October 16, 2025
Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson
Manyan Labarai

Sauya Sheƙa: Diri Da Wasu Na Guje Wa Matsalolin Da Suka Ƙirƙiro – Dickson

October 16, 2025
Next Post
Gasar Kofin Duniya: Kasar Japan Ta Lallasa Germany Da Ci 2 Da 1

Gasar Kofin Duniya: Kasar Japan Ta Lallasa Germany Da Ci 2 Da 1

LABARAI MASU NASABA

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

An Gudanar Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Tsakiyar JKS Na 20 A Beijing

October 20, 2025
Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

Gwamna Lawal Ya Jaddada Muhimmancin Haɗin Kai Wajen Yaƙi Da Ƙalubalen Tsaro

October 20, 2025
Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana

Alkaluman GDP Na Sin Sun Fadada Zuwa Kaso 5.2 A Watanni 9 Na Farkon Bana

October 20, 2025
Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta

October 20, 2025
Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar: Sirrin Kasar Sin Na Saurin Bunkasa

October 20, 2025
Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a

Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Mutane Biyu Da Suka Kashe Malamin Jami’a

October 20, 2025
Hukumar EFCC Ta Tsare Wasu Jami’anta 10 Bisa Zargin Karkatar Da Kayan Aiki

EFCC Ta Ƙwato Kadarorin Naira Biliyan 500 A Ƙarƙashin Gwamnatin Tinubu – Shettima

October 20, 2025
Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara

Kano Pillars Ta Dakatar Da Manyan Masu Horas Da ‘Yan Wasanta Saboda Rashin Nasara

October 20, 2025
Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

Bayan Kauce Hanya, Jirgi Ya Afka Cikin Teku A Hong Kong 

October 20, 2025
Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

October 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.