ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Magoya Bayan Atiku Su Ka Hana Taron Gwamnonin PDP ‘Yan G5 Armashi A Legas

by Sulaiman
4 years ago
Atiku

Taron hasalallun gwamnonin PDP biyar masu neman a cire Shugaban PDP, Iyorchia Ayu, ya samu tangarɗa.

 

Taron wanda aka gudanar a ofishin tsohon mataimakin shugaban PDP na ƙasa, Olabode George a Ikeja, ya samu halartar dukkan gwamnoni biyar masu adawa da shugabancin Iyorchia Ayu.

ADVERTISEMENT
  • Wike Ya Karbi Bakoncin Kwankwaso Don Kaddamar Da Bude Wasu Aiyuka A Jihar Ribas

Rashin amincewar su da Ayu ne ya kai su ga ƙaurace wa rangadin neman zaɓen shugaban ƙasa da Atiku Abubakar ya fara.

 

LABARAI MASU NASABA

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

Gwamnonin biyar sun haɗa da Nyesom Wike na Ribas, Samuel Ortom na Bennwai, Seyi Makinde na Oyo, Ifeanyi Ugwuanyi na Enugu da Okezie Ikpeazu na Abiya.

 

A ranar Litinin ce su ka yi sanarwar kafa ƙungiyar G5, kuma su ka kira ta da ‘Integrity Group’, wadda su ka kafa da niyyar “saita PDP kan turbar yin adalci”, a cewar su.

 

Sai dai kuma wasu gungun magoya bayan Atiku Abubakar da PDP sun hana taron gwamnonin biyar masu adawa da takarar Atiku yin armashi.

 

A wurin taron dai magoya bayan ɗan takarar sun riƙa rera take da kirarin Atiku! Atiku! Atiku! Haka su ka riƙa furtawa da ƙarfi, daidai lokacin da George ya fara bayanin cewa ba za su yi zaɓen shugaban ƙasa da na gwamnonin PDP ba, amma za su yi zaɓen ‘yan majalisar dattawa da na majalisar wakilai ta ƙasa.

 

Mambobin PDP na jihar Legas sun halarci taron, saboda sun gano akwai maƙarƙashiyar da ake zargin Bode George ya shirya, domin ya karya lagon Atiku.

 

Ɗaya daga cikin mambobin PDP a Legas mai suna Kunle Folorunsho, ya saki wani bidiyon da ke tabbatar da cewa ya halarci taron, kuma akwai hayaniyar da ta kaure wurin taron duk a cikin gajeren bidiyon.

 

Ya ce yayin da George ya ke cikin bayanin cewa su ba za su zaɓi Atiku ba, nan da nan sai shi kuma ya miƙe tsaye ya ƙalubalance shi cewa ai PDP ta na da ɗan takarar ta Atiku Abubakar, kuma shi za su zaɓa.

 

Folorunsho ya ce tun bai gama rufe baki ba sai magoya bayan George su ka dira kan sa, su ka kekketa masa riga. “Da kyar wasu magoya bayan Atiku su ka cece ni daga hannun magoya bayan Bode George,” inji shi.

 

Yayin da gwamnonin ke shirin fita daga ɗakin taro, Folorunsho ya ce dandazon jama’ar da ke waje ba su samu shiga ba sun riƙa rera “sai Atiku, sai Atiku, sai Atiku.”

 

Hakan da aka yi a cewar Folorunsho ya nuna hasalallun gwamnonin biyar ba za su iya raba kawunan ‘yan PDP a jihar Legas ba.

 

Gwamnonin biyar masu kiran kan su G5 su da sauran hasalallun magoya bayan su, sun shafe sama da awa uku, su na tattauna matakin da za su ɗauka a gaba.

 

Tsohon gwamnan Filato Jonah Jang ne ya yi magana a madadin sauran gwamnonin, kuma ya ce har yanzu su na kan matsayar da su ka cimma a taron su na Fatakwal, inda su ka ce “ƙofar yin zaman sulhu da mu a buɗe ta ke.”

 

Sauran waɗanda su ka halarci taron na Legas kuma masu goyon bayan G5 har da Sanata Olaka Nwogu, Sanata Ohuabuwa, Sanata Nazifi Suleiman, Bello Adoke, Segun Mimiko, Ayo Fayose, Donald Duke da sauran su.

Atiku
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
  • Sulaiman
    ’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
  • Sulaiman
    Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
  • Sulaiman
    Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

MASU ALAKA

2023: Gwarazan Jam’iyyu A Karon Battar Zaben Shugaban Kasa
Siyasa

PRP Ta Musanta Zargin Cewa Kwankwaso Ya Sayi Fom 69 Domin Kwace Jam’iyyar

June 22, 2026
Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP
Siyasa

Jam’iyyar APC Ta Tafka Asarar Mabiya A Gombe, Sun Bi Pantami PDP

June 22, 2026
ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027
Siyasa

ADC Ta Sake Tabbatar Da Ibrahim Khalil A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano Na 2027

June 21, 2026
Next Post
Gasar Kofin Duniya: Kasar Japan Ta Lallasa Germany Da Ci 2 Da 1

Gasar Kofin Duniya: Kasar Japan Ta Lallasa Germany Da Ci 2 Da 1

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.