ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Magoya Bayan Atiku Su Ka Hana Taron Gwamnonin PDP ‘Yan G5 Armashi A Legas

by Sulaiman
4 years ago
Atiku

Taron hasalallun gwamnonin PDP biyar masu neman a cire Shugaban PDP, Iyorchia Ayu, ya samu tangarɗa.

 

Taron wanda aka gudanar a ofishin tsohon mataimakin shugaban PDP na ƙasa, Olabode George a Ikeja, ya samu halartar dukkan gwamnoni biyar masu adawa da shugabancin Iyorchia Ayu.

ADVERTISEMENT
  • Wike Ya Karbi Bakoncin Kwankwaso Don Kaddamar Da Bude Wasu Aiyuka A Jihar Ribas

Rashin amincewar su da Ayu ne ya kai su ga ƙaurace wa rangadin neman zaɓen shugaban ƙasa da Atiku Abubakar ya fara.

 

LABARAI MASU NASABA

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

Gwamnonin biyar sun haɗa da Nyesom Wike na Ribas, Samuel Ortom na Bennwai, Seyi Makinde na Oyo, Ifeanyi Ugwuanyi na Enugu da Okezie Ikpeazu na Abiya.

 

A ranar Litinin ce su ka yi sanarwar kafa ƙungiyar G5, kuma su ka kira ta da ‘Integrity Group’, wadda su ka kafa da niyyar “saita PDP kan turbar yin adalci”, a cewar su.

 

Sai dai kuma wasu gungun magoya bayan Atiku Abubakar da PDP sun hana taron gwamnonin biyar masu adawa da takarar Atiku yin armashi.

 

A wurin taron dai magoya bayan ɗan takarar sun riƙa rera take da kirarin Atiku! Atiku! Atiku! Haka su ka riƙa furtawa da ƙarfi, daidai lokacin da George ya fara bayanin cewa ba za su yi zaɓen shugaban ƙasa da na gwamnonin PDP ba, amma za su yi zaɓen ‘yan majalisar dattawa da na majalisar wakilai ta ƙasa.

 

Mambobin PDP na jihar Legas sun halarci taron, saboda sun gano akwai maƙarƙashiyar da ake zargin Bode George ya shirya, domin ya karya lagon Atiku.

 

Ɗaya daga cikin mambobin PDP a Legas mai suna Kunle Folorunsho, ya saki wani bidiyon da ke tabbatar da cewa ya halarci taron, kuma akwai hayaniyar da ta kaure wurin taron duk a cikin gajeren bidiyon.

 

Ya ce yayin da George ya ke cikin bayanin cewa su ba za su zaɓi Atiku ba, nan da nan sai shi kuma ya miƙe tsaye ya ƙalubalance shi cewa ai PDP ta na da ɗan takarar ta Atiku Abubakar, kuma shi za su zaɓa.

 

Folorunsho ya ce tun bai gama rufe baki ba sai magoya bayan George su ka dira kan sa, su ka kekketa masa riga. “Da kyar wasu magoya bayan Atiku su ka cece ni daga hannun magoya bayan Bode George,” inji shi.

 

Yayin da gwamnonin ke shirin fita daga ɗakin taro, Folorunsho ya ce dandazon jama’ar da ke waje ba su samu shiga ba sun riƙa rera “sai Atiku, sai Atiku, sai Atiku.”

 

Hakan da aka yi a cewar Folorunsho ya nuna hasalallun gwamnonin biyar ba za su iya raba kawunan ‘yan PDP a jihar Legas ba.

 

Gwamnonin biyar masu kiran kan su G5 su da sauran hasalallun magoya bayan su, sun shafe sama da awa uku, su na tattauna matakin da za su ɗauka a gaba.

 

Tsohon gwamnan Filato Jonah Jang ne ya yi magana a madadin sauran gwamnonin, kuma ya ce har yanzu su na kan matsayar da su ka cimma a taron su na Fatakwal, inda su ka ce “ƙofar yin zaman sulhu da mu a buɗe ta ke.”

 

Sauran waɗanda su ka halarci taron na Legas kuma masu goyon bayan G5 har da Sanata Olaka Nwogu, Sanata Ohuabuwa, Sanata Nazifi Suleiman, Bello Adoke, Segun Mimiko, Ayo Fayose, Donald Duke da sauran su.

Atiku
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe
Siyasa

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM
Siyasa

‘Yan Majalisar Wakilai 6 Daga Oyo Sun Fice Daga PDP Zuwa APM

June 3, 2026
Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada
Siyasa

Gwamnatina Za Ta Mayar Da Hankali Kan Buƙatun Al’ummar Nasarawa – Wadada

June 1, 2026
Next Post
Gasar Kofin Duniya: Kasar Japan Ta Lallasa Germany Da Ci 2 Da 1

Gasar Kofin Duniya: Kasar Japan Ta Lallasa Germany Da Ci 2 Da 1

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.