ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, November 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Magoya Bayan PDP Sun Yi Zanga-Zanga Kan Sakamakon Zaben Gwamnan Kaduna

by Sadiq
3 years ago
Kaduna

‘Ya’yan jam’iyyar PDP reshen Jihar Kaduna a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar lumana a babban birnin jihar domin neman a ayyana dan takararsu Isah Ashiru a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.

A ranar Litinin din da ta gabata ne Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta bayyana dan takarar jam’iyyar APC, Sanata Uba Sani a matsayin wanda ya lashe zaben.

  • Ina So A Ko’ina A Ji Hikima Da Fasaharmu – Yusuf King
  • NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Saboda Karancin Kudi A Nijeriya

Sani ya samu kuri’u 730,002, babban abokin hamayyarsa – Ashiru na PDP – ya samu kuri’u 719,196.

ADVERTISEMENT

Amma ba su gamsu da sakamakon ba, masu zanga-zangar wadanda galibinsu mata ne sanye da bakaken kaya, sun yi zanga-zangar zuwa sakatariyar kungiyar ‘yan jarida ta Nijeriya reshen Jihar Kaduna.

Sun zargi INEC da marawa Uba Sani baya.

LABARAI MASU NASABA

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

Wadanda suka jagoranci zanga-zangar akwai tsohuwar Ministar Muhalli, Laurencia Mallam da tsohuwar shugabar mata ta PDP a jihar, Aishatu Madina.

Sun yi Allah-wadai da ayyana Sani a matsayin wanda ya lashe zaben da INEC ta yi, tare da cewar ba shi ne muradin al’ummar Jihar Kaduna.

“Dalilin da ya sa muka taru a yau shi ne mu bayyanawa duniya rashin jin dadinmu kan sakamakon zaben Jihar Kaduna,” in ji ta.

“Kowa ya san abin da aka bayyana ba wakilcin abin da al’ummar Jihar Kaduna suka zaba ba ne. Abin da ya sa muka zo nan shi ne mu jawo hankalin hukumomin da abin ya shafa, wato INEC da ya kamata ta dauki wannan aiki da su yi abin da ya kamata da kuma nuna wannan amanar da ‘yan Nijeriya suka damka musu.”

Madina ta bayyana cewa, bayanan da aka dora a na’urar sakamakon sakamakon INEC (IReV) sun nuna cewa PDP ce ta lashe zaben gwamna a Kaduna.

Ta yi kira ga jam’iyyar APC mai mulki a jihar da ta amince da cewa mutanen Kaduna sun zabi PDP.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Bai Dace Adalci Ya Zama Na Sayarwa Ba – Tinubu Ga Alƙalai 

November 17, 2025
Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Kakakin Majalisar Taraba Da Ƴan Majalisa 15 Sun Fice Daga PDP Zuwa APC

November 17, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Ɗalibai Ƴan Mata, Sun Kashe Mataimakin Shugaban Makaranta A Kebbi

November 17, 2025
Next Post
Tsohon Kakakin Majalisar Gombe, Nasiru Nono Ya Rasu A Hatsarin Mota

Tsohon Kakakin Majalisar Gombe, Nasiru Nono Ya Rasu A Hatsarin Mota

LABARAI MASU NASABA

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Adadin Motocin Da Sin Ke Fitarwa Waje Ya Karu Da Kashi 15.7 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

Farashin Kayan Abinci Na Cigaba Da Sauka A Jihohin Arewa Maso Gabas

November 17, 2025
An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

An Bude Taron Tattaunawa Kan Wayewar Kai Tsakanin Sin Da Kasashen Larabawa Karo Na 11 A Beijing

November 17, 2025
NBS

Hauhawar Farashin Kayayyaki A Nijeriya Ta Ragu Zuwa Kashi 16.065%

November 17, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

Firaministan Sin Ya Isa Rasha Domin Halartar Taron SCO

November 17, 2025
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

November 17, 2025
Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

Kudaden Kasafin Kudin Sin Sun Karu Da Kashi 0.8 Cikin Watanni 10 Na Farkon Bana

November 17, 2025
Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

Rashin Tsaro: Atiku Ya Yi Allah-wadai Da Harin Makarantar ‘Yan Mata Ta Kebbi

November 17, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

An Sanya Hannu Kan Yarjejeniyoyin Cinikayya Na Biliyoyin Kudi Yayin Baje Kolin CHTF Na Kasar Sin

November 17, 2025

MACBAN Ta Nemi Amurka Ta Cire Sunanta Daga Jerin Waɗanda Ta Ƙaƙabawa Takunkumi

November 17, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.