• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Magoya Bayan PDP Sun Yi Zanga-Zanga Kan Sakamakon Zaben Gwamnan Kaduna

by Sadiq
3 years ago
Kaduna

‘Ya’yan jam’iyyar PDP reshen Jihar Kaduna a ranar Alhamis sun gudanar da zanga-zangar lumana a babban birnin jihar domin neman a ayyana dan takararsu Isah Ashiru a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.

A ranar Litinin din da ta gabata ne Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), ta bayyana dan takarar jam’iyyar APC, Sanata Uba Sani a matsayin wanda ya lashe zaben.

  • Ina So A Ko’ina A Ji Hikima Da Fasaharmu – Yusuf King
  • NLC Za Ta Shiga Yajin Aiki Saboda Karancin Kudi A Nijeriya

Sani ya samu kuri’u 730,002, babban abokin hamayyarsa – Ashiru na PDP – ya samu kuri’u 719,196.

Amma ba su gamsu da sakamakon ba, masu zanga-zangar wadanda galibinsu mata ne sanye da bakaken kaya, sun yi zanga-zangar zuwa sakatariyar kungiyar ‘yan jarida ta Nijeriya reshen Jihar Kaduna.

Sun zargi INEC da marawa Uba Sani baya.

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Wadanda suka jagoranci zanga-zangar akwai tsohuwar Ministar Muhalli, Laurencia Mallam da tsohuwar shugabar mata ta PDP a jihar, Aishatu Madina.

Sun yi Allah-wadai da ayyana Sani a matsayin wanda ya lashe zaben da INEC ta yi, tare da cewar ba shi ne muradin al’ummar Jihar Kaduna.

“Dalilin da ya sa muka taru a yau shi ne mu bayyanawa duniya rashin jin dadinmu kan sakamakon zaben Jihar Kaduna,” in ji ta.

“Kowa ya san abin da aka bayyana ba wakilcin abin da al’ummar Jihar Kaduna suka zaba ba ne. Abin da ya sa muka zo nan shi ne mu jawo hankalin hukumomin da abin ya shafa, wato INEC da ya kamata ta dauki wannan aiki da su yi abin da ya kamata da kuma nuna wannan amanar da ‘yan Nijeriya suka damka musu.”

Madina ta bayyana cewa, bayanan da aka dora a na’urar sakamakon sakamakon INEC (IReV) sun nuna cewa PDP ce ta lashe zaben gwamna a Kaduna.

Ta yi kira ga jam’iyyar APC mai mulki a jihar da ta amince da cewa mutanen Kaduna sun zabi PDP.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Next Post
Tsohon Kakakin Majalisar Gombe, Nasiru Nono Ya Rasu A Hatsarin Mota

Tsohon Kakakin Majalisar Gombe, Nasiru Nono Ya Rasu A Hatsarin Mota

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.