• English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Mahaifina Na Ba Ni Naira 30,000 Kan Duk Yaron Da Na Sato Masa –Wata Budurwa

by Sabo Ahmad
3 years ago
Mahaifina

Asirin wata yarinya mai shekara 22, wadda ta shafe shekara biyu cir, tana satar yara, ta kai wa mahaifinta wanda shi kuma ke kai wa masu garkuwa a jihar Ondo, ya tonu.

Wadda aka kaman mai suna Adeola Omoniyi, ta shafe shekara biyu cir tana kama kananan yara tana ba mahaifinta, mai suna Ilesanmi Omoniyi, yana yin garkuwa da su, a kan ladan naira 30,000 ga kowane daya.

  • ‘Yan Sanda Sun Cafke Fursunan Da Ya Tsere Daga Gidan Yarin Kuje A Ogun

Wadda ake zargi da laifin na hada-kai wajen yin garkuwar, an garkame ta, tare da mahaifin nata a hedikwatar ‘yansanda da ke karamar hukumar Odigbo ta jihar Ondo.

Da take bayani kan yadda suka hada-kai da mahaifin nata,suke aikata wannan laifin cewa ta yi “Ni ina daga cikin masu garkuwa. Ina daukar kananan yara ne in yi garkuwa da su, idan na dauke su, sai in kai su gidanmu wajrn babana a Igbotako. Na samu sa’ar sace yara biyu, kafin in kai su maboya, sai aka kama ni”.

“Idan na kawo wa mahaifina wanda na sato, yana ba ni naira dubu talatin, a kan kowane yaro. Da irin wadannan kudin da nake samu ne nake daukar dawainiyar kaina. Ni ban san, ya yake yi da wadannan yara ba. Ni dai kawai in na sato sai in kawo masa”. “Shi ke sa ni, in sato masa yaran. Na sato yaron farko daga Ilutitun.

LABARAI MASU NASABA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

“Lokacin da na sato yaron, mahaifiyar yaron ta kwalla ihu.
Nan da nan mutane suka taso min, suka kama ni suka kai ni wajen ‘yansanda, daga nan aka wuce da ni Akure.

“Na fara satar kananan yara tare da yin garkuwa da su, tun shekara biyu da suka wuce. “Na sace yaro na farko ne a shekara ta 2021, sa i yaro na biyu a bana.” Sai dai mahaifin yarinyar da ake zargin ya ce, tuni suka yi barankan-barankan da ita.

Na san dai tana zaune a Legas. Ta kai shekara biyu a can, tun da ta tafi, sai lokacin da ta kamu da rashin lafiya aka zo da ita Igbotako.

Na dauke ta na kai ta coci, amma sai faston ya ce, sai na ba shi naira 80,000. Ai daga baya ya gaya min cewa, ta samu sauki, amma bayan ‘yan kwanaki kadan, bayan karbar wannan kudi, sai ta gudu ta bar cocin.

“Ni ce wadda nake sato kananan yara in kawo masa, in ji yarinyar. Shi kuwa uba cewa ya yi bai ba ta naira 30,000 ba. Tun kimanin wata shida bayan ta bar cocin, muke ta nemanta, sai na ji, tana satar yara.”

Bugu da kari, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan na jihar, SP Funmi Odunlami, ya tabbatar da cewa, da zarar sun gama bincikensu za su gurfanar da wadda ake zargin gaban kuliya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa
Kotu Da Ɗansanda

An Fara Binciken Batan Dan Bautar Kasa A Bayelsa

November 8, 2025
An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi
Kotu Da Ɗansanda

An Damke Mutum 11 Da Ake Zargi Da Kisan Wani Matashi A Bauchi

November 8, 2025
Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
Next Post
Adeleke Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamnan Osun Mai Ci Oyetola Na Jam’iyyar APC

Adeleke Na Jam'iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamnan Osun Mai Ci Oyetola Na Jam'iyyar APC

LABARAI MASU NASABA

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025
Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

Kamfanonin Kasa Da Kasa Na Fatan Yin Amfani Da Damammaki Na Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar–Biyar Karo Na 15 Na Sin

November 10, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

Ƴan Bindiga Sun Sace Mata 4 Masu Shayarwa, Da Shanu 50 A Kano

November 10, 2025
Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

Sin Ta Dakatar Da Jiragen Ruwan Amurka Daga Biyan Kudi Na Musammam A Tashoshinta Na Ruwa

November 10, 2025
Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Masu Zagaye Kusa Da Doron Kasa

November 10, 2025
Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

Babban Dalilin Da Ya Sa EFCC Ke Naman Tsohon Minista Ruwa A Jallo

November 10, 2025
Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

Binciken Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Ci Gaba Da Bude Kofa Mai Zurfi A Sin

November 10, 2025
Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

Gwamnati Ta Nemi Ƴan Nijeriya Su Ƙwantar Da Hankali Kan Barazanar Trump

November 10, 2025
Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Kasashen Guinea Da Saliyo

Mataimakin Firaministan Kasar Sin Zai Ziyarci Kasashen Guinea Da Saliyo

November 10, 2025
FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

FCT Ta Saka Ranar 1 Disamba Don Kammala Biyan Kudin Hajjin 2026 N7.7m

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.