• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Mahaifina Na Ba Ni Naira 30,000 Kan Duk Yaron Da Na Sato Masa –Wata Budurwa

by Sabo Ahmad
3 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
‘Mahaifina Na Ba Ni Naira 30,000 Kan Duk Yaron Da Na Sato Masa –Wata Budurwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asirin wata yarinya mai shekara 22, wadda ta shafe shekara biyu cir, tana satar yara, ta kai wa mahaifinta wanda shi kuma ke kai wa masu garkuwa a jihar Ondo, ya tonu.

Wadda aka kaman mai suna Adeola Omoniyi, ta shafe shekara biyu cir tana kama kananan yara tana ba mahaifinta, mai suna Ilesanmi Omoniyi, yana yin garkuwa da su, a kan ladan naira 30,000 ga kowane daya.

  • ‘Yan Sanda Sun Cafke Fursunan Da Ya Tsere Daga Gidan Yarin Kuje A Ogun

Wadda ake zargi da laifin na hada-kai wajen yin garkuwar, an garkame ta, tare da mahaifin nata a hedikwatar ‘yansanda da ke karamar hukumar Odigbo ta jihar Ondo.

Da take bayani kan yadda suka hada-kai da mahaifin nata,suke aikata wannan laifin cewa ta yi “Ni ina daga cikin masu garkuwa. Ina daukar kananan yara ne in yi garkuwa da su, idan na dauke su, sai in kai su gidanmu wajrn babana a Igbotako. Na samu sa’ar sace yara biyu, kafin in kai su maboya, sai aka kama ni”.

“Idan na kawo wa mahaifina wanda na sato, yana ba ni naira dubu talatin, a kan kowane yaro. Da irin wadannan kudin da nake samu ne nake daukar dawainiyar kaina. Ni ban san, ya yake yi da wadannan yara ba. Ni dai kawai in na sato sai in kawo masa”. “Shi ke sa ni, in sato masa yaran. Na sato yaron farko daga Ilutitun.

Labarai Masu Nasaba

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

“Lokacin da na sato yaron, mahaifiyar yaron ta kwalla ihu.
Nan da nan mutane suka taso min, suka kama ni suka kai ni wajen ‘yansanda, daga nan aka wuce da ni Akure.

“Na fara satar kananan yara tare da yin garkuwa da su, tun shekara biyu da suka wuce. “Na sace yaro na farko ne a shekara ta 2021, sa i yaro na biyu a bana.” Sai dai mahaifin yarinyar da ake zargin ya ce, tuni suka yi barankan-barankan da ita.

Na san dai tana zaune a Legas. Ta kai shekara biyu a can, tun da ta tafi, sai lokacin da ta kamu da rashin lafiya aka zo da ita Igbotako.

Na dauke ta na kai ta coci, amma sai faston ya ce, sai na ba shi naira 80,000. Ai daga baya ya gaya min cewa, ta samu sauki, amma bayan ‘yan kwanaki kadan, bayan karbar wannan kudi, sai ta gudu ta bar cocin.

“Ni ce wadda nake sato kananan yara in kawo masa, in ji yarinyar. Shi kuwa uba cewa ya yi bai ba ta naira 30,000 ba. Tun kimanin wata shida bayan ta bar cocin, muke ta nemanta, sai na ji, tana satar yara.”

Bugu da kari, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan na jihar, SP Funmi Odunlami, ya tabbatar da cewa, da zarar sun gama bincikensu za su gurfanar da wadda ake zargin gaban kuliya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Cafke Mutumin Da Ya Kashe Tsohuwa Ya Sayar Da Sassan Jikinta A Ogun

Next Post

Adeleke Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamnan Osun Mai Ci Oyetola Na Jam’iyyar APC

Related

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina
Kotu Da Ɗansanda

An Yanke Wa Mai Gadi Da Mai Dafa Abinci Hukuncin Kisa Kan Kashe Tsohon Kwamishina A Katsina

1 week ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Damke Mutum Shida Kan Kisan Da Aka Yi A Kasuwar Abuja

4 weeks ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

4 weeks ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

1 month ago
‘Yan Sanda Sun Kama Mutum 2 Kan Zargin Jefe Wani Direba Har Lahira A Ondo
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Gurfanar Da Lauya A Abuja A Kotu Bisa Tuhumarsa Da Aikata Sojan Gona

2 months ago
Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe
Kotu Da Ɗansanda

Wasu ‘Yan Ta’adda Dauke Da Makamai Sun Harbi Limamin Katolika A Binuwe

2 months ago
Next Post
Adeleke Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamnan Osun Mai Ci Oyetola Na Jam’iyyar APC

Adeleke Na Jam'iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamnan Osun Mai Ci Oyetola Na Jam'iyyar APC

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

Sin Ta Mika Sabon Kason Tallafin Abinci Ga Zimbabwe

August 8, 2025
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

August 8, 2025
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

August 8, 2025
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

August 8, 2025
An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

An Bude Taron Mutum-Mutumin Inji Na Duniya Na 2025 A Yau Juma’a

August 8, 2025
Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.