ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Mahaifina Na Ba Ni Naira 30,000 Kan Duk Yaron Da Na Sato Masa –Wata Budurwa

by Sabo Ahmad
4 years ago
Mahaifina

Asirin wata yarinya mai shekara 22, wadda ta shafe shekara biyu cir, tana satar yara, ta kai wa mahaifinta wanda shi kuma ke kai wa masu garkuwa a jihar Ondo, ya tonu.

Wadda aka kaman mai suna Adeola Omoniyi, ta shafe shekara biyu cir tana kama kananan yara tana ba mahaifinta, mai suna Ilesanmi Omoniyi, yana yin garkuwa da su, a kan ladan naira 30,000 ga kowane daya.

  • ‘Yan Sanda Sun Cafke Fursunan Da Ya Tsere Daga Gidan Yarin Kuje A Ogun

Wadda ake zargi da laifin na hada-kai wajen yin garkuwar, an garkame ta, tare da mahaifin nata a hedikwatar ‘yansanda da ke karamar hukumar Odigbo ta jihar Ondo.

ADVERTISEMENT

Da take bayani kan yadda suka hada-kai da mahaifin nata,suke aikata wannan laifin cewa ta yi “Ni ina daga cikin masu garkuwa. Ina daukar kananan yara ne in yi garkuwa da su, idan na dauke su, sai in kai su gidanmu wajrn babana a Igbotako. Na samu sa’ar sace yara biyu, kafin in kai su maboya, sai aka kama ni”.

“Idan na kawo wa mahaifina wanda na sato, yana ba ni naira dubu talatin, a kan kowane yaro. Da irin wadannan kudin da nake samu ne nake daukar dawainiyar kaina. Ni ban san, ya yake yi da wadannan yara ba. Ni dai kawai in na sato sai in kawo masa”. “Shi ke sa ni, in sato masa yaran. Na sato yaron farko daga Ilutitun.

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

“Lokacin da na sato yaron, mahaifiyar yaron ta kwalla ihu.
Nan da nan mutane suka taso min, suka kama ni suka kai ni wajen ‘yansanda, daga nan aka wuce da ni Akure.

“Na fara satar kananan yara tare da yin garkuwa da su, tun shekara biyu da suka wuce. “Na sace yaro na farko ne a shekara ta 2021, sa i yaro na biyu a bana.” Sai dai mahaifin yarinyar da ake zargin ya ce, tuni suka yi barankan-barankan da ita.

Na san dai tana zaune a Legas. Ta kai shekara biyu a can, tun da ta tafi, sai lokacin da ta kamu da rashin lafiya aka zo da ita Igbotako.

Na dauke ta na kai ta coci, amma sai faston ya ce, sai na ba shi naira 80,000. Ai daga baya ya gaya min cewa, ta samu sauki, amma bayan ‘yan kwanaki kadan, bayan karbar wannan kudi, sai ta gudu ta bar cocin.

“Ni ce wadda nake sato kananan yara in kawo masa, in ji yarinyar. Shi kuwa uba cewa ya yi bai ba ta naira 30,000 ba. Tun kimanin wata shida bayan ta bar cocin, muke ta nemanta, sai na ji, tana satar yara.”

Bugu da kari, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan na jihar, SP Funmi Odunlami, ya tabbatar da cewa, da zarar sun gama bincikensu za su gurfanar da wadda ake zargin gaban kuliya.

Mahaifina
Sabo Ahmad
+ postsBio
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    An Gurfanar Da Mutum 3 Bisa Laifin Lakada Wa Wani Duka Har Lahira
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Dalilin Da Ya Sa Kotu Ta Tasa Keyar Dakta Idris Dutsen Tanshi Zuwa Gidan Yari
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Uwa Ta Mutu A Kokarin Raba Fada Tsakanin ‘Ya’yanta A Abuja
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    ’Yan Fashi Sun Yi Shigar Injiniyoyi, Sun Saci Manyan Na’urorin Sadarwa

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
Adeleke Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamnan Osun Mai Ci Oyetola Na Jam’iyyar APC

Adeleke Na Jam'iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamnan Osun Mai Ci Oyetola Na Jam'iyyar APC

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.