ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

‘Mahaifina Na Ba Ni Naira 30,000 Kan Duk Yaron Da Na Sato Masa –Wata Budurwa

by Sabo Ahmad
4 years ago
Mahaifina

Asirin wata yarinya mai shekara 22, wadda ta shafe shekara biyu cir, tana satar yara, ta kai wa mahaifinta wanda shi kuma ke kai wa masu garkuwa a jihar Ondo, ya tonu.

Wadda aka kaman mai suna Adeola Omoniyi, ta shafe shekara biyu cir tana kama kananan yara tana ba mahaifinta, mai suna Ilesanmi Omoniyi, yana yin garkuwa da su, a kan ladan naira 30,000 ga kowane daya.

  • ‘Yan Sanda Sun Cafke Fursunan Da Ya Tsere Daga Gidan Yarin Kuje A Ogun

Wadda ake zargi da laifin na hada-kai wajen yin garkuwar, an garkame ta, tare da mahaifin nata a hedikwatar ‘yansanda da ke karamar hukumar Odigbo ta jihar Ondo.

ADVERTISEMENT

Da take bayani kan yadda suka hada-kai da mahaifin nata,suke aikata wannan laifin cewa ta yi “Ni ina daga cikin masu garkuwa. Ina daukar kananan yara ne in yi garkuwa da su, idan na dauke su, sai in kai su gidanmu wajrn babana a Igbotako. Na samu sa’ar sace yara biyu, kafin in kai su maboya, sai aka kama ni”.

“Idan na kawo wa mahaifina wanda na sato, yana ba ni naira dubu talatin, a kan kowane yaro. Da irin wadannan kudin da nake samu ne nake daukar dawainiyar kaina. Ni ban san, ya yake yi da wadannan yara ba. Ni dai kawai in na sato sai in kawo masa”. “Shi ke sa ni, in sato masa yaran. Na sato yaron farko daga Ilutitun.

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

“Lokacin da na sato yaron, mahaifiyar yaron ta kwalla ihu.
Nan da nan mutane suka taso min, suka kama ni suka kai ni wajen ‘yansanda, daga nan aka wuce da ni Akure.

“Na fara satar kananan yara tare da yin garkuwa da su, tun shekara biyu da suka wuce. “Na sace yaro na farko ne a shekara ta 2021, sa i yaro na biyu a bana.” Sai dai mahaifin yarinyar da ake zargin ya ce, tuni suka yi barankan-barankan da ita.

Na san dai tana zaune a Legas. Ta kai shekara biyu a can, tun da ta tafi, sai lokacin da ta kamu da rashin lafiya aka zo da ita Igbotako.

Na dauke ta na kai ta coci, amma sai faston ya ce, sai na ba shi naira 80,000. Ai daga baya ya gaya min cewa, ta samu sauki, amma bayan ‘yan kwanaki kadan, bayan karbar wannan kudi, sai ta gudu ta bar cocin.

“Ni ce wadda nake sato kananan yara in kawo masa, in ji yarinyar. Shi kuwa uba cewa ya yi bai ba ta naira 30,000 ba. Tun kimanin wata shida bayan ta bar cocin, muke ta nemanta, sai na ji, tana satar yara.”

Bugu da kari, jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan na jihar, SP Funmi Odunlami, ya tabbatar da cewa, da zarar sun gama bincikensu za su gurfanar da wadda ake zargin gaban kuliya.

Mahaifina
Sabo Ahmad
+ postsBio
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    An Gurfanar Da Mutum 3 Bisa Laifin Lakada Wa Wani Duka Har Lahira
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Dalilin Da Ya Sa Kotu Ta Tasa Keyar Dakta Idris Dutsen Tanshi Zuwa Gidan Yari
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    Uwa Ta Mutu A Kokarin Raba Fada Tsakanin ‘Ya’yanta A Abuja
  • Sabo Ahmad
    https://hausa.leadership.ng/author/sabo-ahmad/
    ’Yan Fashi Sun Yi Shigar Injiniyoyi, Sun Saci Manyan Na’urorin Sadarwa

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
Adeleke Na Jam’iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamnan Osun Mai Ci Oyetola Na Jam’iyyar APC

Adeleke Na Jam'iyyar PDP Ya Kayar Da Gwamnan Osun Mai Ci Oyetola Na Jam'iyyar APC

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.