• English
  • Business News
Monday, September 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ba Ta Da Hurumin Dakatar Da Shugaban Hukumar Zabe Ta Jiha – Shugaban NBA

by Muhammad Awwal Umar
3 years ago
in Labarai
0
Majalisa Ba Ta Da Hurumin Dakatar Da Shugaban Hukumar Zabe Ta Jiha – Shugaban NBA
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon dambawar zaben kananan hukumomin Neja da majalisar dokokin jiha ta shelanta dakatar da shugaban hukumar zabe ta jiha, Alhaji Baba Aminu.

Shugaban kungiyar lauyoyin jihar, Mohammed Waziri Abdulkadir ya bayyana cewar majalisar ta yi hawan kawara ga dokar zabe ta jiha sashi na 201 da 197 na shekarar 1999 da aka yiwa gyaran fuska, dan haka ya nemi majalisar ta canja tunanin ta.

  • Manchester United Ta Kafa Mummunan Tarihi A Watannin Oktoba
  • Yadda Ake Tabbatar Da Ci Gaba Mai Inganci A Birnin Shanghai Na Kasar Sin

Majalisar ta bayyana dakatar da shugaban hukumar zabe ta jiha inda suka zarge shi da rashin cancantar shugabantar hukumar NISIEC.

Alh. Baba Aminu ya halarci majalisar a wani gayyatar da tai mai saboda maganar ci gaba da shirye-shiryen zaben kananan hukumomi da hukumar ke aiwatarwa a halin yanzu inda majalisar ta nemi a dakatar da zaben wanda za a gudanar a watan Nuwambar wannan shekarar.

Hukumar NISIEC na shirya zaben ne sakamakon wa’adin shugabannin kananan hukumomi zai kare watanni uku masu zuwa, kuma majalisar ta nemi a dakatar da shirya zaben sakamakon karar rashin amincewar zaben da jam’iyyar PDP ta shirgar a babban kotun tarayya da ke minna nakin amincewa da zaben a halin yanzu.

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Sakamakon tambayoyin manema labarai ga shugaban kungiyar lauyoyin jiha, Mohammed Waziri Abdulkakir ya bayyana cewar majalisar bata da hurumin dakatar da shugaban hukumar zaben, domin dakatarwar ya sabawa doka kuma bai kan ka’idar doka.

“Ba su da hurumin dakatar shugaban hukumar zabe, gwamna ne kawai ke da hurumin neman tsige shugaban ko dakatarwar, sannana samu kashi biyu bisa uku na ‘yan majalisar su amince da hakan”.

Yanzu labaran da muke samu awani zaman majalisar wanda gefe daya ne suka zartas da hukuncin.

Kora ko dakatarwar na majalisar ya fito ne daga gwamna ko majalisar dokokin ne tai gaban kan ta na dakatarwar.

Lauyan ya shawarci majalisar da su bi dokar da ta samar da hukumar da kuma bai wa hukumar shugabanci da sakataren hukumar da sauran manyan masu mukamai a hukumar, ya jawo hankalin majalisar akan dokar 1999 da ta samar da hukumar.

“Bari in sake tambaya, shin dakatarwar daga majalisar ne, domin ba wanda ke da hurumin dakatarwa ko korar shugaban hukumar zabe da sakataren hukumar sai gwamna.

Sashi na 201 ya bayyana cewar sai kashi biyu bisa uku na majalisar ta amince da kudurin, yanzu abin da wannan ke magana gwamna ne yake da hurumin neman majalisar dokokin da ta cire shugaban hukumar”.

Saboda haka abinda dokar ya ce, maganar korar shugaban hukumar zabe gwamna kawai ke da wannan damar, ina kira ga majalisar dokokin da su canja tunanin su akan korar shugaban hukumar zabe.

Abdulkadir ya bayyana cewar a zaman kungiyar na gaba za ta tattauna wannan batu dan samar da matsayar doka, dan nuna matsayin su akan irin wannan matsalar saboda gaba.

Tunda farko shugaban majalisar dokokin jiha, Barista Abdullahi Bawa Wuse ya nemi gwamnatin jiha da hukumar zaben su dakatar da batun zaben har sai bayan kamala shari’ar da ke gaban kotu kan yiwuwar gudanar da zaben, wanda gwamnati da hukumar ke cigaba da shirye-shiryen gudanar da zaben.

Kungiyar jam’iyyun siyasa da ke jihar ( IPAC) bisa jagorancin Hon. Bello Maikujeri ta bayyana gamsuwar takan matsayin hukumar na gudanar da zaben kamar yadda shirye-shiryen ke gudana a halin yanzu.

A wani karin hasken da ya yi wa manema labarai, ya ce sanin kowa ne shugabannin kananan hukumomi na yin shekaru biyu ne a sake zabe, amma saboda sabon dokar da majalisar dokokin jiha suka yi, ya bai wa kananan hukumomi damar wa’adin shekaru uku, yanzu wa’adin su zai kare cikin watan Disamba, ka ga ke dole ne a yi zabe tun da sabon dokar ya ce ba rikon kwarya, in ban da PDP dukkanin jam’iyyun siyasar har APC mai Mulki sun amince da maganar zaben.

Saboda wannan dambarwar da majalisa ke son kawo wa son zuciya kawai amma ba maganar ci gaban dimukuradiyya ba.

Kamar yadda hukumar zaben ta ba mu damar ci gaba da shirye-shirye mafi yawan jam’iyyu sun kammala zaben fidda gwani kuma a shirye muke don fara yakin neman zabe kamar yadda aka tsara.

Wasu rahotanni dai sun tabbatar da cewar gwamnati ta sanya kwamiti don nazartar sabon dokar da kuma yiwuwar yin zaben ko rashin sa.

Tsoron da jama’a ke yi kan zaben yana da nasaba da babban zaben kasa na shekarar 2023 mai da ake zargin idan zaben ya gudana yana iya kara barazana da fargaba a samun babban zaben mai zuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kananan HukumomimajalisaNBAShugaba
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manchester United Ta Kafa Mummunan Tarihi A Watannin Oktoba

Next Post

An Gano Mutumin Da Yake Kara Tsawo Duk Bayan Wata Uku Zuwa Hudu

Related

Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa
Labarai

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

50 minutes ago
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
Labarai

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

2 hours ago
Neja
Labarai

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

3 hours ago
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya
Labarai

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

3 hours ago
Zamfara
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

5 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi

6 hours ago
Next Post
An Gano Mutumin Da Yake Kara Tsawo Duk Bayan Wata Uku Zuwa Hudu

An Gano Mutumin Da Yake Kara Tsawo Duk Bayan Wata Uku Zuwa Hudu

LABARAI MASU NASABA

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

September 15, 2025
Sanata Natasha Za Ta Fuskanci Hukunci Daga Kwamitin Ɗa’a Na Majalisa

Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa

September 15, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

September 15, 2025
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

September 15, 2025
Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

Mujallar Qiushi Za Ta Wallafa Sharhin Xi Jinping Mai Taken “Zurfafa Dunkulewar Kasuwannin Kasa Ta Bai Daya”

September 15, 2025
Neja

Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar

September 15, 2025
An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

An Karrama Farfesa Adamu Gwarzo Kan Gudummawarsa Ga Bunƙasa Ilimin Jami’a A Nijeriya

September 15, 2025
Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet

September 15, 2025
Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara

September 15, 2025
Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

September 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.