ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Manchester United Ta Kafa Mummunan Tarihi A Watannin Oktoba

An Yi Wa Manchester United Dukan Kawo Wuka

by Abba Ibrahim Wada
4 years ago
Manchester United

A tarihi, kungiyar kwallon kafa ta Manchester United tana yin rashin nasara da gagarumin rinjaye a wasannin da take yin rashin nasara a watannin Oktoba wanda hakan ya zamo wani abun mamaki.

A ranar Lahadin da ta gabata kungiyar kwallon kafa ta Manchester City ta doke Manchester United da ci 6-3 a wasan hamayya a gasar Premier League karawar mako na takwas kakar wasa ta 2022 zuwa 2023.

  • Asirin Barawon Da Ake Zargin Ya Sace Kudin Da Ake Tarawa A Coci Ya Tonu
  • Shin Gwamnatin Birtaniya Ta Saurari Kiran Kungiyar OAS Kan Tsibiran Malvinas

‘Yan wasa Phil Poden da Erling Haaland kowanne ya ci kwallaye uku-uku a raga, sai dai Manchester United ta ci kwallo biyu ta hannun Anthony Martial da kuma sabon dan wasa Antony De Santos.

ADVERTISEMENT

Sannan magoya bayan Manchester United ba za su manta da watan na Oktoba da kuma sakamakon karawar da suka yi a Etihad ba saboda kungiyar ta buga wasanni hudu a baya tana samun nasara kafin wannan wasan na ranar Lahadi.

Amma kuma kafin wannan fafatawar an ci Manchester United kwallaye da yawa a gasar Premier kuma a cikin watan Oktoba kuma tun bayan da aka sauya fasalin gasar Premier United a shekarar 1992 zuwa 1993 an zazzaga kwallaye da yawa a ragar Manchester United a wasanni shida kenan kuma duk a cikin watan Oktoba Mummunan Tarihin Manchester United A Watannin Oktoba Kafin fara wasan a kakar wasa ta 1996 zuwa1997 Manchester United ta doke Newcastle United da ci 4-0 a gasar cin kofin Charity Shield, karawar da ake yi domin bude labulen kakar gasar Premier League.

LABARAI MASU NASABA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

Wata biyu tsakani shi ne suka sake fuskantar juna karkashin jagorancin Sir AledFerguson, in da Newcastle ta ci United 5-0 a St James Park kuma tun kafin hutun rabin lokaci Darren Peacock da Dabid Ginola suka ci kwallo kowanne.

Daga baya Les Ferdinand ya kara, bayanda suka koma zagaye na biyu, sai dan wasa Alan Shearer ya ci na hudu daga baya Philippe Albert ya kara kwallo ta biyar a raga.

A ranar 3 ga watan Oktoban shekarar 1999 Manchester United ta ziyarci filin wasa na Stamford Bridge a lokacin da take kan ganiyarta, bayan da ta yi wasa 29 ba a doke taba tun daga Disambar shekarar 1998.

A lokacin tana rike da kofin, sai dai cikin dakika 30 da fara wasa Gus Poyet ya zura kwallo a ragar Manchester United sannan mai tsaron ragar Manchester United Massimo Talbi ya je ya yi karo da mai tsaron baya Denis Irwin, inda Poyet ya samu kwallo cikin ruwan sanyi ya zura a raga ba kowa a ciki.

Har ila yau, minti 15 tsakani Chris Sutton ya kara kwallo ta biyu sannan an kuma bai wa Nicky Butt jan kati, bayan keta da ya yi wa Dennis Wise sannan daga baya Poyet ya ci kwallo tare da Jody Morris, ya yin da Henning Berg na Manchester United ya ci gida aka tashi karawar Chelsea da nasara 5-0.

Sannan a ranar 23 ga watan Oktoban shekara ta 2012 dan wasa Mario Balotelli ne ya fara cin Manchester United a wannan wasan na hamayya, haka kuma aka je hutu, kungiyar da Roberto Mancini ke jan ragama tana da 1-0.

Bayan da aka koma zagaye na biyu kuma Manchester United tana gara kwallo, sai aka bai wa Jonny Ebans jan kati minti biyu da komawa zagaye na biyu, bayan keta da ya yi wa dan wasa Balotelli.

Daga nan aka ga barakar Manchester United, inda Balotelli ya kara, sannan Sergio Aguero ya zura kwallo a raga – wasa ya koma3-0 sai dan wasan Manchester United Darren Fletcher ya zare wa Manchester United kwallo daya.

Saura minti daya lokaci ya cika kafin alkalin wasa ya tashi karawar, sai Manchester City ta kara uku a raga ta hannun Edin Dzeko da ya ci biyu da kuma Dabid Silba kuma shi ne was an da aka doke Manchester United kwallaye da yawa a gida tun bayan 5-0 da Manchester City ta yi mata a 1955.

Kuma karon farko da aka ci Manchester United shida a filin wasa na Old Trafford, tun bayan 6-0 da Huddesfield Town ta yi da wanda ta sha kashi da ci 7-4 a hannun Newcastle United kwana hudu tsakani duk a 1930.

Bugu da kari, a ranar 4 ga watan Oktoban shekara ta 2020 Bruno Fernandes ya fara ci wa Manchester United kwallo a bugun fenareti a minti na biyu da fara wasa, bayan da Dabinson Sanchez ya yi wa Anthony Martial keta.

Daga baya aka bai wa Anthony Martial jan kati a minti na 20, bayan ketar da ya yi w aErik Lamela a lokacin ana cin Manchester United 2-1 sannan Tanguy Ndombele da kuma Son Heung-min ne suka ci wa kungiyar da Jose Mourinho ke jan ragama kwallayen.

Kafin hutu Harry Kane da Son suka kara cin kwallae, inda Tottenham ke da 4-1.

Suna komawa zagaye na biyu Sege Aurierya kara na biyar, sannan Kane ya ci na biyu a wasan kuma na shida a karawar.

Suma Liberpool, a ranar 24 ga watan Oktoban shekara ta 2021 Shekara 10 da kwana daya bayan da Manchester United ta sha kashi a hannun City 6-1 a filin wasa na Old Trafford sai tawagar ‘yan wasan Jurgen Klopp ta ziyarci United a wasan Premier, kuma minti biyar da fara wasa sai Naby Keita ya ci wa Liberpool kwallo.

Dan wasa Diogo Jota ya kara ta biyu a minti na 13 daga nan Mohamed Salah ya zura biyu a raga sai dai magoya bayan United sun yiwa ‘yan wasansu ihu tun kafin a tafi hutun rabin lokaci a gaban ‘yan kallo 73,000 sannan bayan da suka koma zagaye na biyu ne Salah ya ci kwallo ta uku rigis a karawar.

Manchester United
Abba Ibrahim Wada
+ postsBio
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Har Yanzu Nijeriya Tana Fatan Zuwa Kofin Duniya Na 2026
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Mece Ce Matsalar Real Madrid? 
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Abba Ibrahim Wada
    https://hausa.leadership.ng/author/abba-ibrahim-wada/
    Ko Ka San Dalilin Da Zai Bai Wa Nijeriya Damar Zuwa Gasar Cin Kofin Duniya?

MASU ALAKA

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
Wasanni

FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64

July 12, 2026
Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
Wasanni

Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare

July 11, 2026
Wasanni

Ronaldo Da Ƴanwasan Da Suka Buga Kofin Duniya Na Ƙarshe A Rayuwarsu

July 11, 2026
Next Post
Majalisa Ba Ta Da Hurumin Dakatar Da Shugaban Hukumar Zabe Ta Jiha – Shugaban NBA

Majalisa Ba Ta Da Hurumin Dakatar Da Shugaban Hukumar Zabe Ta Jiha - Shugaban NBA

LABARAI MASU NASABA

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

Majalisa Ta Ba da Tallafin ₦50m Ga Iyalan Malamai Da Jami’an Tsaro Da Aka Kashe A Aikin Ceto A Oyo

July 15, 2026
Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

Xi Ya Bukaci A Mayar Da Hankali Kan Bukatun Jama’a Yayin Rangadin Da Ya Yi A Shanghai

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

Ci Gaban Fasaha Na Hidimtawa Jama’a Cikin Kowane Yanayi A Kasar Sin

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.