• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta 10: Gwamnoni 25 Sun Mara Wa Akpabio Da Barau Baya

bySadiq
2 years ago
Majalisa

Gabanin shiga zaben Majalisar Dokokin kasar nan karo na 10 a ranar Talata 13 ga watan Yuni 2023, gwamnonin jihohi akalla 25 ne suka zabi Sanata Godswill Obong Akpabio, da Sanata Jibrin Barau a matsayin shugaban majalisar dattawa da mataimakin shugaban majalisar dattawa na majalisa ta 10.

Gwamnonin sun hada kai da zababbun Sanatoci na manyan jam’iyyu uku: APC, PDP da kuma jam’iyyar LP domin mara wa ‘yan takarar baya.

  • Sin Ta Bude Ofishin Jakadanci S Kasar Honduras.
  • Xi Jinping: Ana Kokarin Yaki Da Yaduwar Hamada A Sin Don Bude Sabon Babi

Daga cikin gwamnonin guda 25 da ke goyon bayan Akpabio sun hada da Gwamnonin Kwara, Nasarawa, Benue, Ogun, Oyo, Legas, Ekiti, Osun, Kogi, Ribas, Kuros Riba, Kaduna, Borno, Ebonyi da kuma Ondo.

Gwamnonin, wadanda akasarinsu na Jihohin da ke karkashin Jam’iyyar APC ne, sun ci gaba da cewa, sun yi kakkausar suka wajen amincewa da shawarar da Kwamitin Ayyuka na Kasa (NWC) na jam’iyya mai mulki ya dauka.

Gwamnonin sun kara da cewa jam’iyyar APC ta yanke shawara mafi inganci da za ta inganta zaman lafiya a hukumomi da kuma gudanar da harkokin majalisa cikin lumana a majalisa ta kasa ta 10 nan da shekara hudu masu zuwa.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Musamman a lokacin da Akpabio ya ziyarci Gwamna Yahaya Bello a Jihar Kogi, gwamnan ya bayyana burin Akpabio da Barau na lashe kujerun shugaban majalisar dattawa da mataimaki a majalisa ta 10.

Ya kuma bayyana cewa Akpabio, tsohon ministan harkokin Neja-Delta, shi ne abin koyinsa, inda ya kara da cewa salon mulkin Sanatan da ba a saba gani ba a matsayinsa na gwamnan Jihar Akwa Ibom, ya sa ya so ya zama kamar tsohon gwamnan.

Gwamnan Kogi ya ce zai yi kokarin ganin an samu kwanciyar hankali a fadar shugaban kasa Bola Tinubu.

Har ila yau, gwamnan Jihar Ekiti, Biodun Oyebanji, ya ce zababbun sanatoci da sauran masu ruwa da tsaki a jihar ne ke goyon bayan takarar Sanata Akpabio don ya gaji Ahmad Lawan a matsayin shugaban majalisar dattawa.

Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya kuma bayyana cewa gwamnonin APC na Arewa cewa sun kuduri aniyar mara wa shugaba Bola Tinubu baya na zaben shugabannin majalisar dokokin kasar nan.

Gwamna Babajide Sanwo a Jihar Legas ya ce yana fatan Majalisar ta 10 za ta kasance ne kan “Sarfafa sabbin dokoki” don inganta abubuwan da aka riga aka yi a Majalisar ta tara.

Ya bayyana kungiyar zababbun Sanatoci a fadin jam’iyyar a matsayin “kungiyar da ta yi aiki sosai”.

Har ila yau, wata majiya ta kusa da Gwamnonin APC ta yi nuni da cewa, suna sa ran ganin an samu zaman lafiya, kwanciyar hankali a zauren majalisar ta 10.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Da Dumi-Dumi: Tinubu Ya Kama Aiki A Fadar Shugaban Kasa

Kotu Ta Bukaci Masu Kalubalantar Nasarar Tinubu Su Biya Miliyan 10 Kowannensu

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version