• English
  • Business News
Friday, August 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta 10: Gwamnoni 25 Sun Mara Wa Akpabio Da Barau Baya

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Majalisa Ta 10: Gwamnoni 25 Sun Mara Wa Akpabio Da Barau Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gabanin shiga zaben Majalisar Dokokin kasar nan karo na 10 a ranar Talata 13 ga watan Yuni 2023, gwamnonin jihohi akalla 25 ne suka zabi Sanata Godswill Obong Akpabio, da Sanata Jibrin Barau a matsayin shugaban majalisar dattawa da mataimakin shugaban majalisar dattawa na majalisa ta 10.

Gwamnonin sun hada kai da zababbun Sanatoci na manyan jam’iyyu uku: APC, PDP da kuma jam’iyyar LP domin mara wa ‘yan takarar baya.

  • Sin Ta Bude Ofishin Jakadanci S Kasar Honduras.
  • Xi Jinping: Ana Kokarin Yaki Da Yaduwar Hamada A Sin Don Bude Sabon Babi

Daga cikin gwamnonin guda 25 da ke goyon bayan Akpabio sun hada da Gwamnonin Kwara, Nasarawa, Benue, Ogun, Oyo, Legas, Ekiti, Osun, Kogi, Ribas, Kuros Riba, Kaduna, Borno, Ebonyi da kuma Ondo.

Gwamnonin, wadanda akasarinsu na Jihohin da ke karkashin Jam’iyyar APC ne, sun ci gaba da cewa, sun yi kakkausar suka wajen amincewa da shawarar da Kwamitin Ayyuka na Kasa (NWC) na jam’iyya mai mulki ya dauka.

Gwamnonin sun kara da cewa jam’iyyar APC ta yanke shawara mafi inganci da za ta inganta zaman lafiya a hukumomi da kuma gudanar da harkokin majalisa cikin lumana a majalisa ta kasa ta 10 nan da shekara hudu masu zuwa.

Labarai Masu Nasaba

Manyan Jami’ai A Ma’aikatar Tsaro Ta Cikin Gida Za Su Ci Gaba Da Karɓar Albashi Har Ƙarshen Rayuwa

Shugaban NPA, Dantsoho Ya Zama Mataimakin Shugaban Kungiyar Tashoshin Ruwa Ta Duniya

Musamman a lokacin da Akpabio ya ziyarci Gwamna Yahaya Bello a Jihar Kogi, gwamnan ya bayyana burin Akpabio da Barau na lashe kujerun shugaban majalisar dattawa da mataimaki a majalisa ta 10.

Ya kuma bayyana cewa Akpabio, tsohon ministan harkokin Neja-Delta, shi ne abin koyinsa, inda ya kara da cewa salon mulkin Sanatan da ba a saba gani ba a matsayinsa na gwamnan Jihar Akwa Ibom, ya sa ya so ya zama kamar tsohon gwamnan.

Gwamnan Kogi ya ce zai yi kokarin ganin an samu kwanciyar hankali a fadar shugaban kasa Bola Tinubu.

Har ila yau, gwamnan Jihar Ekiti, Biodun Oyebanji, ya ce zababbun sanatoci da sauran masu ruwa da tsaki a jihar ne ke goyon bayan takarar Sanata Akpabio don ya gaji Ahmad Lawan a matsayin shugaban majalisar dattawa.

Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya kuma bayyana cewa gwamnonin APC na Arewa cewa sun kuduri aniyar mara wa shugaba Bola Tinubu baya na zaben shugabannin majalisar dokokin kasar nan.

Gwamna Babajide Sanwo a Jihar Legas ya ce yana fatan Majalisar ta 10 za ta kasance ne kan “Sarfafa sabbin dokoki” don inganta abubuwan da aka riga aka yi a Majalisar ta tara.

Ya bayyana kungiyar zababbun Sanatoci a fadin jam’iyyar a matsayin “kungiyar da ta yi aiki sosai”.

Har ila yau, wata majiya ta kusa da Gwamnonin APC ta yi nuni da cewa, suna sa ran ganin an samu zaman lafiya, kwanciyar hankali a zauren majalisar ta 10.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AkpabioBarauGwamnoniMajalisa Ta 10
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bude Ofishin Jakadanci S Kasar Honduras

Next Post

Kotu Ta Bukaci Masu Kalubalantar Nasarar Tinubu Su Biya Miliyan 10 Kowannensu

Related

Manyan Jami’ai A Ma’aikatar Tsaro Ta Cikin Gida Za Su Ci Gaba Da Karɓar Albashi Har Ƙarshen Rayuwa
Labarai

Manyan Jami’ai A Ma’aikatar Tsaro Ta Cikin Gida Za Su Ci Gaba Da Karɓar Albashi Har Ƙarshen Rayuwa

2 hours ago
Shugaban NPA, Dantsoho Ya Zama Mataimakin Shugaban Kungiyar Tashoshin Ruwa Ta Duniya
Labarai

Shugaban NPA, Dantsoho Ya Zama Mataimakin Shugaban Kungiyar Tashoshin Ruwa Ta Duniya

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Karrama Nafisa ‘Yar Shekara 17 Da Ta Zama Lamba 1 A Gasar Turanci Ta Duniya 
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Karrama Nafisa ‘Yar Shekara 17 Da Ta Zama Lamba 1 A Gasar Turanci Ta Duniya 

5 hours ago
Ƙungiyar Samar Da Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Ta Arewa Ta Ƙaddamar Da Shugabanninta A Kaduna
Labarai

Ƙungiyar Samar Da Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Ta Arewa Ta Ƙaddamar Da Shugabanninta A Kaduna

6 hours ago
Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 
Manyan Labarai

Gwamnan Kebbi Ya Naɗa Sanusi Mika’ilu Sami A Matsayin Sabon Sarkin Zuru 

6 hours ago
Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho
Manyan Labarai

Gwamnatin Bauchi Ta Amince Da N32,000 A Matsayin Mafi Karancin Kuɗin Fansho

8 hours ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: Tinubu Ya Kama Aiki A Fadar Shugaban Kasa

Kotu Ta Bukaci Masu Kalubalantar Nasarar Tinubu Su Biya Miliyan 10 Kowannensu

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Wasu Kafofin Watsa Labarun Japan Suke Kokarin Musanta Kisan Kiyashin Nanjing?

Me Ya Sa Wasu Kafofin Watsa Labarun Japan Suke Kokarin Musanta Kisan Kiyashin Nanjing?

August 28, 2025
Manyan Jami’ai A Ma’aikatar Tsaro Ta Cikin Gida Za Su Ci Gaba Da Karɓar Albashi Har Ƙarshen Rayuwa

Manyan Jami’ai A Ma’aikatar Tsaro Ta Cikin Gida Za Su Ci Gaba Da Karɓar Albashi Har Ƙarshen Rayuwa

August 28, 2025
Baki Kusan 50 Daga Kasashe 30 Na Turai Za Su Halarci Bikin Tunawa Da Nasarar Yakin Turjiyar Sinawa Kan Zaluncin Japanawa

Baki Kusan 50 Daga Kasashe 30 Na Turai Za Su Halarci Bikin Tunawa Da Nasarar Yakin Turjiyar Sinawa Kan Zaluncin Japanawa

August 28, 2025
Shugaban NPA, Dantsoho Ya Zama Mataimakin Shugaban Kungiyar Tashoshin Ruwa Ta Duniya

Shugaban NPA, Dantsoho Ya Zama Mataimakin Shugaban Kungiyar Tashoshin Ruwa Ta Duniya

August 28, 2025
An Bude Bikin Nune-Nune Na Masana’antar Manyan Bayanai Ta Big Data A Kudu Maso Yammacin Sin

An Bude Bikin Nune-Nune Na Masana’antar Manyan Bayanai Ta Big Data A Kudu Maso Yammacin Sin

August 28, 2025
AC Milan Ta Amince Da Biyan Yuro Miliyan 36 Domin Daukar Nkunku Daga Chelsea

AC Milan Ta Amince Da Biyan Yuro Miliyan 36 Domin Daukar Nkunku Daga Chelsea

August 28, 2025
Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Shigo Da Su Daga Kasashe Masu Karancin Ci Gaba Na Afrika Ya Karu Da Kaso 10.2 Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Yawan Kayayyakin Da Sin Ta Shigo Da Su Daga Kasashe Masu Karancin Ci Gaba Na Afrika Ya Karu Da Kaso 10.2 Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

August 28, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Karrama Nafisa ‘Yar Shekara 17 Da Ta Zama Lamba 1 A Gasar Turanci Ta Duniya 

Gwamnatin Tarayya Ta Karrama Nafisa ‘Yar Shekara 17 Da Ta Zama Lamba 1 A Gasar Turanci Ta Duniya 

August 28, 2025
Shugabannin Kasashe 26 Za Su Halarci Bikin Ranar Nasarar Yakin Turjiyar Sinawa A Ran 3 Ga Satumba

Shugabannin Kasashe 26 Za Su Halarci Bikin Ranar Nasarar Yakin Turjiyar Sinawa A Ran 3 Ga Satumba

August 28, 2025
Ƙungiyar Samar Da Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Ta Arewa Ta Ƙaddamar Da Shugabanninta A Kaduna

Ƙungiyar Samar Da Haɗin Kai Da Zaman Lafiya Ta Arewa Ta Ƙaddamar Da Shugabanninta A Kaduna

August 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.