• English
  • Business News
Saturday, July 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta 10: Gwamnoni 25 Sun Mara Wa Akpabio Da Barau Baya

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Majalisa Ta 10: Gwamnoni 25 Sun Mara Wa Akpabio Da Barau Baya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gabanin shiga zaben Majalisar Dokokin kasar nan karo na 10 a ranar Talata 13 ga watan Yuni 2023, gwamnonin jihohi akalla 25 ne suka zabi Sanata Godswill Obong Akpabio, da Sanata Jibrin Barau a matsayin shugaban majalisar dattawa da mataimakin shugaban majalisar dattawa na majalisa ta 10.

Gwamnonin sun hada kai da zababbun Sanatoci na manyan jam’iyyu uku: APC, PDP da kuma jam’iyyar LP domin mara wa ‘yan takarar baya.

  • Sin Ta Bude Ofishin Jakadanci S Kasar Honduras.
  • Xi Jinping: Ana Kokarin Yaki Da Yaduwar Hamada A Sin Don Bude Sabon Babi

Daga cikin gwamnonin guda 25 da ke goyon bayan Akpabio sun hada da Gwamnonin Kwara, Nasarawa, Benue, Ogun, Oyo, Legas, Ekiti, Osun, Kogi, Ribas, Kuros Riba, Kaduna, Borno, Ebonyi da kuma Ondo.

Gwamnonin, wadanda akasarinsu na Jihohin da ke karkashin Jam’iyyar APC ne, sun ci gaba da cewa, sun yi kakkausar suka wajen amincewa da shawarar da Kwamitin Ayyuka na Kasa (NWC) na jam’iyya mai mulki ya dauka.

Gwamnonin sun kara da cewa jam’iyyar APC ta yanke shawara mafi inganci da za ta inganta zaman lafiya a hukumomi da kuma gudanar da harkokin majalisa cikin lumana a majalisa ta kasa ta 10 nan da shekara hudu masu zuwa.

Labarai Masu Nasaba

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

Musamman a lokacin da Akpabio ya ziyarci Gwamna Yahaya Bello a Jihar Kogi, gwamnan ya bayyana burin Akpabio da Barau na lashe kujerun shugaban majalisar dattawa da mataimaki a majalisa ta 10.

Ya kuma bayyana cewa Akpabio, tsohon ministan harkokin Neja-Delta, shi ne abin koyinsa, inda ya kara da cewa salon mulkin Sanatan da ba a saba gani ba a matsayinsa na gwamnan Jihar Akwa Ibom, ya sa ya so ya zama kamar tsohon gwamnan.

Gwamnan Kogi ya ce zai yi kokarin ganin an samu kwanciyar hankali a fadar shugaban kasa Bola Tinubu.

Har ila yau, gwamnan Jihar Ekiti, Biodun Oyebanji, ya ce zababbun sanatoci da sauran masu ruwa da tsaki a jihar ne ke goyon bayan takarar Sanata Akpabio don ya gaji Ahmad Lawan a matsayin shugaban majalisar dattawa.

Gwamnan Jihar Nasarawa, Abdullahi Sule, ya kuma bayyana cewa gwamnonin APC na Arewa cewa sun kuduri aniyar mara wa shugaba Bola Tinubu baya na zaben shugabannin majalisar dokokin kasar nan.

Gwamna Babajide Sanwo a Jihar Legas ya ce yana fatan Majalisar ta 10 za ta kasance ne kan “Sarfafa sabbin dokoki” don inganta abubuwan da aka riga aka yi a Majalisar ta tara.

Ya bayyana kungiyar zababbun Sanatoci a fadin jam’iyyar a matsayin “kungiyar da ta yi aiki sosai”.

Har ila yau, wata majiya ta kusa da Gwamnonin APC ta yi nuni da cewa, suna sa ran ganin an samu zaman lafiya, kwanciyar hankali a zauren majalisar ta 10.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AkpabioBarauGwamnoniMajalisa Ta 10
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Ta Bude Ofishin Jakadanci S Kasar Honduras

Next Post

Kotu Ta Bukaci Masu Kalubalantar Nasarar Tinubu Su Biya Miliyan 10 Kowannensu

Related

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
Ra'ayi Riga

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

13 hours ago
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a
Rahotonni

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

13 hours ago
Illar Kakaba Wa Majalisa Ta 10 Shugabanni Ga Gwamnatin Tinubu – Dattawan Arewa
Labarai

Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

15 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

16 hours ago
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa
Labarai

Amurka Ta Rage Wa’adin Bizar ‘Yan Nijeriya Zuwa Wata Uku

17 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna

18 hours ago
Next Post
Da Dumi-Dumi: Tinubu Ya Kama Aiki A Fadar Shugaban Kasa

Kotu Ta Bukaci Masu Kalubalantar Nasarar Tinubu Su Biya Miliyan 10 Kowannensu

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

July 12, 2025
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 12, 2025
Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa

July 11, 2025
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

July 11, 2025
Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 

July 11, 2025
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

July 11, 2025
“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

“Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

July 11, 2025
2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

2027: Masu Ruwa Da Tsaki Sun Bukaci A Kawo Karshen Matsalar Sayen Kuri’a

July 11, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka

July 11, 2025
Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

Fahimtar Kyawun Bambance-Bambance Kyakkawar Hanya Ce Ta Wanzar Da Zaman Jituwa A Duniya

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.