• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta Soki Zaben Kananan Hukumomi A Matsayin Cin Fuska Ga Dimokuradiyya

by Yusuf Shuaibu
10 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
‘Yan Majalisar Dokokin Nijeriya Sun Bukaci Karin Albashi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar wakilai ta soki yadda gwamnatocin jihohi ke gudanar da zaben kananan hukumomi, inda ta bayyana shi a matsayin cin fuska ga dimokuradiyya.

A cewarsu, wannan lamari ya gurgunta ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi, kuma dole ne a magance lamarin domin a kiyaye ka’idojin dimokuradiyya.

  • Gwamnatin Kano Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Fadar Sarkin Kano 
  • Gwamnoni Sun Miƙa Ta’aziyya Ga Waɗanda Wani Abu Ya Fashe Da Su A Mota A Zamfara

Shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajuddeen ya bayyana hakan ne a jawabinsa na bude taron tattaunawa kan gyara zaben kananan hukumomi da tsarin mulki na kasa, wanda kwamitin majalisar kan duba kundin tsarin mulki ya shirya a ranar Litinin da ta gabata a Abuja.

Tajuddeen ya ce, “Lokacin da zabubbuka suka kasance mara tsari, inda jam’iyya mai mulki ta mamaye dukkan mukamai, ya bayyana a fili muna cewa wanna cin fuska ne ga ka’idojin dimokuradiyya,” in ji Tajuddeen. Ya kara da cewa irin wadannan zabukan ba wai kawai na kawo cikas ga dimokuradiyya ba ne, har ma suna haifar da matukar damuwa game da daidaito da ayyukan kananan hukumomin.

“Wannan yanayin ba abin kunya ba ne kawai, yana kawo babbar barazana ga dimokuradiyyarmu. Yana haifar da mummunn yanayi, inda abubuwan da ba a so suke kutsawa cikin kananan hukumomi, galibi ba su da karfin da ake bukata da hangen nesa don gudanar da mulki yadda ya kamata.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

“Saboda haka, kananan hukumomi sun zama ‘yan amshin shatan gwamnatocin jihohi ko kuma ‘yan amshin shata a hannun ubangidan siyasa wadanda ke yin magudin zabe domin samun riban kashin kai,” in ji shi.

Tajuddeen ya bayyana rashin isassun kudade a matsayin daya daga cikin manyan kalubalen da kananan hukumomi ke fuskanta. “Yawancin gwamnatocin kananan hukumomi suna aiki da kasafin kudin da bai isa ya sauke nauyin da ke kansu ba,” in ji shi.

Ya kuma jaddada batun ‘yancin cin gashin kai, inda ya ce gwamnatocin jihohi ne ke sarrafa kananan hukumomi, wanda hakan ke haifar da tsoma baki wajen yanke shawara. A cewarsa, wannan rashin ‘yancin kai ne kuma yana dakushe romon dimokuradiyya a matakin kananan hukumomi.

Rashin isassun iya aiki daga fannin albarkatun Dan’adam da tsare-tsaren hukumomi ya kuma kawo cikas ga ingantaccen shugabanci a matakin kananan hukumomi. Yawancin ma’aikatan kananan hukumomi ba su da horo da kwarewa da ake bukata don gudanar da ingantaccen aiki, wanda hakan ke shafar samar da ayyuka da kuma sauke nauyin al’umma wajen gudanar da mulkin kananan hukumomi.

A halin da ake ciki, mataimakin shugban majalisar wakilai, Benjamin Okezie Kalu, wanda shi ne ya shugaban kwamitin majalisar kan yi wa kundin tsarin mulkin kasar kwaskwarima, ya jaddada bukatar hada karfi da karfe a tsakanin masu ruwa da tsaki domin samun gyara mai ma’ana a harkokin kananan hukumomin Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kananan Hukumomimajalisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

“Akwai Bukatar Gwamnatocin Nijeriya Su Inganta Aikin Harkar Ma’adanai”

Next Post

Guguwa Mai Ƙarfi Ta Sa An Soke Wasan Liverpool Da Everton Na Yau

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

2 weeks ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

2 weeks ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

2 weeks ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

3 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

3 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

3 weeks ago
Next Post
Guguwa Mai Ƙarfi Ta Sa An Soke Wasan Liverpool Da Everton Na Yau

Guguwa Mai Ƙarfi Ta Sa An Soke Wasan Liverpool Da Everton Na Yau

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.