ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, November 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Majalisa Ta Soki Zaben Kananan Hukumomi A Matsayin Cin Fuska Ga Dimokuradiyya

by Yusuf Shuaibu
11 months ago
Majalisa

Majalisar wakilai ta soki yadda gwamnatocin jihohi ke gudanar da zaben kananan hukumomi, inda ta bayyana shi a matsayin cin fuska ga dimokuradiyya.

A cewarsu, wannan lamari ya gurgunta ‘yancin cin gashin kan kananan hukumomi, kuma dole ne a magance lamarin domin a kiyaye ka’idojin dimokuradiyya.

  • Gwamnatin Kano Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Fadar Sarkin Kano 
  • Gwamnoni Sun Miƙa Ta’aziyya Ga Waɗanda Wani Abu Ya Fashe Da Su A Mota A Zamfara

Shugaban majalisar wakilai, Abbas Tajuddeen ya bayyana hakan ne a jawabinsa na bude taron tattaunawa kan gyara zaben kananan hukumomi da tsarin mulki na kasa, wanda kwamitin majalisar kan duba kundin tsarin mulki ya shirya a ranar Litinin da ta gabata a Abuja.

ADVERTISEMENT

Tajuddeen ya ce, “Lokacin da zabubbuka suka kasance mara tsari, inda jam’iyya mai mulki ta mamaye dukkan mukamai, ya bayyana a fili muna cewa wanna cin fuska ne ga ka’idojin dimokuradiyya,” in ji Tajuddeen. Ya kara da cewa irin wadannan zabukan ba wai kawai na kawo cikas ga dimokuradiyya ba ne, har ma suna haifar da matukar damuwa game da daidaito da ayyukan kananan hukumomin.

“Wannan yanayin ba abin kunya ba ne kawai, yana kawo babbar barazana ga dimokuradiyyarmu. Yana haifar da mummunn yanayi, inda abubuwan da ba a so suke kutsawa cikin kananan hukumomi, galibi ba su da karfin da ake bukata da hangen nesa don gudanar da mulki yadda ya kamata.

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

“Saboda haka, kananan hukumomi sun zama ‘yan amshin shatan gwamnatocin jihohi ko kuma ‘yan amshin shata a hannun ubangidan siyasa wadanda ke yin magudin zabe domin samun riban kashin kai,” in ji shi.

Tajuddeen ya bayyana rashin isassun kudade a matsayin daya daga cikin manyan kalubalen da kananan hukumomi ke fuskanta. “Yawancin gwamnatocin kananan hukumomi suna aiki da kasafin kudin da bai isa ya sauke nauyin da ke kansu ba,” in ji shi.

Ya kuma jaddada batun ‘yancin cin gashin kai, inda ya ce gwamnatocin jihohi ne ke sarrafa kananan hukumomi, wanda hakan ke haifar da tsoma baki wajen yanke shawara. A cewarsa, wannan rashin ‘yancin kai ne kuma yana dakushe romon dimokuradiyya a matakin kananan hukumomi.

Rashin isassun iya aiki daga fannin albarkatun Dan’adam da tsare-tsaren hukumomi ya kuma kawo cikas ga ingantaccen shugabanci a matakin kananan hukumomi. Yawancin ma’aikatan kananan hukumomi ba su da horo da kwarewa da ake bukata don gudanar da ingantaccen aiki, wanda hakan ke shafar samar da ayyuka da kuma sauke nauyin al’umma wajen gudanar da mulkin kananan hukumomi.

A halin da ake ciki, mataimakin shugban majalisar wakilai, Benjamin Okezie Kalu, wanda shi ne ya shugaban kwamitin majalisar kan yi wa kundin tsarin mulkin kasar kwaskwarima, ya jaddada bukatar hada karfi da karfe a tsakanin masu ruwa da tsaki domin samun gyara mai ma’ana a harkokin kananan hukumomin Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
Guguwa Mai Ƙarfi Ta Sa An Soke Wasan Liverpool Da Everton Na Yau

Guguwa Mai Ƙarfi Ta Sa An Soke Wasan Liverpool Da Everton Na Yau

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Majalisa 60 Sun Yi Barazanar Ficewa Daga PDP

Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa

November 11, 2025
‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

‘Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Kashe Ɗan Wasan Barau FC A Katsina

November 11, 2025
Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

Tinubu Ya Aika Wakilai Don Tattaunawa Da Birtaniya Kan Dawo Da Ekweremadu Nijeriya

November 11, 2025
HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

HOTUNA: Yadda Gobara Ta Ƙone Shaguna 25 A Kasuwar Singa A Kano

November 11, 2025
‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

‘Yan Bindiga Da ‘Yan Ta’adda Sun Fi Sojojin Nijeriya Yawan Makamai – Babachir

November 11, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Faɗa Ya Kaure Tsakanin Boko Haram Da ISWAP, An Kashe Mayaƙa Sama Da 170

November 11, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Yi Barazanar Maka BBC A Kotu Tare Da Neman Diyyar $1bn

November 11, 2025
Rashin Aiki Ga Matasa Babbar Barazana Ce Ga Nijeriya – Obasanjo 

Obasanjo Ya Buƙaci Matasa Su Karɓi Ragamar Shugabanci A Ƙasashen Afrika

November 11, 2025
Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 A Ƙauyen Katsina

November 11, 2025
An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

An Daddale Kulla Cinikin Sama Da Dala Biliyan 83 A Bikin CIIE Na Kasar Sin 

November 10, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.